Fikira24 Hausa

Fikira24 Hausa Fikira24 Hausa jarida ce da take baku labarai sahihai a koda yaushe.

Idan na zama shugaba ƙasa, jirgin sama mara matuki ne minista na na tsaro, cewar dan gwagwarmaya Omoyele Sowore Cikakken...
05/01/2026

Idan na zama shugaba ƙasa, jirgin sama mara matuki ne minista na na tsaro, cewar dan gwagwarmaya Omoyele Sowore

Cikakken labarin yana comment section 👇👇👇

Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar daukar matakin soji kan Columbia bayan Venezuela
05/01/2026

Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar daukar matakin soji kan Columbia bayan Venezuela

Mataimakiyar gwamnan Rivers ta fice daga PDP zuwa APCMataimakiyar Gwamnan Jihar Rivers, Farfesa Ngozi Odu, ta sauya sheƙ...
05/01/2026

Mataimakiyar gwamnan Rivers ta fice daga PDP zuwa APC

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Rivers, Farfesa Ngozi Odu, ta sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC, inda ta kammala rajistar zama mamba a mazabarta da ke Ogba/Egbema/Ndoni (ONELGA).

Odu ta ce matakin na da nufin ƙarfafa goyon baya ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da Gwamna Siminalayi Fubara a matakin ƙasa, tare da wayar da kan jama’a kan rajistar APC.

A yayin rangadin, daruruwan ‘yan jam'iyyar Labour Party a Ndoni sun sauya sheƙa zuwa APC.

A wani labarin makamancin haka, sakataren gwamnatin jihar Rivers, Dakta Benibo Anabraba, ya fice daga jam’iyyar PDP, yana mai cewa matakin na kansa ne bayan yin nazari, tare da gode wa jam’iyyar bisa damar da ta ba shi a baya.

Darren Fletcher ya zama sabon mai horas da 'yan wasan Manchester United na riko.Tushen labari: DCL Hausa
05/01/2026

Darren Fletcher ya zama sabon mai horas da 'yan wasan Manchester United na riko.

Tushen labari: DCL Hausa

DA ƊUMI-ƊUMI: Man United ta kori kocin ta AmorimKungiyar ƙwallon kafa ta Manchester United ta sallami me horaswar ta Rub...
05/01/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Man United ta kori kocin ta Amorim

Kungiyar ƙwallon kafa ta Manchester United ta sallami me horaswar ta Ruben Amorim a safiyar yau Litinin.

Ajiya ne dai United ta yi kunnen doki 1-1 da ƙungiyar ƙwallon kafa ta Leeds United a gasar Firimiya ta kasar England.

Bayan an tashi daga wasan, sai Amorim ya zargi shugabanin Man United a wata hira da ya yi da manema labarai bayan an tashi daga wasan.

Kwatsam kuwa a yau sai aka tashi da labarin sallamar Amorim, wanda ya jagoranci wasanni 63 a united ya kuma yi watanni 14 kacal a kungiyar.

Tushen labari: Daily Nigerian Hausa

HOTUNA: Yadda Gobara ta ƙone wani gidan mai a garin Shira da ke Jihar Bauchi. Hotuna: Sadis Yakubu Shira/Aminiya
05/01/2026

HOTUNA: Yadda Gobara ta ƙone wani gidan mai a garin Shira da ke Jihar Bauchi.

Hotuna: Sadis Yakubu Shira/Aminiya

Faka faka ta fito a farashi mai sauki duk mai bukata ya yi magana ta wannan lambar dake jikin hoton.
05/01/2026

Faka faka ta fito a farashi mai sauki duk mai bukata ya yi magana ta wannan lambar dake jikin hoton.

Yadda tambayar “Cire Sarkin Bogi” ta sa Grok AI ta cire hoton Aminu Ado Bayero, ya janyo cece kuce a shafukan sada zumun...
05/01/2026

Yadda tambayar “Cire Sarkin Bogi” ta sa Grok AI ta cire hoton Aminu Ado Bayero, ya janyo cece kuce a shafukan sada zumunta.

Gwamnatin Kano ta nesanta kanta da labarin tarbar Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero da aka ce gwamna Abba zai yi...
03/01/2026

Gwamnatin Kano ta nesanta kanta da labarin tarbar Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero da aka ce gwamna Abba zai yi a gobe Lahadi

Hadimin Gwamnan Kano Hon. Salisu Yahya Hotoro kenan sanye da hular 'Tinubu Arewa na godiya'.Hoto: Arewa Updates
03/01/2026

Hadimin Gwamnan Kano Hon. Salisu Yahya Hotoro kenan sanye da hular 'Tinubu Arewa na godiya'.

Hoto: Arewa Updates

02/01/2026
Gwamna Yusuf zai sauya sheka zuwa APC a ranar Litinin - RahotoGwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zai shiga jam’iyya mai mul...
02/01/2026

Gwamna Yusuf zai sauya sheka zuwa APC a ranar Litinin - Rahoto

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zai shiga jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance a ranar Litinin, kamar yadda DAILY NIGERIAN ta rawaito.

Abba Yusuf, wanda shi kaɗai ne gwamna a jam’iyyar NNPP, ya riga ya isa Abuja domin kammala shirye-shiryen sauya shekar tasa.

Majiyoyi da ke da masaniya kan shirin sauya shekar gwamnan sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Yitwalda Nentawe, ne za su karɓi gwamnan a Abuja.

Tuni dai an dawo da jagoran APC a Kano, Abdullahi Ganduje, daga wata tafiya da yake yi a Dubai. Haka kuma an umarci shugaban jam’iyyar APC na jihar, Abdullahi Abbas, da ya taƙaita tafiyarsa ta Umara domin ya miƙa katin zama ɗan APC ga gwamnan a mazabarsa ta Diso, da ke Karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano, a cikin makon nan.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fikira24 Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fikira24 Hausa:

Share