Hausa Independent Post

  • Home
  • Hausa Independent Post

Hausa Independent Post Independent post Jarida ce abar dogaron ku wajen samun ingantattun labarai da rahotanni da dumi-dum

Allah Ya yiwa fitaccen Malamin addinin musulunci shileikh Abubakar Pharmacy Rasuwa a yau Juma'a.Wata sanarwar da taaziyy...
05/06/2026

Allah Ya yiwa fitaccen Malamin addinin musulunci shileikh Abubakar Pharmacy Rasuwa a yau Juma'a.

Wata sanarwar da taaziyya da Farfesa Ali Isa Pantami ya Sanya a shafin sa na Facebook tace, Malam Abbakar Pharmacy ya rasu bayan jinya da ya sha fama da ita.

Sheikh Pantami ya yi addu'ar Neman rahma ga marigayin tare da Neman gafarar kurakuransa, ya Kuma yalwata masa kabarinsa.

Ya kuma yi addu'ar Allah ya kuma bai wa iyalansa da masoyansa haƙuri da juriya.

"Allah Ya sa Aljannah ce makomarsa tare da iyayenmu da malamanmu da zurriyyarmu da aminanmu da yan'uwanm".

Al’ummar Gobirawa Sun Bukaci Hon. Aliyu Sani Madakin Gini Ya Karasa Aikin Titin Kurna Farin Bene Zuwa Babban Layi.Al’umm...
31/05/2026

Al’ummar Gobirawa Sun Bukaci Hon. Aliyu Sani Madakin Gini Ya Karasa Aikin Titin Kurna Farin Bene Zuwa Babban Layi.

Al’ummar unguwar Gobirawa da ke ƙaramar hukumar Dala a jihar Kano sun roƙi ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙaramar hukumar Dala, Aliyu Sani Madakin Gini, da ya taimaka wajen kammala aikin titin da aka fara daga Kurna Farin Bene zuwa Babban Layi.

Mazauna yankin sun bayyana cewa aikin titin wanda Sanatan Kano ta Arewa, Barau Jibrin, yafara amma har yanzu ba a kai ga kammala shi ba, lamarin da suke ganin yana ci gaba da jefa al’umma cikin wahalhalu musamman a lokacin damina.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun ce titin na da matuƙar muhimmanci ga harkokin sufuri da kasuwanci, kasancewar yana haɗa unguwanni da dama tare da sauƙaƙa zirga-zirgar al’umma a yankin Gobirawa da kewaye.

Sun ce dalilin roƙon nasu ga Hon. Aliyu Sani Madakin Gini shi ne ganin irin ayyukan alheri da yake gudanarwa a mazaɓarsa, musamman yadda ya shimfiɗa tituna a yankin Kurna Yan Ganda, aikin da s**a bayyana a matsayin wanda ya kawo sauƙi da ci gaba ga mazauna yankin.

Al’ummar sun nuna fatan cewa ɗan majalisar zai duba koken nasu tare da ɗaukar matakin kammala aikin titin domin inganta rayuwar jama’a da bunƙasa ci gaban yankin.

PR/ABK

Barkan mu da Sallah, Allah Ya Karbi ibadun mu Ya maimaita mana mana.
28/05/2026

Barkan mu da Sallah, Allah Ya Karbi ibadun mu Ya maimaita mana mana.

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi gudanar da bincike kan kisan fararen hula a NajeriyaShugaban hukumar kare haƙƙin bil’ada...
13/05/2026

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi gudanar da bincike kan kisan fararen hula a Najeriya

Shugaban hukumar kare haƙƙin bil’adama na Majalisar Ɗinkin Duniya Volker Turk, ya buƙaci a gudanar da bincike na musamman game da kisan fararen hular da aka samu a Arewacin Najeriya, bayan hare-haren da dakarun ƙasar da na Chadi s**a kai kan ƴan ta’adda.

Rahotanni sun nuna cewar masinta da dama ne s**a rasa rayukansu a harin da sojojin Chadi sun kai a yankin Tafkin Chadi, wanɗanda mahukunta N'Djamena s**a zarga da taimakawa ƴan ta’addan Boko Haram.

