Arewa Update Plus

Arewa Update Plus An Bude Arewa Update Plus a Facebook Saboda Wallafawa Hausawa Labarai📰🗞️ Pictures, Updates n Promotes
(5)

Kare ya cije mazakutar tsohon ɗan wasan Barcelona, Carles PerezTsohon ɗan wasan Barcelona, Carles Perez, na kwance a asi...
31/07/2025

Kare ya cije mazakutar tsohon ɗan wasan Barcelona, Carles Perez

Tsohon ɗan wasan Barcelona, Carles Perez, na kwance a asibiti a ƙasar Greece bayan da wani kare ya cije shi a mazakuta yayin da ya ke rangadi da karen na sa a Thermi, wani ƙauye kusa da Thessaloniki.

Perez, mai shekaru 27, ya samu babban rauni da ya bukaci dinki guda shida, kuma an garzaya da shi asibiti a Panorama.

Ƙungiyarsa ta yanzu, Aris FC, ta tabbatar da cewa ya samu rauni kuma zai rasa wasan UEFA Conference League da Araz-Nakhchivan.

Kocin ƙungiyar, Marinos Ouzounidis, ya ce Perez ya kamata ya fara wasan kafin wannan lamari ya faru, sai dai sun riga sun shirya madadinsa.

Da ya ke jawabi a yayin taron jin ra'ayoyin al'umma da Majalisar Dattawa ta shirya kan gyaran kundin tsarin mulkin ƙasa ...
27/07/2025

Da ya ke jawabi a yayin taron jin ra'ayoyin al'umma da Majalisar Dattawa ta shirya kan gyaran kundin tsarin mulkin ƙasa na 1999, wanda aka kaddamar da shi a Kano a jiya Asabar, Kawu Sumaila ya ce gwamnoni su ne babbar matsalar da ke daƙile ƴancin ƙananan hukumomi.

Kotun ɗaukaka ƙara ta umarci a mayar da tsohon mataimakin kwamishinan ƴansanda aikiKotun Daukaka Kara da ke Abuja, a jiy...
20/07/2025

Kotun ɗaukaka ƙara ta umarci a mayar da tsohon mataimakin kwamishinan ƴansanda aiki

Kotun Daukaka Kara da ke Abuja, a jiya Juma’a ta bayar da umurnin a gaggauta mayar da ACP James Idachaba, wanda Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yansanda (PSC) ta tilastawa yin ritaya daga aikin.

Mai shari’a Mohammed Danjuma, wanda ya jagoranci yanke hukuncin, ya soke umurnin PSC na cewa Idachaba ya mayar da albashin shekaru takwas.

Kotun ta yanke wannan hukunci ne bayan sauraron karar da lauya Chikaosolu Ojukwu (SAN) ya shigar a madadin Idachaba, inda ta rushe hukuncin da Kotun Ma’aikata ta Najeriya ta yi a baya.

A baya dai, a ranar 15 ga Mayu, 2024, Mai shari’a O.O. Oyewumi na kotun ma'aikata ya yi watsi da karar da Idachaba ya shigar yana kalubalantar tilasta masa ritaya daga rundunar ƴansandan.

Idachaba ya bayyana a kotun farko cewa bayan an yi masa karin matsayi zuwa mukamin mataimakin kwamishinan ƴansanda a 2023, PSC ta dakatar masa da albashi tare da yanke hukunci na korar sa ba tare da “baiwa shi damar kare kansa ba.”

MATSAYATA GAME DA SAUYA SUNAN UNIMAID ZUWA MUHAMMADU BUHARI UNIVERSITY Daga: Omoyele SoworeIna so na bayyana matsayata b...
18/07/2025

MATSAYATA GAME DA SAUYA SUNAN UNIMAID ZUWA MUHAMMADU BUHARI UNIVERSITY

Daga: Omoyele Sowore

Ina so na bayyana matsayata ba tare wani wasar ɓoye-ɓoye ba cewa bana goyon bayan sauya sunar University of Maiduguri zuwa Muhammad Buhari University domin a girmama tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

University of Maiduguri dai wata manuniya ce ta cigaba da ilimi ya samu da kuma kafuwarta a Arewa Maso Gabashin Nijeriya. Ta tsaya ƙyam a lokacin da take ta samu kanta a mawuyacin hali. Kuma jami'ar ta shahara a fannin ilimi, zuzzurfan tunani, da kuma hidima ga bil'adama. Sauya sunan wannan tsangaya mai daraja zuwa sunan tsohon shugaban da a lokacinsa aka ga yanda ake ƙin hukunta masu laifi, rarrabuwan kawunan ('yan ƙasa), da kuma koma bayan tattalin arziki gaskiya abin bai kamata ba, kuma bai yi tsari ba.

