GARI YA WAYE

GARI YA WAYE Kasance da shafin "GARI YA WAYE"
(2)

Sabon shafin vision FM...👇👇
09/08/2025

Sabon shafin vision FM...👇👇

Akwai 'yan mata da dama a masana'antar Kannywood da kuma shafukan sada zumunta irinsu Tik Tok ko Facebook da ake ta jira...
09/08/2025

Akwai 'yan mata da dama a masana'antar Kannywood da kuma shafukan sada zumunta irinsu Tik Tok ko Facebook da ake ta jiran ganin aurensu.

shin waɗanne ne daga cikinsu kuke tunanin za su yi auren bazata tamkar yadda jaruma Rahama Sadau tayi???

Rikicin daba na ƙaruwa a kano! ‘Yan daba a unguwar Zango da Ƙofar Mata tsakiyar birnin Kano, sun sassari wasu dabbobi a ...
09/08/2025

Rikicin daba na ƙaruwa a kano!

‘Yan daba a unguwar Zango da Ƙofar Mata tsakiyar birnin Kano, sun sassari wasu dabbobi a kasuwar rimi.

‘Yan kasuwar sun shaida wa manema labarai cewa ‘yan dabar sun sassari wasu dabbobin, yayin da s**a sossoki wasu.

Daga cikin dabbobin da aka ji wa rauni akwai Dawaki, da Shanu, da Tumakai.

SHIN INA UBANGIJI YAKE??Anyi wani mutum a kasar Baghdad wanda ke nuna gaba da musulunci sosai, Inda duk ƙasar ba wanda y...
09/08/2025

SHIN INA UBANGIJI YAKE??

Anyi wani mutum a kasar Baghdad wanda ke nuna gaba da musulunci sosai, Inda duk ƙasar ba wanda ya isa ya amsa mishi wasu tambayoyinshi guda 3 dayake yawan tambayar musulman garin.

Wata rana wani yaro ɗan shekara 10 yafito yaji mutumin yana challenging musulunci da musulmai akan hanya domin waɗannan tambayoyi nashi da baisamu amsarsu ba. sai yaron ya tsaya ya saurari mutumin a nutse, nan take ya yanke decision akan zaiyi challenging na mutumin, ya matsa kusa dashi yace yazone domin bashi amsoshin tambayoyinshi, mutumin ya kwashe da dariya da yaga wannan ɗan yaron? 🤔

Daga karshe dai ya amince akan zaiyi facing challenging daga yaron, jama'a s**a taru a gindin wani dutse inda ananne daman ake yin dukkan shela kan muqabala.

Duk jama'ar garin s**a taru a gindin dutsen, mutumin yahau saman dutsen ya ɗaga muryarsa yayi tambayarsa ta farko yace:

Meye Ubangijinka yakeyi yanzu haka?

Yaron yayi tunani kaɗan sai yacewa mutumin yasauko kasa yabarshi yahau saman domin ya bashi amsa, mutumin yace: mene? kanason nasauko ƙasa? yaron yace eh! domin nasamu nabaka amsarka, mutumin yasauko ƙasa ƙaramin yaron yayi wuf da gajerun kafofinshi yayi sama, sai yaron ya amsa da cewa: Ya Allah Mafi Daukaka kazama shaida a gaban waɗannan mutane cewa yanzu kasa wannan mutumin yayi ƙasa, musulmi ƙarami yayi sama.

Jama'ar wajen s**ace: "Takbir"...."Allah-hu-akbar!!!"

Mutumin ya hura hanci sannan ya sake tambaya ta 2 sai yace: "Meye kenan a duniya kafin Ubangijinka?" yaron ya nutsu sai yacewa mutumin ya ƙirga mishi 10 amman ta baya ."

mutumin ya ƙirga:"10, 9 ,8 , 7 , 6, 5, 4, 3, 2, 1,0"

Sai yaron yace, "Meye yazo kafin 0 ?"

mutumin yace: ban saniba, ma'ana babu komai"

Sai yaron yace: "Exactly" tabbas babu abinda kenan kafin Allah domin shine farko tunba farkon"

Jama'a s**a kara: "Takbir!"...."Allah-hu-akbar!!!!"

Mutumin yazama completely frustrated, sai yayi final question dinshi yace: " wani direction Allah yake kalla?"

Yaron yace akawomar candle, aka kawo yacewa mutumin ya kunna, bayan ya kunna sai ya tambayeshi da cewa wani direction hasken ke kalla? sai mutumin yace wannan kuma me kakeson nunamin?

sai yaron yace ka faɗamin wani direction hasken ke kalla? sai mutumin yace: kowani direction hasken nanan.

sai yaron yace: " ka amsawa kanka tambayar. Allah yana ko ina tamkar yadda hasken nan ya karaɗe ko ina, babu inda babu Allah

Jama`a s**a Kara "Takbir!"...."Allah-hu-akbar!!!"

Mutumin yaji daɗin amsoshin yaron ta hanyar ilimi dayayi amfani dasu, inda daga bisani ya karbi musulunci, Anan muqabala ta kare.

Ko kunsan waye yaron? shine daya daga cikin maluman addini wato Imamu Abu Haneefa (Rahimahullah)

Allah Ya ƙara daukaka musulunci
ya kuma ƙara bamu ilimi mai amfani.