A cikin sanarwar da Volker Turk ya fitar, ya kuma ce akwai buƙatar a gudanar da bincike na musamman, kan yadda aka kashe fararen hula a harin da jirgin saman sojin Najeriya ya kai kasuwar Tumfa da ke yankin ƙaramar hukumar Zurmi a jihar Zamfara, wanda rahotanni s**a ce sama da mutum ɗari s**a mutu.

Kafin wannan kira na Majalisar Ɗinkin Duniya, anji dama Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adam ta Amnesty International na Allah wadai da wannan hari.

RFI HAUSA

An kirkiro jihohin Daura, Gobir Da Katsina Da Wasu Guda 8 A Jamhoriyar NigerA yanzu, adadin jihohi a Jamhoriyar Nijar ya...
12/05/2026

An kirkiro jihohin Daura, Gobir Da Katsina Da Wasu Guda 8 A Jamhoriyar Niger

A yanzu, adadin jihohi a Jamhoriyar Nijar ya tashi Daga 8 zuwa 19 kamar yadda wani darakta da ya wakilci ministan cikin gida Janar Mohamed Toumba ya sanar a gaban Majalisar Shawara ta ƙasar a wannan talata.

Daftarin da ke sanar da ƙirƙiro jihohin da ya gabatar wa majalisar, na nuni cewa aƙalla kowace daga cikin jihohin ƙasar 8 an raba ta zuwa gida biyu, wasu kuwa uku yayin da aka ƙirƙiri sauran ta hanyar cire ƙananan hukumomi daga wasu jihohi tare da dunƙule su a matsayin jiha ɗaya.

A cewar minista Toumba, jihar Maradi ta asali, ƙarƙashin wannan tsari, an raba ta zuwa uku don samar da jihohin Katsina, Gobir da kuma Tazar, kamar dai yadda aka raba jihar Damagaram/Zinder gida uku don samar da jihohin Daura, Damagaram da kuma Damergou.

Wani abu sabo game da lamarin shi ne canza wa illahirin jihohin suna in ban da birnin Yamai da zai ci gaba da riƙe sunansa a matsayin fadar gwamnatin ƙasar

Madogara: RFI HAUSA

Nuhu Ribadu na Nan daram kan muƙaminsa -Fadar Shugaban KasaFadar shugaban Najeriya ta fitar da wata sanarwar cewa, Nuhu ...
12/05/2026

Nuhu Ribadu na Nan daram kan muƙaminsa -Fadar Shugaban Kasa

Fadar shugaban Najeriya ta fitar da wata sanarwar cewa, Nuhu Ribadu yana nan a matsayinsa na babban mashawarcin tsaron ƙasar.

Wata majiya daga fadar shugabancin ƙasar da ta nemi a sakaya sunanta, ta shaidawa jaridar PRNigeria cewa, nada Adeyinka Famadewa da Shugaba Tinubu ya yi a matsayin mashawarcin tsaron kasar na musamman a cikin gida, ba yana nufin an cire Ribadu daga muƙaminsa bane.

Fadar Shugaban ƙasar ta tabbatar da cewa jita-jitar maye gurbin Ribadu ƙarya ce, tare da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa na haɗin gwiwar hukumomin tsaro da sarrafa bayanan sirri.

Majiyar ta ce, sabon ofishin Adeyinka an ƙirƙire shi ne don ya taimaka wajen ƙarfafa tsaron cikin gida, wanda ya haɗa da harkokin shige da fice, da tsaron hanyoyin sufuri.

Majiyar ta ce, Famadewa zai yi aiki ne ƙarƙashin Ribadu don inganta tsarin tsaron ƙasar, ba tare da katsalandan a ayyukan da kundin tsarin mulki ya bai wa ofishin mashawarcin tsaron ba.

Adeyinka Famadewa tsohon Manjo Janar ne wanda ya ƙware a fannin bayanan sirri da dabarun yaƙi da ta'addanci, kuma ya taɓa zama babban jami'i a ofishin mai ba wa shugaban ƙasa shawara tsakanin shekarar 2015 zuwa 2021.

Wannan naɗin na Famadewa wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin Tinubu wajen sake fasalin tsaro don fuskantar matsalolin garkuwa da mutane, ta'addanci, da sauran barazanar tsaro da ke addabar Najeriya.

RFI Hausa

Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan KanoAn rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsa...
05/05/2026

Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano

An rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakin gwamnan Kano

Gwamnan Jihar ta Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ne ya jagoranci rantsar da shi yau talata a fadar gwamnatin Jihar.

