Tongas Narrative Scope

Tongas Narrative Scope Let's Spread Happiness for Everyone. Fatanmu kowa ya yi farin ciki.

Ku zo mu Tattauna. Shin, a wace shekara ka shiga Izala? Ka san lokacin bayyanar ta, ko kuwa kai Dan Izalar bana bakwai c...
30/11/2025

Ku zo mu Tattauna. Shin, a wace shekara ka shiga Izala? Ka san lokacin bayyanar ta, ko kuwa kai Dan Izalar bana bakwai ce?

28/11/2025

Ban taɓa ganin sakaran addini kamar addinin mutanen nan ba, addinin da dole ka yarda irin Buhari da ya kashe mutane ya zubar da jinane, amma yana Aljanna, shi kuma Shehu Ɗahiru da ya rayu yana yiwa Addinin Allah hidima da Kur'ani ya na wuta. Sai dauko wasu littafan Bogi suke yi suna Karanta tatsuniyoyi Suna kafirta Shaik Dahiru. Wallahi tir da irin wannan Addini na ku. Allah ka jikan Shaik Dahiru Bauchi.

27/11/2025

Allah ya jikan Shaik Dahiru Bauchi, Malamin da ba a taba mai kamar sa ba a Najeriya da Afrika

23/11/2025

'Yan kishin arewa, ku taya ni lissafi don Allah.

23/11/2025

Arewa ana zaman lafiya, manya na kokari. Me za ku ce 'yan Arewa?

21/11/2025

Abin da ke Shirin faruwa a Muqabalar Ahlis Sunna da Masussuka.
Explain👇👇👇Opinion.
Say no to Muqabala, yes to Hadin Kai.

21/11/2025

A wani Hadisi aka ambaci Bukhari da Muslim? Amsa pls 🙏 ban da Zagi.
Manzon Allah SAW cewa ya yi, na bar muku nauyayan Abubuwa guda biyu, idan ku ka bi su, ba za ku bace ba har sai kun sameni a bakin tafki. Ya ce Alkur'ani da iyalan gida na, Itrati. To, shin a wani Hadisi ne Manzon Allah ya ce mu yi riko da Bukhari da Muslim? Don Allah masana musamman Malaman Ahlis sunna ko dalibansu a kawo mana hadisin da ya ce mu yi riko da Bukhari da Muslim. Idan babu, me ya sa za ku ce dole sai an bi su?
Muna jiran amsoshin ku.

Masussuka: Budaddiyar Wasika zuwa ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda.Kiyaye Hakkin Shaik Masussuka-Amb...
20/11/2025

Masussuka: Budaddiyar Wasika zuwa ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda.

Kiyaye Hakkin Shaik Masussuka-Ambasadan Zaman Lafiya, tare da damar gudanar da Addini dai dai fahimta da 'Yancin fadin Albarkacin baki.
______________
Ya Mai Girma Gwamna.
Ina fata wannan wasikar tawa za ta sameka a cikin kwanciyar hankali da ingantaciyyar lafiya. Na rubuta maka wannan wasikar ce, domin na jawo hankalinka kan damar da kowane dan kasa ke da ita na damar yin addininsa kamar yadda yayi imani da 'yancin fadin albarkacin baki.
A 'Yan kwanakin nan Shaik Masussuka wanda aka ba shi matsayin Ambasadan zaman lafiya saboda salonsa na waazin zaman lafiya yana samun matsi da barazana daga gungun wadansu Malamai saboda kawai bambanci fahimta na addini. Akwai rade-radin da ke nuni da cewa wadancan Malamai sun matsa maka lamba, ko dai ka sa Shaik Masussuka ya daina wa'azi, ko kuma ka Kai shi Gidan Kurkuku.

Kamar yadda ka sani ya mai girma gwamna, sashen kundin tsarin mulkin Najeriya mai lamba 38 (1) a cikin baka ya bada dama ga kowane dan kasa yayi Addinin da ya ga dama ba tare da wani yayi masa katsalandan ba.
Haka kuma, sashe na 39 (1) cikin baka ya bayyana cewa kowane Dan kasa na da 'yancin yin addinin da ya ga dama, da fadin albarkacin bakinsa ba tare da wani ko wasu sun tsangame shi ba, ko su tilasta masa Ajiye raayinsa don ya koma na su. Wadannan dokoki sun bawa kowane Dan kasa cikakkiyar dama na yi addininsa yadda ya ke so.

