05/05/2026
Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano
An rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakin gwamnan Kano
Gwamnan Jihar ta Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ne ya jagoranci rantsar da shi yau talata a fadar gwamnatin Jihar.
An gudanar da bikin ne a dakin taro na Ante Chamber da ke cikin Gidan Gwamnati, inda manyan jami’an gwamnati, jiga-jigan jam’iyya, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar s**a halarta.
Bayan da Babbar Alkalin Jihar, Mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jagoranci rantsar da shi, gwamnan ya bukaci sabon mataimakin gwamnan da ya mutunta kundin tsarin mulki tare da gudanar da ayyukansa cikin gaskiya, jajircewa da kuma rikon amana.
Gwamna Yusuf ya jaddada muhimmancin hadin kai da aiki tare a harkokin mulki, inda ya bayyana cewa nasarar gwamnatinsa na dogara ne da kokarin hadin gwiwa da kuma jajircewar hidimtawa al’ummar Jihar Kano.
A nasa jawabin, tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana kwarin gwiwa ga sabon mataimakin gwamnan, yana mai cewa zai bayar da gudunmawarsa wajen bunkasa jihar.
A jawabin karbarsa, Alhaji Murtala Sule Garo ya gode wa gwamnan da al’ummar Jihar Kano bisa amincewar da s**a yi da shi, tare da yin alkawarin yin aiki tukuru domin tallafawa manufofin ci gaban gwamnati.
Ya kuma tabbatar da cewa zai yi amfani da kwarewarsa wajen tabbatar da ingantacciyar hidima ga jama’a, tare da inganta zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a fadin jihar.