Sharhin Siyasa Nigeria

Sharhin Siyasa Nigeria Wannan kafa an kirkire ta ne don yin sharhi kan al'amuran siyasar Nigeria da na kasashen ketare

19/10/2025

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa, wasu majiyoyin tsaro sun bayyana ma ta cewa, jami’an sojan da ake zargi da shirin juyin mulki a Najeriya sun tsara kai hari da kuma kashe manyan jami’an gwamnati, ciki har da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da mataimakinsa, Kashim Shettima, da wasu shugabanni na majalisa.

Majiyoyin sun shaida wa jaridar Premium Times cewa shirin ya haɗa da kai hari a lokaci guda ga waɗanda aka nufa, a ranar da dukkan su za su kasance cikin ƙasa.

“Sun tsara su hallaka su duka a lokaci guda. Suna neman lokaci da za su tabbata duk manyan jami’an nan suna cikin ƙasa. A duk inda suke, za a kashe su,” in ji wata majiya.

Rahoton ya ƙara da cewa waɗanda ake zargi sun kuma yi niyyar k**a wasu manyan jami’an tsaro ciki har da shugabannin rundunonin soja.

“Haka kuma sun tsara su k**a manyan hafsoshin soja, ciki har da shugabannin rundunoni, amma ba su da niyyar kashe su,” in ji wata majiya daga cikin binciken.

Rahoton ya ce sunan waɗanda aka nufa da kisan ya haɗa da:

* Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu
* Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima
* Shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio
* Shugaban majalisar wakilai Tajudeen Abbas

An ce waɗanda ake zargi sun samu taimako daga wasu jami’an da ke aiki a fadar shugaban ƙasa da wasu wurare masu muhimmanci don tattara bayanai game da motsin waɗanda ake son kai wa hari.

A wata sanarwa da rundunar sojojin ta fitar, an bayyana cewa binciken da ake yi bai tabbatar da wani yunkurin juyin mulki ba tukuna, amma ana duba yiwuwar take dokoki da rashin ladabi daga jami’an da ake zargi.

Rahoton ya ce wannan lamari ya haifar da damuwa a tsakanin hukumomin tsaro da gwamnati, inda ake ganin shi ne daya daga cikin dalilan da ya sa aka dakatar da bikin ranar ’yancin kai ta bana.

Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa tana ci gaba da bincike kan lamarin, tare da tabbatar da cewa ba za ta lamunci duk wani yunkuri da zai barazana ga tsarin dimokuraɗiyya da zaman lafiya a ƙasar ba.




18/10/2025

Mu da Dimukuradiya mutu ka raba: Rundunar sojin Nigeria ta cè shifcin gizo ne kawai Shedanu ke yadawa cewa wasu sojoji sun shirya juyin mulki ga gwamnatin Tinubu kafin asirinsu ya tonu a k**asu.

18/10/2025

Wasu manyan jami’an sojin Najeriya da ke tsare a halin yanzu bisa zargin shirya juyin mulki domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sun fito ne daga ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro (ONSA), wanda Nuhu Ribadu ke jagoranta.

Wannan ofishi na ONSA na tattara jami’ai daga sassa daban-daban na tsaro – sojoji, ‘yan sanda, jami’an leƙen asiri da kuma hukumomin tsaro na paramilitary. A cewar rahoton SaharaReporters, an k**a waɗannan jami’an ne a ranar bikin ‘yancin kai na 1 ga Oktoba, inda ake zargin sun shirya kifar da gwamnati tare da kafa sabuwar gwamnatin soja. Wannan rana ce da ake murnar samun ‘yancin kai a Najeriya, kuma su s**a zaɓi ta domin aiwatar da shirin su.

Duk da cewa rundunar soji ta fitar da sanarwa tana cewa an k**a jami’an ne saboda gazawa a jarabawar haɓaka matsayi da kuma rashin ci gaba a aiki, wasu manyan majiyoyi sun bayyana cewa ainihin dalilin k**a su shi ne yunkurin juyin mulki.

Wani babban jami’in hukumar leƙen asiri ta soji (DIA) ya tabbatar da cewa an k**a jami’an ne bayan an gano shirin su na kifar da gwamnati, wanda s**a fara ta hanyar tarurruka a ɓoye. Ya ce:
“Jami’ai 16 ne ke cikin wannan shiri. Daga Kyaftin har zuwa Birgediya Janar. An k**a su a gidajensu daban-daban a faɗin ƙasar nan.”