Anan, da girman kujerarka ya Mai girma Gwamna, Ina ba ka shawara kamar haka.
1. Ka bada kariya ga Shaik Masussuka kamar yadda tsarin mulki ya tanada da kowace irin tsangwama, da ba shi goyon baya wajen waazinsa na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, da hadin kai tsakanin musulmi da wadanda ba Musulmi ba.
2. Kada ka yarda da matsin Lamba, na kowane bangare na addini wajen kokarin ingizaka na amfani da Karfin mulki domin dakushewa da hana 'yancin mutum na bayyana raayinsa na addini. Domin masu kokarin sai an yi haka, suma raaayoyinsu suke bayyanawa
3. Ka manta da su ka cigaba da ayyukan kyautata rayuwar Jama'ar Jihar Katsina, musamman halin da Jihar ta ke ciki na 'yan ta'adda, yaki da talauci da ayyukan kyautata rayuwa a Jihar Katsina da zai amfani al'umma.
4. Kada ka yarda a yi wani zaman Muqabala da Shaik Masussuka. Gayyatarsa da zaman Muqabala kaucewa tsarin mulkin Najeriya ne, da tauye masa hakkinsa a matsayinsa na Dan kasa.
5. Na yarda da kai a matsayin gwamna mai ilimi da hangen nesa, sanin ya kamata da adalci. Ina kara ba ka shawara cewa, Jihar Katsina ba hayaniya da musun fahimtar addini take bukata ba, maimakon haka tana neman wanda zai cece ta daga halin da take ciki, kuma Kai ne ka dace da haka.

Tambayoyi masu wahalar amsawa ga Malaman Ahlis Sunna kan Malam Masussuka.1. Idan kun ce Masussuka Kafiri ne. To wace dok...
20/11/2025

Tambayoyi masu wahalar amsawa ga Malaman Ahlis Sunna kan Malam Masussuka.
1. Idan kun ce Masussuka Kafiri ne. To wace dokar Allah ce da dokar Najeriya ta ce dole sai kun musuluntar da shi?
2. Idan Kun ce bai yarda da littafan Bukhari da Muslim ba, to ku a cikin wani Hadisi ne Manzon Allah SAW ya ce ya bar mana Bukhari da Muslim dole ne mu yarda da su? Ko kuwa wace aya ce ta ce duk wanda bai yarda da Bukhari da Muslim ba Kafiri ne a kai shi kara wajen Gwamnati?
3. Masussuka ya ce shi Kur'ani zai Yi riko zalla. Ku kuma kun ce Shi Kafiri ne. To wane littafi zai rike ya zama Musulmi?
4. Najeriya kasa ce ta Secular kowa na da 'yancin yayi Addininsa yadda ya ga dama yadda ya fahimta, yadda ya ke so ba tare da tsangwama ba. Shi Masussuka ya ce da Kur'ani zai yi addininsa zalla, bai yarda da kowane Hadisi da ya ci karo da Kur'ani ba. To Ina ruwanku da shi? Ku ba sai ku yi addininku yadda ku ka fahimta ba. Ko kuwa wace dokar Najeriya ce ta ce dole sai ya yarda da Hadisi? Da ku ka Kai shi kara ga gwamnati saboda rauninku, to ita gwamnatin da wace dokar Najeriya za ta yi masa hukunci?
5 Shin a Dokar Najeriya akwai hukunci ne da aka tanada ga wanda ya ce shi Kur'ani zai bi, bai yarda da Hadisi ba?
Mutane masu hankali da lura na jiran amsoshin ku.

18/11/2025

Masussuka ya sussuka Gwamna Abba Kabir Yusuf da Kwamandan Hisbah kan auren Zawarawa.

13/11/2025

Wai Ina Malam Lawal Triumph ya shiga? Ya maganar tuhumar Kwamitin Shura? Mu hadu wajen comment

10/11/2025

Ga Bizness Nigeria don bunkasa kasuwancinku da samun Kwastomomi.

Address

No 365, Shaik Ja'afar Mahmud Adam Street, Dorayi Panshekara Road
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tongas Narrative Scope posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tongas Narrative Scope:

Share