Gambiza Tv

Gambiza Tv Follow the Gambiza Tv channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VbBseF6DuMR Gambiza tv mai tsage gaskiya komai dacinta.

Gambiza TV shafi da aka kirkira domin samar da sahihan labarai da ra’ayoyi masu zurfi game da harkokin siyasa, kasuwanci, da al’amuran yau da kullum na gida da waje. Gambiza Tv mai leka gidan kowa,

11/06/2026

Wani abu ya ja hankali a duniya… huta na ci a kan hular mafarauci amma bai kona shi ba — shin gaskiya ne ko AI?”

An bayyana cewa an kimanta darajar Dangote Refinery zuwa kusan dala biliyan 39.1 a tsarin saka hannun jari na musamman (...
11/06/2026

An bayyana cewa an kimanta darajar Dangote Refinery zuwa kusan dala biliyan 39.1 a tsarin saka hannun jari na musamman (Private Placement), lamarin da ke nuna irin karfin gwiwar da masu zuba jari ke yi kan makomar kamfanin. Rahotanni sun nuna cewa an samu gagarumar sha'awa daga masu saka jari tun kafin fara sayar da hannayen jari ga jama'a

Wannan na zuwa ne yayin da ake shirin fitar da hannayen jarin matatar zuwa kasuwar hada-hadar hannayen jari, inda masana ke hasashen cewa zai kasance daya daga cikin manyan cinikayyar kasuwanci a tarihin Afirka. Haka kuma, an ruwaito cewa masu zuba jari sun nuna sha'awar zuba sama da dala biliyan 2 tun kafin a kaddamar da shirin gaba daya.

A cewar Gambiza Tv, wannan ci gaba na kara nuna yadda matatar Dangote ke samun karbuwa a kasuwannin duniya, yayin da ake kallonta a matsayin daya daga cikin manyan ayyukan masana'antu da s**a sauya fannin man fetur a Najeriya.

Shin kana ganin fitar da hannayen jarin matatar Dangote zai bai wa 'yan Najeriya damar amfana da wannan katafaren kamfani?

Jagoran jam'iyyar Seriake Dickson, ya kare jam'iyyar NDC bayan s**a daga wasu magoya bayan Peter Obi, yana mai cewa jam'...
11/06/2026

Jagoran jam'iyyar Seriake Dickson, ya kare jam'iyyar NDC bayan s**a daga wasu magoya bayan Peter Obi, yana mai cewa jam'iyyar ce take bai wa 'yan takara damar tsayawa takara a ƙarƙashin inuwarta, ba wai tana karɓar wata alfarma daga kowa ba.

A wata hira da ya yi a shirin Prime Time na Arise Television, Dickson ya yi watsi da ra'ayin cewa ya kamata NDC ta yi godiya ga Peter Obi ko wani ɗan siyasa saboda shiga jam'iyyar domin tunkarar zaɓen shekarar 2027.

Ya ce jam'iyya tana da tsari da manufofinta, kuma ita ce ke ba 'yan takara damar neman kujerun siyasa a ƙarƙashinta.

A cewarsa, babu wani mutum da ya fi jam'iyya muhimmanci, yana mai jaddada cewa NDC ba ta dogara ga mutum guda wajen cimma burinta na siyasa.

Gambiza Tv : Wannan furuci na Dickson na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara tsakanin magoya bayan Peter Obi da wasu jiga-jigan NDC kan makomar jam'iyyar gabanin babban zaɓen 2027.

Shin jam'iyya ce ke ɗaga darajar ɗan takara, ko kuwa ɗan takara ne ke ɗaga darajar jam'iyya?

11/06/2026

Muhammadur Rasulullah ﷺ

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta kuduri aniyar kawo ƙarshen al'adar fara manyan ayyukan ...
11/06/2026

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta kuduri aniyar kawo ƙarshen al'adar fara manyan ayyukan gwamnati ba tare da kammala su ba. Ya ce daga yanzu gwamnati za ta tabbatar da cewa duk wani aiki da aka fara an kammala shi yadda ya kamata.

Tinubu ya yi wannan jawabi ne yayin ƙaddamar da wani sabon titin mota a Abuja, inda ya jaddada cewa gwamnatinsa ta dawo da amincewar jama'a ta hanyar kammala ayyukan da aka gada da kuma waɗanda aka fara a zamaninta. Ya ce zamanin da ayyuka ke zama a kasafin kuɗi na tsawon shekaru ba tare da an kammala su ba ya wuce.

A cewar shugaban ƙasar, ci gaban ababen more rayuwa na daga cikin muhimman manufofin gwamnatinsa domin bunƙasa tattalin arziki da inganta rayuwar al'umma.

Gambiza Tv : A baya dai an sha samun manyan ayyukan gwamnati da s**a tsaya cik a sassa daban-daban na Najeriya, lamarin da ke janyo asarar kuɗaɗen jama'a da kuma jinkirin ci gaba.

Shin kuna ganin gwamnatin Tinubu za ta iya cika wannan alƙawari na kawo ƙarshen ayyukan da ake watsarwa a hanya?

11/06/2026
11/06/2026

Mabiya Gambiza Tv dare yayi dare
Kuna tare damu KO Barchi ya dauke Ku ?

10/06/2026

Shin ka san irin gagarumar gudummawar da Sheikh Usman Dan Fodio ya bayar wajen gina ilimi, addini da shugabanci a Kasar Hausa?

Mutane da yawa suna jin sunansa, amma ba kowa ne ya san irin sauyin da ya kawo wanda har yanzu ake amfana da shi ba. Ku biyo mu tare da Sheikh Malam Yahaya Lawan Husain domin jin wannan tarihi mai cike da darussa.

10/06/2026

Prof Umar Sani Fagge ya bayyana cewa yawan wahalhalun da al'umma ke fuskanta na da alaƙa da yadda aka yi watsi da sunnonin Manzon Allah ﷺ.

Shin lokaci bai yi da za mu koma ga koyarwarsa ba?

:::

10/06/2026

Ya Rasulallah ﷺ, hasken duniya da lahira,
Mai ceton al'umma da izinin Allah,
Kai ne abin koyi ga masu gaskiya,
Salati da aminci su tabbata a gare ka har abada.

Address

Court Road Kano
Kano
700101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gambiza Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share