Hausa Independent Post

Hausa Independent Post Independent post Jarida ce abar dogaron ku wajen samun ingantattun labarai da rahotanni da dumi-dum

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya yi kira ga al’umma da su yi amfani da kuri’a wajen sauke shugabannin da ...
20/09/2025

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya yi kira ga al’umma da su yi amfani da kuri’a wajen sauke shugabannin da s**a gaza, yana mai jaddada cewa magudin zabe na daga cikin manyan barazanar da ke hana dimokuradiyya ci gaba a nahiyar Afirka.

Jonathan ya bayyana haka ne a wajen Taron Dimokuradiyya na 2025 na Gidauniyar Goodluck Jonathan (GJF Democracy Dialogue) da aka gudanar a Accra, Ghana, inda ya gargadi cewa tsarin dimokuraɗiyya a Afirka na cikin mawuyacin hali, kuma gazawar shugabanni wajen cika bukatun jama’a na iya haifar da mulkin k**a-karya.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na GJF, Wealth Dickson Ominabo, ya fitar a ranar Asabar, Jonathan ya ce sahihin zabe shi ne kadai hanya da za ta tabbatar da adalci da kuma sanya shugabanni su amsa wa jama’a kan ayyukan da s**a yi ko s**a gaza yi.

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta k**a wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a wani fashin makami da yunkurin kisa d...
20/09/2025

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta k**a wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a wani fashin makami da yunkurin kisa da ya faru a Bera Estate, Chevron, Jihar Legas, a watan Agusta.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Abdullahi Haruna, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, inda ya ce kamen ya biyo bayan bayanan sirri da aka samu.

A cewarsa, a ranar 11 ga Satumba, 2025, jami’an rundunar na musamman sun k**a Mathew Adewole mai shekara 25 daga unguwar Na’ibawa, da Mukhtar Muhammad mai shekara 31 daga unguwar Unguwa Uku, Kano.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa hare-haren da ‘yan ta’adda masu alaka da Boko Haram s**a kai a sansanin soja da daddare a ...
20/09/2025

Majiyoyi sun tabbatar da cewa hare-haren da ‘yan ta’adda masu alaka da Boko Haram s**a kai a sansanin soja da daddare a garuruwan Banki da Freetown, kusa da iyakar Kamaru, sun tilasta wa fararen hula kusan 5,000 tserewa zuwa Kamaru.

Harin ya afku ne kasa da mako biyu bayan wani hari da aka kai a Darul Jamal, inda aka kashe akalla mutane 90 a sak**akon rikicin da ya barke a wurin.

Shaidu sun ce kungiyar Boko Haram ce ta kai harin, inda s**a fara kai hari da misalin karfe 12 na dare, kuma a musayar wuta tsakanin sojoji da maharan, wani faran hula ya rasa ransa.

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta sanar da mutuwar kwamandan ta na jihar Cross River, C...
20/09/2025

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta sanar da mutuwar kwamandan ta na jihar Cross River, CN Ogbonna Maurice Uzoma, wanda aka tsinci gawarsa a cikin dakin otal da yake zama a Calabar.

Kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya bayyana cewa rahoton rasuwar ya kai ga shugaban hukumar, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), a Maiduguri, jihar Borno, inda yake halartar taron shugabannin hukumomi da Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya ta shirya.

Babafemi ya ce marigayin, wanda kwanan nan aka nada shi a matsayin kwamandan NDLEA na jihar Cross River, ya fara aiki a ranar 18 ga watan Agusta, 2025.

Gwamnatin Norway tare da Asusun Raya Jama’a na Majalisar Dinkin Duniya (UNFPA) sun hada kai da Cibiyar Nazari da Magance...
20/09/2025

Gwamnatin Norway tare da Asusun Raya Jama’a na Majalisar Dinkin Duniya (UNFPA) sun hada kai da Cibiyar Nazari da Magance Matsalolin Cin Zarafi a Gida (CERSDOV) domin karfafa yaki da cin zarafi da kuma kare ’yancin lafiyar haihuwa (SRHR) a karamar hukumomin Akko da Billiri, Jihar Gombe.

Wannan shiri ya biyo bayan jerin horo da aka gudanar a matakin al’umma, inda aka shirya taro a Kumo domin duba tasirin ayyukan da aka kaddamar da kuma karfafa dabarun yaki da cin zarafi a tsakanin mata da ’yan mata.

Babban mai bincike na CERSDOV, Dr. Hussaini Momoh Lawal, ya bayyana cewa shirin ya kunshi inganta wayar da kan jama’a tare da karfafa mata su karya shingayen al’ada domin kare kansu da kuma tallafawa ’yan mata masu tasowa.

