Ganji Hausa Reporter's

Ganji Hausa Reporter's Jarida mai zaman kanta da take kawo muku labaru iriri daga fadin Duniya free of charge 08060886677 zaku aiko da labari a WhatsApp

Tinubu ya naɗa shugaban PenCom Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa Opeyemi Agbaje, tsohon Mataimakin Babban Manaja (AGM) n...
18/08/2025

Tinubu ya naɗa shugaban PenCom

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa Opeyemi Agbaje, tsohon Mataimakin Babban Manaja (AGM) na bankin GTBank, a matsayin sabon shugaban Hukumar Kula da Fensho ta Ƙasa (PenCom).

Agbaje ya taɓa zama Daraktan Gudanarwa a Metropolitan Bank kafin ya bar harkar banki.

TheCable ta rawaito cewa wannan naɗin ya zo ne bayan wa’adin kwanaki bakwai da Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta bayar, inda ta nemi a gaggauta sake kafa hukumar gudanarwa ta PenCom, tare da yin gargaɗin shiga yajin aiki idan gwamnati ta ƙi bin umarnin.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, an bayyana shi a matsayin masani mai tasiri a fannoni na kasuwanci, tattalin arziki da manufofin gwamnati.

Agbaje ya kammala karatu a Jami’ar Ife (wanda yanzu ake kira Jami’ar Obafemi Awolowo), inda ya yi fice a fannin Shari’a a shekarar 1985, kuma Lauya a 1986.

NNPP ta lashe zaɓen cike-gurbin majalisar dokokin Kano na da mazabar Bagwai/ShanonoJam’iyyar NNPP ta lashe zaɓen cike gu...
17/08/2025

NNPP ta lashe zaɓen cike-gurbin majalisar dokokin Kano na da mazabar Bagwai/Shanono

Jam’iyyar NNPP ta lashe zaɓen cike gurbi na mazabar Bagwai/Shanono a majalisar dokokin jihar Kano.

Jami’in tattara sak**akon zaɓen, Hassan Adamu Sh*tu ne ya bayyana haka a yau Lahadi.

Sh*tu ya ce dan takarar NNPP, Ali Hassan Kiyawa, ya samu ƙuri’u 16,198, inda ya doke na APC, Ahmad Muhammad Kadamu, wanda ya samu ƙuri’u 5,347.

Wakilin da ya rasu a mazabar, Halilu Ibrahim Kundila, ɗan jam’iyyar APC ne, kuma ya rasu a watan Afrilu 2024.

Da wannan nasara, NNPP ta ci gaba da zama jam’iyya mai rinjaye a majalisar dokokin jihar Kano da mambobi 26, yayin da APC ke da mambobi 14.

A ranar Asabar, APC ta nemi hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta soke zaɓukan jihar.

Mai magana da yawun APC na ƙasa, Felix Morka, ya bayyana cewa an “cika zaɓen da tarzoma mai tsanani da kuma tada jijiyoyin wuya daga ‘yan daba masu mak**ai a wurare daban-daban.”

Ya ce rahotanni daga Shanono, Bagwai da Ghari sun nuna cewa masu zaɓe sun tsere daga rumfunan ƙuri’a yayin da jami’an tsaro ke ƙoƙarin shawo kan lamarin.

Kuma kwamishinan INEC a Kano, Audu Zango, ya tabbatar da cewa an k**a sama da mutum 100 da ake zargin ‘yan daba ne yayin zaɓen cike gurbin na Bagwai.

Mai magana da yawun NNPP na ƙasa, Ladipo Johnson, ya soki kiran na APC na a soke zaɓen, inda ya bayyana shi a matsayin “ba shi da tushe kuma ba shi da gaskiya.”

Johnson ya jaddada cewa zaɓen ya gudana cikin gaskiya, adalci da lumana, tare da nuni da cewa kasancewar Kano gadon NNPP ne, abin da ba zai yiwu ba shi ne sak**akon ya karkata a wata jam’iyya.

APC ta lashe zaɓen cike gurbi na mazaɓar Ghari/Tsanyawa a KanoJam’iyyar APC ta yi nasara a zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsa...
17/08/2025

APC ta lashe zaɓen cike gurbi na mazaɓar Ghari/Tsanyawa a Kano

Jam’iyyar APC ta yi nasara a zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa da aka gudanar a jihar Kano.

