Mujallar MARUBUTA

  • Home
  • Mujallar MARUBUTA

Mujallar MARUBUTA Mujallar MARUBUTA
Manufa:
Assalamu alaikum warahamatullahi ta’ala wa barakatuh. Don kawo labarai da ayyukan marubuta. Bisa la’akari da rashin wata kafa tsa

05/10/2024

Salisu S Fulani A Matsayin Gidado A Sabon Shirinmu Mai Dogon Zango Mai Suna

MATAR WAYE

Wanda zai Fara Zuwa Ranar Litinin 7 October, 2024.

A Channel Dinmu Mai suna

MATAR WAYE TV

31/05/2024

SAKAMAKON FARKO NA GASAR 2024 AMRL HAUSA BOOK PRIZE.

Biyo bayan nazari mai zurfi da alƙalan gasar 2024 Aliyu Mohammed Research Library (AMRL) Hausa Book Prize s**a yi wajen tace da kuma tantance tsakuren labaran da kuka turo domin shiga gasar 2024 AMRL Hausa Book Prize.

A karshen zagaye na farko, Labarai goma sha biyar (15) ne s**a cancanci shiga zagaye na biyu a gasar shekarar 2024.

Labaran sune kamar haka:

1. WASA DA RAYUWA na ZAINAB ABDULLAHI

2. TUBALIN TOKA na FAUZIYYA SANI JIBRIL

3. DANASANI na HAFSAT SANI

4. MARUBUCIYA na RUFAI ABUBAKAR ADAM

5. KOMAR MATA na MUBARAK IDRIS

6. YAƊIN MAGE na HAUWA ADAM SULEIMAN

7. KANTAFI na NURA ISMAIL ABUBAKA

8. TUBALIN TOKA na ZULAIHA HARUNA

9. FITAR RANA DAGA YAMMA na ISMAIL GAMBO

10. DUNIYAR FATIMA na FATIMA UMAR

11. ABINDA KA SHUKA na UMMI ABBA MUHAMMAD

12. RAYUWATA na FATIMA IBRAHIM GARBA

13. ƊAN DUMA na FAISAL HARUNA HUNKUYI

14. NAƊIN LAUJE na HASSANA LABARAN DANLARABAWA

15. A DALILIN WAYA na LAWAN MUHAMMAD

Waɗennan labarai goma sha biyar (15) sune s**a cancanci shiga zagaye na biyu a gasar shekarar 2024.

Ana buƙatan masu labaran da su turo da cikkaken labarin su mai kalmomi dubu ashirin (20,000) zuwa dudu ashirin da biyar (25,000) ta hanyar amfani tsarin typing na word document kafin karfe goma (10:00pm) na daren ranar laraba 10 ga watan July shekarar 2024, ta lambar WhatsApp (+2349011476342) ko email adireshi ([email protected]), domin shiga zagayen karshe na gasar.

Za’a sanar da wadenda s**ayi nasara a gasar shekarar 2024 a ranar litinin 30 ga watan satumbar shekarar 2024, idan Allah ya kaimu.

Muna Miƙa godiya marar adadi ga zaƙaƙuran marubuta da s**a samu zarafin shiga wannan gasar na shekarar 2024.

Muna muku fatan alkhairi, Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa, Ameen.

Mungode,
Hukumar Gudanarwar 2024 AMRL Hausa Book Prize

GASAR RUBUTATTUN GAJERUN LABARAN HAUSA TAARC. AHMAD MUSA DANGIWA LITERARY FOUNDATIONKamar yadda tsare-tsaren gidauniyar ...
09/05/2024

GASAR RUBUTATTUN GAJERUN LABARAN HAUSA TA
ARC. AHMAD MUSA DANGIWA LITERARY FOUNDATION

Kamar yadda tsare-tsaren gidauniyar adabi ta Arc. Ahmad Musa Dangiwa ta shirya cewar, za a riƙa gudanar da gasa daga lokaci zuwa lokaci akan wasu muhimman lamura da s**a shafi rayuwar al’umma, domin bayar da dama ga al’umma su fito da matsalolin su da kansu.