An gudanar da bikin ne a dakin taro na Ante Chamber da ke cikin Gidan Gwamnati, inda manyan jami’an gwamnati, jiga-jigan jam’iyya, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar s**a halarta.

Bayan da Babbar Alkalin Jihar, Mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jagoranci rantsar da shi, gwamnan ya bukaci sabon mataimakin gwamnan da ya mutunta kundin tsarin mulki tare da gudanar da ayyukansa cikin gaskiya, jajircewa da kuma rikon amana.

Gwamna Yusuf ya jaddada muhimmancin hadin kai da aiki tare a harkokin mulki, inda ya bayyana cewa nasarar gwamnatinsa na dogara ne da kokarin hadin gwiwa da kuma jajircewar hidimtawa al’ummar Jihar Kano.

A nasa jawabin, tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana kwarin gwiwa ga sabon mataimakin gwamnan, yana mai cewa zai bayar da gudunmawarsa wajen bunkasa jihar.

A jawabin karbarsa, Alhaji Murtala Sule Garo ya gode wa gwamnan da al’ummar Jihar Kano bisa amincewar da s**a yi da shi, tare da yin alkawarin yin aiki tukuru domin tallafawa manufofin ci gaban gwamnati.

Ya kuma tabbatar da cewa zai yi amfani da kwarewarsa wajen tabbatar da ingantacciyar hidima ga jama’a, tare da inganta zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a fadin jihar.

Ofishin Jakadancin Ƙasar Amurka da ke Abuja ya sanar da dakatar da dukkan tarurrukan neman visa da aka tsara, inda ya bu...
09/04/2026

Ofishin Jakadancin Ƙasar Amurka da ke Abuja ya sanar da dakatar da dukkan tarurrukan neman visa da aka tsara, inda ya bukaci dukkan masu neman bisa da su duba imel ɗinsu domin samun sabbin ranakun da za a sake tsara musu.

A cikin sanarwar da aka fitar, ofishin ya bayyana cewa duk da dakatarwar da aka yi a Abuja, harkokin neman bisa za su ci gaba da gudana a Ofishin Jakadancin Amurka da ke Legas kamar yadda aka saba. Haka kuma, an ce ayyukan hidima ga ‘yan ƙasar Amurka za su ci gaba, amma ta hanyar alƙawari ko a yanayin gaggawa.

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta bayar, inda ta ba wa ma’aikatan gwamnati da ba na gaggawa ba da iyalansu damar ficewa daga ofishin jakadancin da ke Abuja, sakamakon abin da ta bayyana a matsayin tabarbarewar yanayin tsaro a Najeriya.

Ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Saud, ya yi tattaunawa ta waya da takwaransa na Iran, Abba...
09/04/2026

Ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Saud, ya yi tattaunawa ta waya da takwaransa na Iran, Abbas Araqchi, a karon farko tun bayan ɓarkewar rikici da hare-haren Iran a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wannan na zuwa ne a matsayin mataki na farko na hulɗa kai tsaye tsakanin ƙasashen biyu tun bayan fara wannan rikici.

Ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya ta wallafa a shafinta na X, ta ce ministocin biyu sun tattauna kan sabbin abubuwan da ke faruwa a yankin, tare da duba hanyoyin da za a bi domin dawo da tsaro da rage tashin hankali a yankin.

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki wasu fitattun ‘yan siyasa da s**a haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙ...
09/04/2026

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki wasu fitattun ‘yan siyasa da s**a haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, Peter Obi, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da kuma tsohon gwamnan jihar Ribas Rotimi Amaechi, inda ya zarge su da yin watsi da muradun talakawa tare da fifita bukatun kansu.

Lamido ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai, yana mai cewa ko a lokacin da suke kan madafun iko, wadannan shugabanni ba su nuna cikakkiyar kulawa da girmamawa ga jama’ar da s**a zabe su ba.

Ya ce, “Dole ne shugabanni su mutunta amanar da al’umma s**a ba su,” yana mai ƙara da cewa sauya sheƙar siyasa da wasu daga cikinsu ke yi a baya-bayan nan na nuna rashin la’akari da ra’ayin masu zaɓe.

Address

Kano

Telephone

+2348066418481

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Independent Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share