Da yake bayyana sak**akon zaɓen da misalin ƙarfe 6:10 na safiyar Lahadi, jami’in tattara sak**akon zaɓen, Farfesa Muhammad Waziri daga Jami’ar Bayero, ya sanar da cewa Garba Ya’u Gwarmai na jam’iyyar APC ya yi nasara da ƙuri’u 31,472.

Ya doke ɗan takarar jam’iyyar NNPP, Yusuf Ali Maigado, wanda ya samu ƙuri’u 27,931.

An gudanar da zaɓen cike gurbin ne bayan an bayyana zaɓen farko da aka yi a mazabar a matsayin wanda bai kammalu ba.

Nasarar NNPP a zaɓen Bagwai/Shanono ya nuna ra'ayin al'ummar Kano ƙarara -  Kwankwaso Jagoran  jam’iyyar NNPP, Sanata Ra...
17/08/2025

Nasarar NNPP a zaɓen Bagwai/Shanono ya nuna ra'ayin al'ummar Kano ƙarara - Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana godiya ga mutanen mazabar Bagwai da Shanono bisa goyon bayan da s**a nuna wa jam’iyyar a zaɓen cike gurbi da aka kammala.

A wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi, Kwankwaso ya bayyana nasarar ɗan takarar NNPP, Ali Lawan Alhassan, a matsayin babbar nasara, ya na mai cewa hakan ya nuna a fili inda amincin jama’a ya ke yanzu da nan gaba.

Ya kuma yabawa shugabanni da magoya bayan jam’iyyar bisa jajircewa da kuma gudanar da zaɓen cikin lumana da tsari na dimokuraɗiyya.

“Mutanen Bagwai da Shanono sun yi magana a bayyane ta hanyar kada ƙuri’a mai tarin yawa ga jam’iyyar NNPP. Nasarar da Ali Lawan Alhassan ya samu a fili take cewa ga inda amincin jama’armu yake, yanzu da nan gaba,” in ji Kwankwaso.

Ya ƙara jinjinawa jajircewar ‘yan jam’iyyar da magoya baya da s**a yi aiki tukuru domin tabbatar da gudanar da zaɓen cike gurbin cikin lumana da nasara.

DSS sun cafke shugaban ƙungiyar ta'addanci ta Mamudawa a jihar NejaGwamnatin jihar Neja, ƙarƙashin jagorancin gwamna Muh...
15/08/2025

DSS sun cafke shugaban ƙungiyar ta'addanci ta Mamudawa a jihar Neja

Gwamnatin jihar Neja, ƙarƙashin jagorancin gwamna Muhammad Umaru Bago ta sanar da k**a jagoran ƙungiyar ƴan ta’adda ta Mahmuda wato Abubakar Abba.

Kafin kamen nasa Abubakar shine shugaban ƙungiyar da tuni ta fara kai hare-harenta a yankin ƙaramar hukumar Borgu ta jihar Neja da wasu sassan jihar Kwara.

Shafin X na RFI ya rawaito cewa Bago ya ce jami’an tsaron sirri na DSS ne s**a yi aikin kamen, kuma bayan lokacin sun yi nasarar far masa a garin Wawa.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, mai magana da yawun gwamnan ya ce an k**a jagoran ƴan ta’addar ne ba tare da wata turjiya da zata tilasta yin harbi ba.

A cewarsa wannan kamen babbar nasara ne ga ci gaban tsaro a Najeriya, wanda ke nuna yadda gwamnati ke ƙoƙari wajen ganin an kakkaɓe ayyukan ta’addanci a Najeriya.

Gwamnan ya kuma jadadda ƙudurinsa na aiki kafada-da-kafaɗa da gwamnatin tarayya wajen kare Lafiya, rayuka da kuma dukiyoyin al’ummar kasar.

Gwamnatin taraiya ta dakatar da samar da sabbin makarantun gaba da sakandare tsawon shekaru 5Majalisar zartarwa ta ƙasa,...
15/08/2025

Gwamnatin taraiya ta dakatar da samar da sabbin makarantun gaba da sakandare tsawon shekaru 5

Majalisar zartarwa ta ƙasa, karkashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a jiya Laraba ta amince da dakatar da kafa sababbin makarantun gaba da sakandire na tarayya a duk faɗin ƙasar na tsawon shekaru biyar.

Dakatarwar ta shafi jami’o’i, kwalejojin kimiyya da fasaha (polytechnics), da kuma kwalejojin ilimi.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a yayin zaman majalisar.

