Hausa Independent Post

Hausa Independent Post Independent post Jarida ce abar dogaron ku wajen samun ingantattun labarai da rahotanni da dumi-dum

Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan KanoAn rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsa...
05/05/2026

Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano

An rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakin gwamnan Kano

Gwamnan Jihar ta Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ne ya jagoranci rantsar da shi yau talata a fadar gwamnatin Jihar.

An gudanar da bikin ne a dakin taro na Ante Chamber da ke cikin Gidan Gwamnati, inda manyan jami’an gwamnati, jiga-jigan jam’iyya, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar s**a halarta.

Bayan da Babbar Alkalin Jihar, Mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jagoranci rantsar da shi, gwamnan ya bukaci sabon mataimakin gwamnan da ya mutunta kundin tsarin mulki tare da gudanar da ayyukansa cikin gaskiya, jajircewa da kuma rikon amana.

Gwamna Yusuf ya jaddada muhimmancin hadin kai da aiki tare a harkokin mulki, inda ya bayyana cewa nasarar gwamnatinsa na dogara ne da kokarin hadin gwiwa da kuma jajircewar hidimtawa al’ummar Jihar Kano.

A nasa jawabin, tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana kwarin gwiwa ga sabon mataimakin gwamnan, yana mai cewa zai bayar da gudunmawarsa wajen bunkasa jihar.

A jawabin karbarsa, Alhaji Murtala Sule Garo ya gode wa gwamnan da al’ummar Jihar Kano bisa amincewar da s**a yi da shi, tare da yin alkawarin yin aiki tukuru domin tallafawa manufofin ci gaban gwamnati.

Ya kuma tabbatar da cewa zai yi amfani da kwarewarsa wajen tabbatar da ingantacciyar hidima ga jama’a, tare da inganta zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a fadin jihar.

Ofishin Jakadancin Ƙasar Amurka da ke Abuja ya sanar da dakatar da dukkan tarurrukan neman visa da aka tsara, inda ya bu...
09/04/2026

Ofishin Jakadancin Ƙasar Amurka da ke Abuja ya sanar da dakatar da dukkan tarurrukan neman visa da aka tsara, inda ya bukaci dukkan masu neman bisa da su duba imel ɗinsu domin samun sabbin ranakun da za a sake tsara musu.

A cikin sanarwar da aka fitar, ofishin ya bayyana cewa duk da dakatarwar da aka yi a Abuja, harkokin neman bisa za su ci gaba da gudana a Ofishin Jakadancin Amurka da ke Legas kamar yadda aka saba. Haka kuma, an ce ayyukan hidima ga ‘yan ƙasar Amurka za su ci gaba, amma ta hanyar alƙawari ko a yanayin gaggawa.

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta bayar, inda ta ba wa ma’aikatan gwamnati da ba na gaggawa ba da iyalansu damar ficewa daga ofishin jakadancin da ke Abuja, sakamakon abin da ta bayyana a matsayin tabarbarewar yanayin tsaro a Najeriya.

Ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Saud, ya yi tattaunawa ta waya da takwaransa na Iran, Abba...
09/04/2026

Ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Saud, ya yi tattaunawa ta waya da takwaransa na Iran, Abbas Araqchi, a karon farko tun bayan ɓarkewar rikici da hare-haren Iran a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wannan na zuwa ne a matsayin mataki na farko na hulɗa kai tsaye tsakanin ƙasashen biyu tun bayan fara wannan rikici.

Ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya ta wallafa a shafinta na X, ta ce ministocin biyu sun tattauna kan sabbin abubuwan da ke faruwa a yankin, tare da duba hanyoyin da za a bi domin dawo da tsaro da rage tashin hankali a yankin.

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki wasu fitattun ‘yan siyasa da s**a haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙ...
09/04/2026

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki wasu fitattun ‘yan siyasa da s**a haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, Peter Obi, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da kuma tsohon gwamnan jihar Ribas Rotimi Amaechi, inda ya zarge su da yin watsi da muradun talakawa tare da fifita bukatun kansu.

Lamido ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai, yana mai cewa ko a lokacin da suke kan madafun iko, wadannan shugabanni ba su nuna cikakkiyar kulawa da girmamawa ga jama’ar da s**a zabe su ba.

Ya ce, “Dole ne shugabanni su mutunta amanar da al’umma s**a ba su,” yana mai ƙara da cewa sauya sheƙar siyasa da wasu daga cikinsu ke yi a baya-bayan nan na nuna rashin la’akari da ra’ayin masu zaɓe.

Yayin da wa’adin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya baiwa Iran na sake buɗe mashigin Hormuz ke gabatowa, rahotanni sun...
07/04/2026

Yayin da wa’adin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya baiwa Iran na sake buɗe mashigin Hormuz ke gabatowa, rahotanni sun nuna cewa magoya bayan gwamnatin Iran sun fantsama kan tituna, tare da yin tattaki a wasu tashoshin wutar lantarki.