19/09/2025

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Ya Sake Magantuwa Kan Komawarsa APC Ya gindaya Sharadi.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Juma’a ya kaddamar da wasu manyan ayyuka a masallacin tarihi na Sultan Bello da ...
19/09/2025

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Juma’a ya kaddamar da wasu manyan ayyuka a masallacin tarihi na Sultan Bello da ke Kaduna, wadanda kamfanin Tantita Security Services Nigeria Limited ya dauki nauyin aiwatarwa.

Ayyukan sun hada da ginin wajen alwala na zamani, dakunan wanka da hutawa guda 50, da kuma tankin ruwa mai daukar lita 300,000 domin amfani da masu ibada da kuma mazauna unguwar Sarki, inda masallacin yake.

Shugaba Tinubu, wanda ya halarci Kaduna domin daurin auren Nasirudeen, dan tsohon gwamnan Zamfara, Sanata Abdul’Aziz Yari, ya yaba da aikin da kamfanin Tantita ya gudanar.

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, tare da mataimakinsa, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo, sun kasance tare da jagora...
19/09/2025

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, tare da mataimakinsa, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo, sun kasance tare da jagoran siyasar jihar, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a wajen daurin auren kwamishinan ma’aikatar matasa da wasanni ta jihar Kano, Hon. Mustapha Rabiu Kwankwaso.

An gudanar da daurin auren ne a Masallacin Alfurqan da ke Alu Avenue, Nassarawa GRA, Kano.

Allah ya sanya alheri ya bada zaman lafiya.

Mamallakan katafariyar kasuwar zamani ta Shoprite, sun musanta jita-jitar da ake yadawa cewa za su rufe dukkan kantunans...
19/09/2025

Mamallakan katafariyar kasuwar zamani ta Shoprite, sun musanta jita-jitar da ake yadawa cewa za su rufe dukkan kantunansu a sassan Najeriya.

A ‘yan makonnin da s**a gabata, an ruwaito cewa wasu daga cikin shagunan kamfanin na fama da karancin kayayyaki, lamarin da ya haifar da zargin cewa jita-jitar ta iya zama gaskiya.

Sai dai wata sanarwa da Shoprite ya fitar, ta ce rashin kayakin cinikayyar da ake gani a rassansa ba ya nufin suna da shirin kulle shagunansu a sassan Najeriya.

Kotun Soja ta yanke wa wani soja hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ta same shi da laifin kisan kai a jihar Bauchi.Soj...
19/09/2025

Kotun Soja ta yanke wa wani soja hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ta same shi da laifin kisan kai a jihar Bauchi.

Sojan da aka bayyana sunansa a matsayin Private Lukman Musa, na rundunar sojoji ta 3 da ke Jos, jihar Filato, an same shi da laifin kashe wani mai tuka Keke NAPEP mai suna Abdulrahman Isa a garin Azere, jihar Bauchi.

Bisa shari’ar da aka gabatar a gaban kotun, Musa ya kashe Isa ba bisa ka’ida ba, sannan ya yi kokarin boye laifinsa ta hanyar sanya gawar a cikin buhu da jefar da ita tsakanin kauyukan Shira da Yala.

An gudanar da jana’izar marigayi Hakimin Kabo, Alhaji Idris Adamu Dankabo, a harabar Gidan Sarkin Kano da ke Kofar Kudu,...
19/09/2025

An gudanar da jana’izar marigayi Hakimin Kabo, Alhaji Idris Adamu Dankabo, a harabar Gidan Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, bayan rasuwarsa sak**akon hatsarin mota.

Marigayin, wanda shi ne Hakimin Kabo kuma Sarkin Gabas, yana da shekaru 48, ya bar mata daya da yara biyu.

Tuni aka binne shi a makabartar Kuka Bulikiya da ke karamar hukumar Dala a Kano.

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yaba da irin rawar da hukumar Hisba ke takawa wajen kyautata tarbiyya da kare...
19/09/2025

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yaba da irin rawar da hukumar Hisba ke takawa wajen kyautata tarbiyya da kare martabar al’umma a jihar Kano.

A cikin ziyarar da s**a kai ofishin hukumar, Sarkin ya bukaci a samar da kundi na musamman da za a rika adana bayanan batun sakin aure, domin rage matsalolin da ke addabar aure a tsakanin jama’a.

Haka kuma, Sarkin ya shawarci hukumar da ta kirkiro asusu na bayar da rance ga mazajen da s**a rabu da matayensu, domin bayar da kudin ciyarwa ga yara, inda iyayen za su iya biya a hankali.

Address

Kano
Kano

Telephone

+2348066418481

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Independent Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share