Gambiza Tv

Gambiza Tv Gambiza tv mai tsage gaskiya komai dacinta. Gambiza Tv mai leka gidan kowa,

Gambiza TV shafi da aka kirkira domin samar da sahihan labarai da ra’ayoyi masu zurfi game da harkokin siyasa, kasuwanci, da al’amuran yau da kullum na gida da waje.

ADC Ta Karyata Maganganun Datti Baba-Ahmed, Ta Ce Ra’ayinsa Na Kashin Kanshi NeJam’iyyar African Democratic Congress (AD...
24/08/2025

ADC Ta Karyata Maganganun Datti Baba-Ahmed, Ta Ce Ra’ayinsa Na Kashin Kanshi Ne

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta yi watsi da maganganun Sanata Datti Baba-Ahmed, mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben 2023, tana mai bayyana su a matsayin ra’ayin kashin kansa, ba matsayar jam’iyyar ba.

A wata sanarwa da Mataimakiyar Sakatariyar Yada Labarai ta kasa, Jackie Wayas, ta fitar ranar Asabar, jam’iyyar ta jaddada kudirinta na ci gaba da hada kan jam’iyyun adawa domin shiryawa zaben 2027.

Me zaku CE ?

Kuyi following din Gambiza Tv

IPOB: Nnamdi Kanu Ya Kai Karar  Alkalai Uku, Ya Nemi NBA Ta Dauki MatakiShugaban kungiyar Indigenous People of Biafra (I...
24/08/2025

IPOB: Nnamdi Kanu Ya Kai Karar Alkalai Uku, Ya Nemi NBA Ta Dauki Mataki

Shugaban kungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB), Mazi Nnamdi Kanu, ya kai ƙorafi ga Kungiyar Lauyoyin Najeriya (NBA), yana neman ta ɗauki mataki kan wasu alkalai uku – Justices Binta Nyako, Haruna Tsammani, da Garba Lawal – bisa zargin aikata babban kuskuren shari’a.

A cikin ƙorafin da ya sa hannu da kansa, Kanu ya yi zargin cewa alkalai sun aikata babbar kura-kurai da s**a haifar da rashin adalci a shari’ar da ake yi masa.

Me zaku CE

Kuyi following din Gambiza Tv

24/08/2025

Kubiyo mu mu leka jaridun najeriya muga wance wainar Ake toyawa a safiyar nan
Kuna tare da Gambiza Tv ?

24/08/2025

Assallamun alaikum mabiya Gambiza Tv barka Ku da safiyar
A yau dame kuka tashi ?
Muna yi muku fatan Alheri.

24/08/2025

YanZu karfe 3: 00 daidai na dare
Mabiya Gambiza Tv menene ya hana Ku barchi ?

DADUMI DUMINSA: Majalisar malaman Addinin Musulunci ta haramta bukukuwan biki a jihar Taraba.Yaya kuke Gani ?
23/08/2025

DADUMI DUMINSA: Majalisar malaman Addinin Musulunci ta haramta bukukuwan biki a jihar Taraba.

Yaya kuke Gani ?

23/08/2025

Idan aka baka second 10 kawai ka yi addu'a,kuna za'a karba mai zaka fara roka?

23/08/2025

A fahintar Ku menene ya kawo saukar farashin kayan Abinci yanzu ?

23/08/2025

Barkan Ku da dare
Ku bamu labarin yau
Menene ke Faruwa yanzu haka a inda kuke ?

DA DUMI-DUMI: Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian Council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau a ofishin ...
23/08/2025

DA DUMI-DUMI: Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian Council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau a ofishin shi dake Abuja.

Malaman sun fito daga kungiyoyin addinin musulunci daban-daban, sunce manufar ziyarar shine Hadinkai tsakanin musilmi, domin a samu fahimtar juna da hada karfi da karfe domin tunkarar maunfofin musulunci a dukkan lamura.

Muna Addu'ar Allah ya kara hada kan malamanmu da al'ummar musulmi baki daya, Yaa Hayyu Yaa Qayyum.

DADUMI DUMINSA:"Za a saki Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabbara domin komawa cikin iyalansa, amma zai ci gaba da zaman ɗauri...
23/08/2025

DADUMI DUMINSA:

"Za a saki Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabbara domin komawa cikin iyalansa, amma zai ci gaba da zaman ɗaurin talala."

Me zakuce?

EMEFELE YAFI DEZANI ALISON MADUEKE...A wani nazari kan manyan badakalar cin hanci a Najeriya, an bayyana cewa zargin da ...
23/08/2025

EMEFELE YAFI DEZANI ALISON MADUEKE...

A wani nazari kan manyan badakalar cin hanci a Najeriya, an bayyana cewa zargin da ake wa tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya fi na tsohuwar Ministar Man Fetur, Diezani Alison-Madueke, girma matuƙa.

Bisa ga bayanai na hukumomin bincike, Diezani tana fuskantar zargin karkatar da kuɗaɗe da dukiyoyi da darajarsu ta kai kusan dala biliyan biyu, tare da wasu kuɗaɗe a bankuna na cikin gida da na ƙasashen waje.

Sai dai a gefe guda, Emefiele na fuskantar tuhuma mai nauyi wacce ta haɗa da wawurar kuɗaɗe da darajarsu ta kai naira tiriliyan 26.6, fam miliyan 543 a asusun waje, da gidaje 753 da ake zargin ya mallaka ta hanyar da ba ta dace ba.

Masana harkar tattalin arziki na cewa, wannan na nuna cewa badakalar Emefiele ta kai matakin tarihi, inda aka ce ta zarta duk wata irin barna da aka taba gani a baya a Najeriya.

Me zakuce ?

Address

Court Road Kano
Kano
700101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gambiza Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category