GARI YA WAYE
Sir wisdom pen 🖊️🖊️🖊️

Wani tsari kuke ganin yakamata a hau kai domin kawo karshen kwacen waya a Jihar Kano ?  A Shirin mu na MADUBI na karfe 1...
08/08/2025

Wani tsari kuke ganin yakamata a hau kai domin kawo karshen kwacen waya a Jihar Kano ?

A Shirin mu na MADUBI na karfe 10 Na safe zamu kasance tare daku domin karanto sakonnin ra'ayoyinku a cikin Shirin kai tsaye.

Zaku iya turo mana sako a lambar waya 09075471055



https://www.facebook.com/share/1EonVmXjsE/

Kwamitin binciken kwamishinan sufuri Ibrahim Ali Namadi kan zargin belin dillalin kwaya ya mika rahotansa ga sakataren g...
04/08/2025

Kwamitin binciken kwamishinan sufuri Ibrahim Ali Namadi kan zargin belin dillalin kwaya ya mika rahotansa ga sakataren gwamnatin jihar Kano a yau.

Tunda farko gwamnatin Kano ta kafa kwamitin ne domin ya bincika mata abinda ake zargi na karbar beli, bayan da aka zargi kwamishinan da tsayawa a kotu, domin karbo belin Hamisu Danwawu da ake zargi da dillancin miyagun kwayoyi.

Yayin Karbar rahoton Kwamitin, sakataren gwamnatin jihar Umar Farouk Ibrahim yasha alwashin mikawa gwamnan Kano Eng. Abba Kabir Yusuf rahoton, da kuma bada tabbacin cewa gwamnan zaiyi abinda ya dace bisa shawarwarin da kwamitin ya gabatar.

04/08/2025

Muna masu sanar daku komawa kan shafin mu na baya, da fatan zaku cigaba da bibiyar mu a koda yaushe

03/08/2025

Muna yiwa kowa fatan alkhairi, da fatan anyi hutun karshen mako lafiya.

A wani taro da aka gudanar karkashin jagorancin tsohon kakakin majalisa Femi Gbajabiamila, wasu daga cikin ‘yan majalisa...
03/08/2025

A wani taro da aka gudanar karkashin jagorancin tsohon kakakin majalisa Femi Gbajabiamila, wasu daga cikin ‘yan majalisar sun bayyana goyon bayansu, suna masu cewa Tinubu ya nuna adalci da cigaba a dukkan sassan ƙasar.

Sai dai wata ƙungiya daban ta tsoffin ‘yan majalisar ta fito fili tana s**ar wannan goyon baya, tana mai cewa ba su da hurumin wakiltar dukkan Arewa.

Sun bayyana taron da aka yi a Kaduna a matsayin wani shirin siyasa na masu neman amfanin kai, tare da jaddada cewa Arewa na fama da talauci, matsanancin rashin tsaro da rashin aikin yi, wanda gwamnati mai ci ta kasa magancewa.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na ƙasa, Mohammed Idris, ya ce hukumar NBC ce kaɗai ke da ikon janye lasisi...
02/08/2025

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na ƙasa, Mohammed Idris, ya ce hukumar NBC ce kaɗai ke da ikon janye lasisin kowanne gidan rediyo ko talabijin, ba gwamnoni ba.

Ministan ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, dangane da matakin Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, na rufe Gidan Rediyon Badeggi FM bisa zargin tunzura jama’a.

Matakin ya jawo cece-kuce daga kungiyoyi da dama ciki har da Amnesty International, wadda ta soki matakin gwamnatin jihar.

Ministan ya ce gwamnoni ba su da ikon rufe kafar yada labarai kai tsaye, kuma ya tabbatar da cewa za a bi doka da adalci wajen warware lamarin.

Rahoton da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta fitar ya bayyana cewa komishinan sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, y...
02/08/2025

Rahoton da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta fitar ya bayyana cewa komishinan sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya karɓi cin hancin dala $30,000 daga wani shahararren dillalin miyagun kwayoyi, Sulaiman Danwawu, domin tsaya masa a matsayin mai ceto (surety).

Namadi, wanda aka taɓa bayyana a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo a 2013 bisa zargin zamba, ya samu nadin komishina a gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ne bayan zaben 2023.

Wata majiya daga hedikwatar SSS ta ƙasa ta shaida wa DAILY NIGERIAN cewa sun gudanar da bincike cikin sirri game da lamarin kuma sun ba da shawarar a tsige Namadi daga mukaminsa.

Bayan zazzafar s**a daga jama’a, Gwamna Abba Yusuf ya kafa kwamitin bincike don zakulo gaskiyar lamarin cikin mako guda.

Ma'aikatan Jinya a Najeriya sun sanar da janye yajin aikin da suke gudanarwa
02/08/2025

Ma'aikatan Jinya a Najeriya sun sanar da janye yajin aikin da suke gudanarwa

Address

Kano

Opening Hours

Monday 06:00 - 01:00
Tuesday 06:00 - 01:00
Wednesday 06:00 - 01:00
Thursday 06:00 - 01:00
Friday 09:00 - 01:00
Saturday 06:00 - 01:00
Sunday 06:00 - 01:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GARI YA WAYE posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share