MAUDU'IN GASA (BURI)
A wannan shekarar 2024, maudu'in gasar zai kasance ya taɓa batutwa da s**a shafi hanyoyin cimma burika da kuma muradu da Ɗan’Adam kan buƙaci cimmawa a rayuwarsa, za a so marubutan su fito a batutuwa da s**a shafi:

• Burukan ko ƙudurorin da rayuwa kan buƙaci cimmawa na Ɗan’adam.
• Ƙalubalen da akan haɗu da su a hanya, wanda wasu lokutta s**an hana cimma waɗannan buruka, ko su zama tarnaƙi ga Ɗan’adam na cimma burinsa na zama wani abu.
• Yadda za a iya gane mene ne burin mutum tun yana ƙarami da yadda za a taimake shi ya cimma wannan burin nasa, ko kuma a sauya mai shi idan ana ganin burin ba wanda ya dace da yanayin rayuwarsa ba ne.
• Matsalolin da ke tattare da rashin cikar buri da abin da hakan kan haifar a rayuwar mai burin.

Tilas masu shiga gasa su yi anfani da salon ayyanawa na gajerun labaran zube na Hausa.

TASWIRAR GASA

An bayar da dama ga marubutan Hausa maza da mata, su aiko da samfurin labarin da za su rubuta mai ɗauke da kalmomi da basu gaza 500 ba kuma kar su wuce 1000. A tabbata an turo da samfurin kai tsaye ga [email protected] daga ranar 8/05/2024 zuwa ranar 15/06/2024. Za a tace da zabar 30 daga cikin samfurin labaran da aka aiko waɗanda s**a fi burgewa a cikin kwanaki sha biyar (20/6/2024-5/7/2024). sDaga nan za a nemi masu waɗannan samfuran labaran guda talatin da su halarci bita domin samar masu da wani horo na musamman kan yadda ake son alabaran su kasance. Sannan su koma su rubuto labari cikakake wanda bai gaza kalma 4000 ba bai kuma wuce dubu biyar ba (5000) daga 1/8/2024 zuwa 1/09/2024. Za a bayyana sha ukun da s**a yi nasara a cikin watan Satumbar 2024./
Za a tace da tsara da kuma buga labaran, a ƙaddamar da su a wani gaggarumin biki da za a shirya a Katsina da yardar Allah.

DOKOKIN RUBUTUN
Domin shiga wannan tsarin samar da gajerun labarai na Hausa wanda zai kasance mai ɗauke da kalmomi 5000, marubuta na da damar su yi bincike da nazari da tuntuɓa na tsawon wata ɗaya kafin aiko da labaran, bayan tantance su da aka yi.
1. Waɗanda s**a yi na ɗaya zuwa na uku a gasar Muhalli, Sutura ta 2020 da gasar Ɗaukar Jinka ta 2022 ba za su shiga wannan gasar ba.
2. Ba a kuma buƙatar sai ana da wani kwali ko satifket na musamman kafin a kasance cikin wannan tsarin samar da labarai, illa iyaka gwaninta da fasahar tsara labaran Hausa. Ana kuma buƙatar rubutun ya dace da batutuwan da s**a shafi burukan rayuwa da duk wani abu da ke da alaƙa da shi.
3. Dole ne ya kasance an yi amfani da ƙa'idojin rubutu bisa daidaitaciyar Hausa.
4. Dole ne a yi rubutun bisa tsarin haruffa masu ƙugiya, kuma rubutun ya kasance an aika shi bisa tsarin Microsoft word ko PDF. Zuwa ga wannan email ɗin [email protected]
5. Wajibi ne labaran su kasance sabbi waɗanada ba a taba shiga wata gasa da su ba ko kuma buga su a wasu jaridu ko zauruka na kafafen sadarwa.
6. Mutum biyu za su iya haɗin guiwa domin samar da labari guda.
7. Wannan gasar buɗe take ga duk marubuta da masu sha’awar farawa, matuƙar da zai iy kiyaye dokoki da ƙa'idojin da aka gindaya.
8. Wajibi ne a aiko da somun taɓi na kalmomi ɗari biyar zuwa dubu (500-1000) a cikin tsawon wata ɗaya.
9. Duk labarin da aka shiga gasar da shi mallakin gasa ne, ba a yarda a sake ɗaukar shi a shigar da shi wata gasa ba ko makamancin haka.
10. Hukuncin da alƙalan gasa s**a yanke shi ne na ƙarshe ba za a sake tattaunawa ko duba hukuncin ba, bayan fitar sakamako.

KYAUTUKAN DA ZA A BAYAR
Za a bada kyautuka ga waɗanda s**a shiga gasar daga na ɗaya zuwa na goma sha uku (13) kuma a buga littafin, a ƙaddamar da shi a yayin bikin bayar da kyautukan.