Wannan mataki cin fuska ne ga ɗalibai, ƙungiyar tsofaffin ɗalibai, tsangayu da kuma al'ummar da s**a shafe shekaru aru-aru wurin gina kimar da University of Maiduguri ta samu. Wannan wani ƙoƙari ne na shafe wannan ginannen tarihi da ya kamata a yi zuzzurfan nazarinsa ba wai kawai a ringa saka musu da sunayen tsoffin mutane ba.

Ina kira ga Gwamnatin Nijeriya, da Jagororin Jami'ar Maiduguri, da Hukumar Kula da Jami'o'i ta Kasa (NUC) da su lashe amansu game da wannan ƙuduri ba tare da ɓata lokaci ba.

Haka kuma, ina kira ga ɗalibai, da ƙungiyar tsofaffin ɗalibai, da duk 'yan kasar da abin ya shafa da su ƙi yarda da wannan ƙoƙari na ƙaƙaba wasiyyar da bata cancanta ba a kan makarantar da shaharanta ya wuce sunan mutum guda.

Dole mu kare makarantunmu daga murɗiyar siyasa da sauya fasalin tarihi.

Majalisar dokokin Kano ta tabbatar da karɓar ƙorafe-ƙorafe kan shugabar ALGON amma ta ƙaryata rahoton bincikar taMajalis...
18/07/2025

Majalisar dokokin Kano ta tabbatar da karɓar ƙorafe-ƙorafe kan shugabar ALGON amma ta ƙaryata rahoton bincikar ta

Majalisar dokokin jihar Kano ta ƙaryata rahotannin da ke cewa za ta fara binciken Hajiya Sa’adatu Yusha’u, shugabar karamar hukumar Tudun Wada kuma shugabar kungiyar ma'aikatan ƙananan hukumomi, ALGON, a jihar.

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labarai na shugaban majalisar, Kamaludeen Sani Shawai, majalisar ta bayyana ikirarin da aka yi a matsayin “marasa tushe, yaudara, kuma gaba daya karya ce.”

Majalisar ta fayyace cewa Shugaban Masu Rinjaye, Alhaji Lawan Hussaini Dala bai bayar da wata tattaunawa ba ko kuma ya yi magana a bainar jama’a dangane da fara wani bincike a kan Shugaban ALGON.

“Hon. Dala, kamar kowane zababben mamba, kundin tsarin mulki ya ba shi ikon karbar koke daga mazabu. Karbar koke ba ya nufin amincewa da abin da ke cikinta ko kuma wani mataki na doka,” in ji sanarwar.

Majalisar ta kuma yi gargadin cewa rahotannin da ake ta yadawa, musamman ma daga majiyoyin da ba na hukuma ba, suna nuna bata-gari ne na tsarin dokoki, kuma da alama wani shiri ne na lalata mutuncin Shugaban masu rinjaye.

Da take jaddada kudurinta na bin ka’ida, majalisar ta tunatar da jama’a cewa babu wani bincike da zai iya ci gaba ba tare da bin ka’idojin da aka kafa ba, ciki har da yin adalci ga duk bangarorin da abin ya shafa.

Ya yi Allah wadai da yada zarge-zarge marasa tushe ba tare da wata shaida ko tabbaci daga wata majiya ta Majalisar ba.

Lamarin babu dadi ga tsohon Kochin Manchester United Erik ten Hag's. A wasansa na farko:5-1 Flamengo U20 s**a yi nasara ...
18/07/2025

Lamarin babu dadi ga tsohon Kochin Manchester United Erik ten Hag's. A wasansa na farko:

5-1 Flamengo U20 s**a yi nasara akansa a wasan sada zumunci na preseason🫥

Bakaķèn Kayan Da Iyalan Buhari S**a Saka Domin Nuna Jimàmìn Mutuwarśà, Kiŕìstancì Nè, Wanda Kuma 'Ýàn Shì'a Ne Sukà Arò ...
18/07/2025

Bakaķèn Kayan Da Iyalan Buhari S**a Saka Domin Nuna Jimàmìn Mutuwarśà, Kiŕìstancì Nè, Wanda Kuma 'Ýàn Shì'a Ne Sukà Arò Wannan Al'adar, Cewar Sheik Lawal Triumph

Manchester United ta amince da farashin fam miliyan 71 don sayen ɗan wasan gaban Brentford, Bryan Mbeumo.
18/07/2025

Manchester United ta amince da farashin fam miliyan 71 don sayen ɗan wasan gaban Brentford, Bryan Mbeumo.

