HAUSA NEWAS 24 AREWA

HAUSA NEWAS 24 AREWA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from HAUSA NEWAS 24 AREWA, Digital creator, AREWA KANO, Kano.

31/05/2024

'Yan Sanda Sun Cafke Masu Karbar Adai-daita Sahu Na Sata

Jami’an ‘yan sanda a jihar Adamawa sun k**a wasu matasa biyu da ake zargi da karbar babur mai uku na sata.

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta samu ranar Alhamis, inda ta ce ta kuma kwato babur din da aka sace.

“A ranar 28 ga watan Mayu, 2024, rundunar ‘yan sandan Adamawa ta samu bayanai game da wani keken napep da aka sace a kan titin Chochi, Rumde, Yola ta Arewa” in ji rundunar a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai daukar hotonta na SP Suleiman Nguroje.

“Bayan samun labarin, an tura tawagar ‘yan sanda masu sanya ido a hedikwatar Jimeta Divisional ba tare da bata lokaci ba. An yi sa’a, an k**a wani Yusuf Adamu mai shekara 18 da kuma Abdul Salam Abubakar mai shekaru 18 a lokacin da suke kokarin sayar da babur din,” in ji ‘yan sandan.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa, babur din mai kafa uku an sace shi wanda har yanzu ba a k**a wanda ake zargi ba kuma wadanda ake zargin s**a karba.

Nguroje ya ce, “An gano wani Mohammed Sani a matsayin mamallakin babur din mai kafa ukun da aka sace,” in ji Nguroje, ya kuma kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Dankombo Morris, ya yaba da bayanan da jama’a s**a bayar a kan lokaci da s**a taimaka wajen k**a wadanda ake zargin tare da dawo da Adai-daita Sahun.

Daga: Abbas Yakubu Yaura

Wasu ’yan ta’adda sun afkawa al’umomin yankunan kananan hukumomin Mangu da Bokkos da kuma Barkin Ladi a jihar Filato dak...
26/12/2023

Wasu ’yan ta’adda sun afkawa al’umomin yankunan kananan hukumomin Mangu da Bokkos da kuma Barkin Ladi a jihar Filato dake arewa ta tsakiyar Najeriya, inda kusan sama da mutum 100 s**a rasa rayukansu yayin da kuma kaddarori da dama s**a salwanta.
Al’amarin dai ya faru ne a jajiberin ranar bikin Kirsimeti, wanda ya yi sanadin daruruwan mutane barin muhallansu.
Daga tarayyar Najeriya wakilinmu Garba Abdullahi Bagwai ya aiko mana da rahoto.
Farko dai ’yan ta’addan sun fara kai hari ga yankin Bokkos kafin daga bisani ya yadu zuwa wasu sassan yankin Barkin Ladi da Mangu.
A kalla dai ya zuwa yau Talata adadin mutanen da suke kwance a asibiti ya haura dari 3 bayan mumunan raunikan da s**a samu yayin harin.
A lokacin da ya ziyarci yankunan da al’amarin ya faru da yammacin jiya Litinin, gwamnan jihar Filato Mr. Caleb Mutfwang ya yi alla wadai da wannan hari.
Ya ce ya kadu sosai da samun wannan labarin wanda ya yi sanadin mutuwar mutanen da ba su ji ba su gani ba a dai dai lokacin da ake tsaka da shagulgulan bikin Kirsimeti.
“Ina son na nanata cewa al’amarin ya isa haka, ba za mu taba amincewa da ci gaba da irin wannan halayya ta rashin hankali da rashin tunani ba na hare-haren babu gaira babu dalili, wannan abun takaici ne kuma abun kaico.”
Yayin ziyarar dai, gwamnan na jihar Filato yana tare ne da kwamandan rundunar Operation Save Heaven Major Janar Abdullsalam Abubakar. Kwamandan ya ce dakarun rudunarsa sun sami nasara fatattakar maharan, inda a lokacin s**a sami nasarar samun wasu wayoyin hannun maharan.
“Ba za mu huta ba har sai mun kamo wadannan ’yan ta’adda, wanda yanzu haka wayoyin da muka samu sun fara ba mu haske a kan yadda za mu kamo masu laifin domin dai fuskantar hukunci.”
Yanzu haka dai an baza jami’an tsaro a yankunan guda uku, kuma tuni aka fara gudanar da bincike domin gano ainihin musabbabin tagwayen hare-haren. (Garba Abdullahi Bagwai)

Wannan yarinyar ce ta yanke jiki ta fadi saboda hukuncin da kotun daukaka Kara tayi akan gwamnan Kano Abba Gida Gida , k...
25/12/2023

Wannan yarinyar ce ta yanke jiki ta fadi saboda hukuncin da kotun daukaka Kara tayi akan gwamnan Kano Abba Gida Gida , kuma tun daga ranar duk alhamis da litinin sai tayi azumi da niyyar Allah ya baiwa Abba nasara a kotun koli
Cikin hukuncin Allah yau an kaita taga gwamna , Amma baya nan tabbas maryam tana matakur kaunar abba , Maryam dai tana da shekara 14 a duniya tana cikin karamar hukumar kumbotso a unguwar Na'ibawa yenlemo
Ya Allah bamu da karfi bamu da dabara ya Allah ko Dan irin wadannan yara kanana Ya Allah ka tausayawa al'umar jihar Kano ka faranta musu da tabbatar da nasarar Abba a ranar yanke hukuncin kotun koli

25/12/2023

Ma'aikatar Kudi ta Isra'ila ta ce yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza zai iya lashe ƙarin dala biliyan 14 a shekarar 2024, adadin da ya ninka giɓin kasafin kuɗinta kusan sau uku.

An gano wajen da ƙasurgumin ɗan bindiga Halilu Sububu yake hakar ma'adinai da ke jihar Zamfara
25/12/2023

An gano wajen da ƙasurgumin ɗan bindiga Halilu Sububu yake hakar ma'adinai da ke jihar Zamfara

Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Sufuri Na Gwamna Zulum A MaiduguriMotocin kirar bas guda 107 mas...
25/12/2023

Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Sufuri Na Gwamna Zulum A Maiduguri

Motocin kirar bas guda 107 masu amfani da wutar lantarki da iskar gas za’ayi amfani dasu wajen sufuri a Jihar ta Borno da nufin saukaka radadin zafin janye tallafin man fetur, da samar da sufuri mai sauki a Jihar.

Ana sa ran irin wadannann matakai zasu yi tasiri matuka wajen wajen kara imani da kudirorin gwamnati na kawo nagartattun sauye-sauye masu dorewa.

Babu shakka, ‘yan Najeriya zasu cigaba da sanya ido don ganin irin tsare-tsare da sauran jahohin kasar zasu kaddamar don rage radadin cire tallafin mai da ake ciki a kasa.

📸: Gwamnatin Jihar Borno

Ƙasashen Afirka sun dage tuƙuru a 2023 wajen yaƙi da sauyin yanayi, sai dai wani babban ƙalubale kuma shi ne na ganin an...
25/12/2023

Ƙasashen Afirka sun dage tuƙuru a 2023 wajen yaƙi da sauyin yanayi, sai dai wani babban ƙalubale kuma shi ne na ganin an rage yawan fitar da iskar carbon a duniya da kaso 43 a shekaru goma masu zuwa.

Address

AREWA KANO
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HAUSA NEWAS 24 AREWA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share