Don karin bayani a tuntubi wadannan lambobin: 08060767379, 08036954354

DEPARTMENT OF HAUSAFEDERAL UNIVERSITY DUTSIN-MAPMB 5001 DUTSIN-MA KATSINA STATE, NIGERIAGASA! GASA!! GASA!!!SASHEN HAUSA...
20/04/2024

DEPARTMENT OF HAUSA
FEDERAL UNIVERSITY DUTSIN-MA

PMB 5001 DUTSIN-MA KATSINA STATE, NIGERIA

GASA! GASA!! GASA!!!

SASHEN HAUSA NA JAMI’AR TARAYYA DA KE DUTSIN-MA, JIHAR KATSINA NIJERIYA na farin cikin sanar da marubuta da masu sha'awar rubutu cewa, ga dama ta samu da za ku nuna fasaharku da baiwar da Allah ya huwace maku, domin kuwa sashen ya shirya maku GASAR GAJERUN LABARAI NA HAUSA A KAN MATSALAR TSARO A AREWACIN NIJERIYA.

Wannan gasa za ta buɗe wani sabon babi wanda ake da ƙamfar rubutu a kansa, musamman ga ɗaliban manyan makarantu tun daga kan sakandire har zuwa kwalejoji da jami’oin ƙasar nan. Duba da girman asalin matsalar tsaro, wato yadda ta zamar wa al’umma ƙayar kifi a maƙogoro kuma ta yi kaka-gida, musamman a yankin arewacin Nijeriya wato Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya.

MANUFAR GASAR
Manufar wannan gasa ita ce samar da gajerun labaran da za su fito da girman matsalolin da ake fuskanta na tsaro ta sigar labari ta hanyar zaƙulo duk wani abu da ya shafi matsalar ko yake goya wa matsalar tsaro baya a da da kuma yanzu. Misali rikicin Fulani da makiyaya da fashi da makami da rikicin ‘yan banga (‘yan sa kai da mutanen gari) da rikicin addinai ko na gari ko na ƙabilanci ko garkuwa da mutane don kuɗin fansa ko tayar da ƙayar baya ko ta’addancin ɓarayin daji ko ƙwacen ababen hawa kamar mota da babur ko ƙwacen waya ko bayar da bayanan sirri ga ‘yan ta’adda ko goyon bayansu, ko gayyato su su yi ta’addanci domin biyan wata buƙata/cimma wata manufa ko ƙulla wata mu’amalar sirri da su.

Wata manufar kuma ita ce, don a ƙara ilmantar da mutane cikin sigar rubutun zube, irin haɗarin da yake tattare da tashin hankali da kuma fa’idar da take tattare da zaman lafiya da lumana, wanda hakan ne yake zama silar cigaban ƙasa da bunƙasarta.

Haka kuma, labaran za su haska wa gwamnati da al’umma girman yadda matsalar ta hana wa kowa haɗiyar ruwa cikin sa’ida musamman ta fuskar tattalin arziki da zamantakewa da ilimi da kasuwanci da mutuncin mutane da cigaba kowane iri da zaman lafiya mai ɗorewa da sauransu.

ƘA'IDOJON SHIGA GASAR
1. Ba za a karɓi duk wani labarin da ya ci mutuncin wani ko wasu ba, ta fuskar ƙabila yare ko addini ko ɗaura wa wata hukuma laifi kacokam.
2. Ƙagaggen labarin kar ya gaza kalmomi dubu huɗu kar kuma ya wuce dubu biyar (4000-5000).
3. Dole ƙagaggen labarin da za a rubutu ya kasance ya shafi matsalar tsaro ta hanyar fito da girman matsalar tsaron da yadda ta shafi ɓangarori da yawa na rayuwar al’umma da mayar da su baya tare da fito da wasu hanyoyi da za su iya zama mafita kan matsalolin.
4. Dole ne a kula da ƙa'idojin rubutu, kuma wajibi ne a yi rubutun bisa tsarin haruffa masu ƙugiya na Hausa Latin, sannan kuma rubutun ya kasance an turo shi bisa tsarin Microsoft word.
5. Wajibi ne labaran su kasance sababbi waɗanada ba a taɓa shiga wata gasa da su ba ko kuma aka buga su a littattafai ko wasu jaridu ko zauruka na kafafen sadarwa ko gidajen rediyo da talabijin ba.
6. Duk wanda za ya shiga gasar, dole ya zama shi kaɗai, ba haɗin guiwa wajen shigarta ba. Wato dai ana buƙatar ɗaiɗaikun mutane ne kawai mace ko namiji. Haka kuma gasar a buɗe take ga duk wanda ya iya rubutu da harshen Hausa ko da ba a Nijeriya yake ba, matuƙar dai zai iya kiyaye dokoki da ƙa'idojin da aka shimfiɗa.
7. Wajibi ne a aiko da cikakken aiki daga 12 dare na ranar 17 ga watan Afrilu zuwa 12 dare na 30 ga watan Yuli na shekarar 2024.
8. Duk labarin da aka shiga gasar da shi mallakin sashen Hausa na Jami'ar Tarayya Dutsin-Ma ne, ba a yarda a sake ɗaukar shi a shigar da shi wata gasa ba ko a sarrafa shi ta wata hanya ko makamancin haka ba.
9. Hukuncin da alƙalan gasa s**a yanke shi ne maganar ƙarshe ba za a sake tattaunawa ko duba hukuncin bayan fitar sakamako ba.
10. Marubuta za su turo da cikakken sunansu, lambar waya da adireshi a saman shafin farko na labarinsu ta wannan imail (ƙibɗau): [email protected]