Gidan talabijin na ƙasar Iran ya watsa bidiyo na magoya bayan gwamnati suna rike da tutar Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Haka kuma, wasu hotunan sun nuna mutanen suna taruwa a kusa da tashoshin wutar lantarki a biranen Neka, Mashhad, Tabriz da sauransu.

Maganar ta biyo ne bayan Trump ya yi barazanar kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran tare da shafe tarihinta, idan ƙasar ba ta buɗe mashigin Hormuz ba.

Jam’iyyar ADC ta sanar da ficewar tsohon sanatan Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya, daga jam’iyyar APC zuwa cikinta.Sana...
07/04/2026

Jam’iyyar ADC ta sanar da ficewar tsohon sanatan Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya, daga jam’iyyar APC zuwa cikinta.

Sanarwar ta fito ne ta shafin Facebook na jam’iyyar, inda ta bayyana Gaya a matsayin gogaggen ɗan siyasa mai tasiri a harkokin majalisar dokoki a Najeriya.

Gaya ya fara zama sanata a shekarar 2007, inda ya wakilci mazabar Kano ta Kudu tsawon wa’adi da dama. A lokacin da yake majalisa, ya kasance mamba a muhimman kwamitoci da s**a haɗa da na gas, basuss**an cikin gida da na waje, jihohi da ƙananan hukumomi, bangaren bincike da hako man fetur, da kuma ayyuka.

Fadar White House ta yi ƙarin haske kan kalaman mataimakin shugaban Amurka, JD Vance, dangane da ɗaukar matakin soji a k...
07/04/2026

Fadar White House ta yi ƙarin haske kan kalaman mataimakin shugaban Amurka, JD Vance, dangane da ɗaukar matakin soji a kan ƙasar Iran.

Ta ce kalaman nasa ba su nufin cewa Amurka za ta yi amfani da makamin nukiliya kan Iran ɗin.

Wannan na zuwa ne bayan da JD Vance, ya bayyana cewa sojojin ƙasar za su iya amfani da wasu sabbin makamai da ba a taɓa amfani da su ba, idan wa’adin da Trump ya gindaya ya cika.

Rundunar sojin Najeriya ta musanta zargin da wani tsohon jami’inta, Rotimi Olamilekan, ya yi cewa sojojin ƙasar na sayen...
07/04/2026

Rundunar sojin Najeriya ta musanta zargin da wani tsohon jami’inta, Rotimi Olamilekan, ya yi cewa sojojin ƙasar na sayen kayan sarki da kuɗin aljihunsu.

Zargin ya fito ne bayan wani bidiyo da ya yaɗu a kafafen sada zumunta, inda tsohon sojan wanda aka sallama daga aiki ya bayyana damuwarsa kan abin da ya ce rashin kulawa da ake nuna wa jami’an soji.

Sai dai a wata sanarwa da daraktar yaɗa labarai ta rundunar sojin ƙasa na Najeriya, Appolonia Anele, ya fitar, rundunar ta ce iƙirarin ba gaskiya ba ne. Ta jaddada cewa ana samar da kayan aiki yadda ya kamata ga jami’an soji.

Majalisar Dokokin Jihar Kano tace ta jingine tuhumar da take yi wa tsohon mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwa...
07/04/2026

Majalisar Dokokin Jihar Kano tace ta jingine tuhumar da take yi wa tsohon mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo, bayan ya sauka daga mukaminsa.

Majalisar ta bayyana hakan ne a zamanta na yau, karkashin jagorancin Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Jibrin Isma’il Falgore.

Da yake ƙarin haske kan lamarin, shugaban masu rinjaye na majalisar, Hon. Lawan Husaini Chediyar Yan’gurasa, ya ce majalisar ba ta da hurumin ci gaba da bin tuhumar da take yiwa tsohon mataimakin gwamnan.

Ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, Yusuf Buhari, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majali...
07/04/2026

Ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, Yusuf Buhari, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai a zaɓen 2027.

Tsohon mai taimaka wa shugaban ƙasa kan harkokin sadarwa, Bashir Ahmad, ne ya tabbatar da hakan, bayan yaɗuwar jita-jita a kafafen sada zumunta game da shirin Yusuf na shiga siyasa.

A wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 3 ga Afrilu, wadda aka aika wa masu ruwa da tsaki a mazaɓar Sandamu/Daura/Mai’Adua ta jihar Katsina, Yusuf Buhari ya bayyana cewa zai tsaya takara a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Rundunar Juyin Juya Halin Iran (IRGC) ta tabbatar da mutuwar shugaban sashen tattara bayanan sirri nata, Majid Khademi.A...
06/04/2026

Rundunar Juyin Juya Halin Iran (IRGC) ta tabbatar da mutuwar shugaban sashen tattara bayanan sirri nata, Majid Khademi.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a safiyar Litinin, ta zargi Israel da Amurka da kai harin da ya yi sanadin mutuwarsa.

BBC ta tuntuɓi rundunar sojin Isra’ila, wadda ta ce za ta “duba” rahoton.

Address

Kano
Kano

Telephone

+2348066418481

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Independent Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share