Alausa ya bada dalilan wannan mataki da cewa babban ƙalubale a fannin ilimi a Najeriya yanzu ba samun damar shiga makarantu ba ne, illa magance yawaitar kafa sababbin makarantun da dama can akwai su.

A cewar sa, hakan ya janyo tabarbarewar ilimi ta hanyar ƙarancin gine-gine da ma’aikata.

"Idan ba mu ɗauki mataki da gaggawa ba, to ilimin gaba da sakandire zai ci gaba da lalacewa kuma kimar ɗaliban Nijeriya za ta zube a idon duniya," in ji Ministan.

Majalisar zartaswa ta Jihar Katsina a karkashin jagorancin Malam Dikko Ummaru Radda PhD CON, ta Amince da aikin mak**ash...
15/08/2025

Majalisar zartaswa ta Jihar Katsina a karkashin jagorancin Malam Dikko Ummaru Radda PhD CON, ta Amince da aikin mak**ashi Mai Sabuntawa domin Samar da Wuta ga Manyan Gidaje 11 da Fadada Lambar Rimi Wind Farm da Karin 10MW na Solar PV.

A wani gagarumin mataki mai hangen nesa na sauya makomar mak**ashi a jihar Katsina, Majalisar Zartaswa ta Jiha, karkashin jagorancin Malam Dikko Umaru Radda, ta amince da kashe kudi Naira 19,898,400,000.00 don samar da wutar lantarki mai karfin 20.1MWp na Solar PV tare da 10.1MWh na tsarin ajiyar baturi (BESS) a fadin muhimman wuraren gwamnati guda 11, tare da karin 10MWp na wutar lantarki a Lambar Rimi.

Wannan gagarumin amincewa ya biyo bayan gabatar da wata takarda mai zurfi daga hannun Mataimakin Gwamna na Musamman kan Harkokin Wutar Lantarki da Mak**ashi, Dr. Hafiz Ibrahim Ahmed, a yayin taron Majalisar Zartaswa na 10 da aka gudanar a jiya.

Wannan kudiri, wanda Kwamitin Kan Samar da Mak**ashi na Madadin ya goyi baya, ya nuna jajircewar gwamnatin wajen amfani da mak**ashi mai sabuntawa a matsayin hanya mai dorewa don rage dogaro da man fetur, rage radadin dogaro da wutar lantarki ta kasa, da kuma cimma ingantaccen tsarin kudi na dogon lokaci.

Za a shigar da tsarin wutar lantarki mai amfani da hasken rana da na batir (solar + BESS) a muhimman wurare da s**a hada da:

* Kamfanonin Ruwa:Ajiwa, Zobe, da Funtua Water Works
* Jami'a: Umaru Musa Yar’adua University
* Asibitoci: General Amadi Rimi Orthopedic Hospital da Turai Yar’adua Maternity Hospital
* Koleji:Hassan Usman Katsina Polytechnic da Isah Kaita College of Education
* Gwamnati da Shari'a:Katsina State House of Assembly da State High Court
* Sauran Wurare: Tashar Booster

Wadannan wurare za su amfana da wutar lantarki mai tsafta, ingantacciya, kuma mai rahusa, wanda zai tabbatar da cewa muhimman ayyuka k**ar samar da ruwa, kiwon lafiya, ilimi, da mulki suna aiki da inganci da kuma dogaro.

Wani muhimmin bangare na shirin shi ne farfado da gidan iska na 10 MW na Lambar Rimi, tare da karin 10 MWp na wutar lantarki mai amfani da hasken rana. Gwamnatin jiha za ta mallaki wannan kadarar mak**ashi mai sabuntawa gaba daya, wanda zai tabbatar da amfanin ta na dogon lokaci ga jihar Katsina.

Za a aiwatar da zuba jarin Naira biliyan 19.89 ta hanyar amfani da farashi mai gasa a duniya don na’urorin hasken rana (solar panels), na’urorin sauya wuta (hybrid inverters), da kuma na'urorin ajiyar baturi (battery storage systems), wanda zai tabbatar da cewa an sami inganci da dawwama.

Dr. Hafiz Ibrahim* maiba Gwamna shawara kan Harkokin Wutar Lantarki da Mak**ashi, ya ce: "Wannan wani mataki ne mai muhimmanci zuwa ga makoma mai haske da dorewa ga jihar Katsina."