KYAUTUTTUKAN DA ZA A BAYAR
Za a bayar da kyauttuka ga waɗanda s**a shiga gasar daga na ɗaya zuwa na uku,sannan daga na uku zuwa na goma kuma za a buga labaran nasu a matsayin littafi a kuma ƙaddamar da shi a yayin bikin bayar da kyautukan.
Za a bayar da kambu ga na ɗaya zuwa na uku, sannan daga na hudu zuwa na shida za a ba su tukuicin kudin alkalami da takardar shaida wadda take ɗauke da sa hannun shugaban Jami'a da Shugaban Sashen Hausa na Jami'ar Tarayya da ke Dutsin-Ma.

SAKAMAKON DA AKE SA RAN GASAR ZA TA SAMAR BAYAN KAMMALATA
Ana sa ran idan an yi wannan gasa za ta haifar da samuwar abubuwa muhimmai kamar haka:

a. Ankarar da mutane irin rawar da kowa zai iya takawa domin magance ko kawo ƙarshen wannan matsala ta tsaro.

b. Samar da littafi guda ɗaya sukutum wanda zai ƙunshi labarai masu ɗauke da maudu’i kan sha’anin tsaro da za a ringa karantawa da nazarta a makarantu tun daga ƙananan makarantu har manya.

c. Daga cikin sakamakon da ake sa ran gani a ƙarshen wannan gasa shi ne zaƙulo zaƙaƙuran marubuta masu baiwa da baiwarsu za ta iya taimakawa wurin magance wasu matsalolin da suke cikin al’umma ta hanyar amfani da alƙalummansu a inda ya dace

d. Gasar na iya zama dalilin shigar da darasin Ilimin Zaman Lafiya da Tsaro (Peace And Security Education) a cikin Manhajar karatun ɗaliban makarantun Firamare da Sakandare.

e. Jawo hankalin ‘yan kasuwa da masu hali da kamfanoni da ƙungiyoyin ‘yan kasuwa da masu zaman-kansu domin su tallafa wa matsalar tsaro domin a kai ƙarshenta domin samun cigaba mai ɗorewa a ƙasa.

f. Fito da girman matsalar tsaro da yadda ta shafi ɓangarori da yawa na rayuwar al’umma da mayar da su baya tare da fito da wasu hanyoyi da In Sha Allahu za su iya zama mafita kan wannan gagarumar matsala.

Domin tuntuɓa ko ƙarin bayani:
07067708766
08036796121
08167600111

Zan kawo sauye-sauye kan yadda ake tafiyar da ƙungiyar ɗaliban Hausa ta BUK - Kabiru Anka FaggeKaranta cikakken labarin ...
07/04/2024

Zan kawo sauye-sauye kan yadda ake tafiyar da ƙungiyar ɗaliban Hausa ta BUK - Kabiru Anka Fagge

Karanta cikakken labarin a nan:

SABON Shugaban Ƙungiyar Ɗaliban Harshen Hausa ta Jami'ar Bayero, Kano, Malam Kabiru Yusuf Fagge (Anka), ya sha alwashin zai kawo sauye-sauye da za su canza yadda ake tafiyar da ƙungiyar a baya. Ya faɗi haka ne bayan an zaɓe shi a matsayin sabon ƙungiyar a ranar Juma’a a zangon karatu na 2022...

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mujallar MARUBUTA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mujallar MARUBUTA:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share