Sha'irar kasidun fiyayyen Halitta Annabi Muhammad💕 Fatima Tabatul, ta tabbatarwa da gidan jaridar Arewa Update Plus cewa...
18/07/2025

Sha'irar kasidun fiyayyen Halitta Annabi Muhammad💕 Fatima Tabatul, ta tabbatarwa da gidan jaridar Arewa Update Plus cewa Su yan Fairar Shehu Ibrahim Nyas, kuma 'yan Tijjaniyar Shehu Ahmadu Tijjani masu son zaman lafiya ne, domin soyayyar Annabi ita ce rayuwarsu. Zasu kare kima da darajar Manzon Allah da dukkanin rayuwarsu.

Ta kara tabbatar mana cewa, dabiu da ilmin da ta samu daga Shehin ta Shehu Mustapha Mai Salanta abin alharinta ne.

Zamu zo muku da videon Interview nan bada jimawa ba.

DA DUMI-DUMI: Majalisar tarayyar Najeriya ta amince da kirkiro sabbin jihohi 12 Kwamitin Majalisar Dattijai mai kula da ...
18/07/2025

DA DUMI-DUMI: Majalisar tarayyar Najeriya ta amince da kirkiro sabbin jihohi 12

Kwamitin Majalisar Dattijai mai kula da ƙirƙirar jihohi ne ya gabatar da rahoton bayan karatu na uku da s**a yi a ranar Alhamis.

SABBIN JIHOHNI DA AKA AMINCE DA SU

Kudu maso Yamma Jihar Ijebu (daga Ogun), Ibadan (daga Oyo)

Kudu maso Gabas Jihar Anim (daga Anambra da Imo), Adada (daga Enugu)

Kudu maso Kudu Jihar Toru-Ibe (daga Ondo/Edo/Delta), Obolo (daga Akwa Ibom)

Arewa maso Gabas Jihar Savanna(daga Borno), Amana (daga Adamawa)

Arewa maso Yamma Jihar Tiga (daga Kano), Gurara (daga Kudancin Kaduna)

Arewa ta Tsakiya Jihar Okura (daga Kogi), Apa (daga Benue).

Me za ku ce?

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Muhammad Babangida, ɗa ga tsohon shugaban ƙasa, Ibrahim Babangida a matsayin...
18/07/2025

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Muhammad Babangida, ɗa ga tsohon shugaban ƙasa, Ibrahim Babangida a matsayin shugaban Bankin Manoma na ƙasar

Na ji mutuwar Dantata kuma har addu'a ya yi min ta nasarar zaɓe a 2023 - Tinubu Shugaba Bola Tinubu ya bayyana marigayi ...
18/07/2025

Na ji mutuwar Dantata kuma har addu'a ya yi min ta nasarar zaɓe a 2023 - Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana marigayi attajirin Alhaji Aminu Dantata, a matsayin mutum mai kamala, gaskiya da rikon amana.

Tinubu ya bayyana hakan ne a yau Juma’a a Kano yayin da ya ziyarci gidan marigayin domin yin ta’aziyya ga iyalinsa.

Ya ce gudunmawar Dantata ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya da ayyukan alheri sun bar tarihi mai kyau a kasar.

“Ya kasance mutum mai kamala, gaskiya, son taimakawa, da rikon amana, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al'umma hidima da tallafawa marasa galihu,” in ji Tinubu.

Shugaban ya ce ya je Kano ne domin yin ta’aziyya ga iyalin da kuma daukacin al’ummar jihar.

“Na gode muku duka saboda tarbar da kuka yi mini cikin mutunci da kima,” inji shi.

“Kafin zabe, na zo nan domin neman tabaraki kuma ya yi min addu'a sosai don nasara ta a zabe. Na nemi ya min addu'a kuma ya yi min,” in ji shi.

Shugaban ya yi addu’a Allah ya jiƙan marigayin tare da bukatar iyalinsa da su ci gaba da rike gadonsa na tawali’u, hidima, da taimakon jama’a.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Update Plus posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Update Plus:

Share