Za a fara aikin nan take, kuma za a yi shigarwar a matakai daban-daban domin manyan cibiyoyi su fara amfana da wuri. Wannan aiki yana nuna jajircewar gwamnatin Radda wajen kirkire-kirkire, hadin kai, da ci gaba mai dorewa

Hon Sada Bujawa
S A on media to the Governor of Katsina State

YANZU-YANZU: Shugaban ƙaramar hukumar Nasarawa Amb. Yusuf Ogan Ɓoye ya sauka a ƙaramar hukumar Shanono, bayan kalaman Sh...
15/08/2025

YANZU-YANZU: Shugaban ƙaramar hukumar Nasarawa Amb. Yusuf Ogan Ɓoye ya sauka a ƙaramar hukumar Shanono, bayan kalaman Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Kano kan ƙalubalaɲtãr gwamna Abba Kabir da cewa idan ya isa yau juma'a ya shigø Shanono.

A gobe Asbar ne dai ake zaben cike gurbin ɗan majalisar kananan hukumomi huɗu a jihar Kano.

Me zaku ce?

Tinubu ya naɗa sabon shugaban gidan talabijin na ƙasa, NTAShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi babban sauy-sauye na shu...
15/08/2025

Tinubu ya naɗa sabon shugaban gidan talabijin na ƙasa, NTA

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi babban sauy-sauye na shugabanci a gidan talabijin na ƙasa, NTA, inda ya naɗa Rotimi Richard Pedro, a matsayin sabon Darakta-Janar na gidan talabijin din na gwamnati.

“Sauran manyan nade-naden sun haɗa da Karimah Bello daga Jihar Katsina a matsayin Daraktar Tallace-Tallace, Stella Din daga Jihar Filato a matsayin Daraktar Labarai, da kuma Sophia Issa Mohammed daga Jihar Adamawa a matsayin Babbar Darakta ta Kamfanin NTA Enterprises Limited.

“Pedro, ɗan asalin Legas, fitaccen mai kasuwanci a fannin kafafen watsa labarai da kuma mai ba da shawara, wanda ke da kusan shekaru talatin na kwarewar jagoranci a harkar watsa shirye-shirye, wasanni, da kuma tallace-tallace a faɗin Afirka, Birtaniya da Gabas ta Tsakiya,” in ji sanarwar.

Kotun daukaka kara ta jaddada hukuncin kwace motocin gwamnati sama da 40 daga hannun tsohon Gwamna Matawalle na jihar Za...
15/08/2025

Kotun daukaka kara ta jaddada hukuncin kwace motocin gwamnati sama da 40 daga hannun tsohon Gwamna Matawalle na jihar Zamfara - Gwamnatin Dauda

YANZU-YANZU: Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce ta kammala shirye-shirye domin zaɓen cike gurbi da aka sh...
15/08/2025

YANZU-YANZU: Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce ta kammala shirye-shirye domin zaɓen cike gurbi da aka shirya gudanarwa a faɗin mazabu 16 a jihohi 12 na Najeriya 🇳🇬 a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafin ta na X

MAAN ta nemi taimakon EFCC, DSS da ƴansanda wajen karɓo bashin da manoman masara su ka karbaKungiyar Masu Noman Masara t...
15/08/2025

MAAN ta nemi taimakon EFCC, DSS da ƴansanda wajen karɓo bashin da manoman masara su ka karba

Kungiyar Masu Noman Masara ta Najeriya (MAAN) ta ce ta na haɗa gwiwa da DSS, EFCC da ‘yansanda domin dawo da rancen shirin Anchor Borrowers da aka bai wa manoma tsakanin 2018 zuwa 2021.

Shugaban MAAN na ƙasa, Bello Abubakar, ya bayyana haka a taron manema labarai a Abuja, inda ya ce yawancin manoman da s**a karɓi kuɗin sun ki biyan bashin, suna ɗaukar sa a matsayin “kudin al’umma.” Ya ce ƙungiyar ta tura wasikun tuni, ta kuma kai ƙara ga wasu masu bashi, yayin da ake ci gaba da shari’o’i a kotu.

Abubakar ya bayyana cewa matsalar tsaro da ambaliyar ruwa na barazana ga noman masara a jihohi da dama, yayin da fari ya shafi wasu yankuna.

Ya roƙi gwamnatin tarayya ta samar da yanayi mai sauƙaƙa domin manoma su biya bashin, tare da rage ko yafewa ragowar kuɗin, yana kuma yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu bisa ƙoƙarin tabbatar da samar da abinci.

Address

Zoo Road
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ganji Hausa Reporter's posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ganji Hausa Reporter's:

Share