An bayyana Laftanar Kanar Al-Makura a matsayin jagoran wannan yunkuri. Ya dawo ne daga wani kwas na musamman a China, kuma an tura shi ofishin NSA kwanan nan. Shi da ɗan uwansa – wanda shima Laftanar Kanar ne a Elele – duk kawunan tsohon gwamnan Nasarawa ne, Tanko Al-Makura. Sai dai an ce ɗan uwan nasa ba ya cikin shirin, kuma an sake shi bayan bincike.

Majiyar ta bayyana cewa mafi yawan waɗanda ake zargi ‘yan Arewa ne, kuma matasa daga cikinsu sun shiga shirin ne bisa ruɗu da yaudara. A halin yanzu, babu wanda ke da damar ganin iyalansa daga cikin waɗanda ake tsare da su.

Wani babban jami’i ya bayyana cewa wannan shiri ne ya sa aka soke bikin ranar ‘yancin kai da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, domin gudun abin da ka iya faruwa.

Madogaran Labari: SaharaReporters

18/10/2025

A ranar 15 ga watan Aprilu 1989 'yan kallo 97 s**a mutu a filin wasa na Hillsborough da ke Sheffield a INGILA sak**akon turmutsisi lokacin da Liverpool ke fafatawa da Nottingham Forest a gasar FA CUP

18/10/2025

Shugaban Jam'iyyar APC ta kasa Farfesa Nentawe Yilwatda, ya ce Jam'iyyar a yanzu ta zama 'yar-lele sak**akon farin Jinta a wajen 'yan Nigeria.

Fasha iya fasha 😲
17/10/2025

Fasha iya fasha 😲

A ranar 7 ga watan Yuli, 2013, an gudanar da wasu wasannin ƙwallon ƙafa da s**a girgiza Najeriya da ma duniya baki ɗaya!
Wasannin sun gudana ne a matakin neman hawa gasar ƙananan rukuni (Nationwide League), amma abin da ya faru ya zama abin dariya da mamaki.

A wancan rana, Plateau United Feeders ta lallasa Akurba FC da kwallaye 79–0, sannan Police Machine ta doke Bubayaro FC da 67–0. Jimillar kwallayen da aka zura kuwa ta kai 146! 😳

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya (NFF) ba ta yi wasa ba — ta gudanar da bincike, ta gano cewa an shirya wasannin domin a samu damar hawa rukuni na gaba.
Sak**akon haka, duk ‘yan wasa da jami’an da s**a halarci wasannin an yi musu takunkumin har abada (life ban), yayin da ƙungiyoyi huɗun da abin ya shafa aka hana su shiga kowace gasa tsawon shekaru 10.

NFF ta ce za ta aika rahoton zuwa CAF da FIFA, kuma za ta wallafa sunayen da hotunan waɗanda s**a shiga wannan almundahana domin zama izina ga sauran masu wasa.

Har yau, wannan lamari yana daga cikin fashar ƙwallon ƙafa mafi girma da aka taɓa gani a tarihin wasanni na Najeriya — inda aka ci kwallaye 146 cikin wasanni guda biyu kacal!

🔥 Me kake tunani — me yasa ƙungiyoyi ke iya yin haka don hawa mataki? Ka bayyana ra’ayinka 👇

Wani ya ƙwaƙwale Idon ƙanwarsa.Wani Matashi mai suna Auwalu ya ƙwaƙwale Idon ƙanwarsa  yar'shekara 7 Mai suna Ruƙayya da...
17/10/2025

Wani ya ƙwaƙwale Idon ƙanwarsa.

Wani Matashi mai suna Auwalu ya ƙwaƙwale Idon ƙanwarsa yar'shekara 7 Mai suna Ruƙayya daga Garin Wailo Ƙaramar Hukumar Ganjuwa Jihar Bauchi.

Da yake Jawabi wa Globe FM Bauchi Mahaifin Yarinya Muhammad Adamu ya ce wanda ake zargin Auwalu ɗa ne ga ƙanwarsa uwa ɗaya uba ɗaya.

Mahaifin Yarinyar ya ce Auwalu ya ja Ruƙayya ne cikin Dawa inda ya ƙwaƙwale mata idon ta guda biyu.

Ruƙayya dai tuni Likitocin ido s**a yi mata aiki, Dr Shahir Umar Bello Ƙwararren Likitan Ido ne kuma Shugaban Sashen kula da lafiyar ido a Asibiti koyarwa na Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa dake nan Bauchi ya kuma ce Ruƙayya ganinta ba zai sake dawowa ba, ma'ana ta makance kenan.

17/10/2025

Address

Kumbotso Street Dan Maliki
Kano
KANO

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sharhin Siyasa Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sharhin Siyasa Nigeria:

Share