
20/09/2025
Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya yi kira ga al’umma da su yi amfani da kuri’a wajen sauke shugabannin da s**a gaza, yana mai jaddada cewa magudin zabe na daga cikin manyan barazanar da ke hana dimokuradiyya ci gaba a nahiyar Afirka.
Jonathan ya bayyana haka ne a wajen Taron Dimokuradiyya na 2025 na Gidauniyar Goodluck Jonathan (GJF Democracy Dialogue) da aka gudanar a Accra, Ghana, inda ya gargadi cewa tsarin dimokuraɗiyya a Afirka na cikin mawuyacin hali, kuma gazawar shugabanni wajen cika bukatun jama’a na iya haifar da mulkin k**a-karya.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na GJF, Wealth Dickson Ominabo, ya fitar a ranar Asabar, Jonathan ya ce sahihin zabe shi ne kadai hanya da za ta tabbatar da adalci da kuma sanya shugabanni su amsa wa jama’a kan ayyukan da s**a yi ko s**a gaza yi.