03/08/2026
SHIEKH IBRAHIM INYASS (RA) WA'AZIN SA:
Shaihu Ibrahim (RA) ya shagaltu da shiriya da koyarwa da kuma gyara dan Adam, kauyen da ya assasa Madina Baye- wanda ke wajen Kaolack ya zama fitilar ilimi da gyarawa.
Kiran Shaihu Ibrahim (RA) bai tsaya nan ba; ya zagaya kasashen Afirka, da kasashen musulmi, da sauran kasashe da dama, yana yada addinin Allah, da kira zuwa ga Musulunci da kyawawan kalmomi, da yada iliminsa a tsakanin al'umma, yana muhawara da malamai domin bayarwa da samun fa'ida.
Ya ziyarci cibiyoyin ilimi na addinin muslunci daban-daban da s**a hada da Mauritania, Morocco, Tunisia, Jami'ar Al-Azhar ta Masar, Hijaz a Saudi Arabia, Pakistan, India, da China, kuma yana cikin kungiyoyi da dama na duniya da s**a sadaukar da kai wajen daukaka addinin Musulunci.
Ya kasance mataimakin shugaba, kuma daga baya shugaban kungiyar musulmi ta duniya a birnin Karachi na kasar Pakistan, wanda ya kafa kungiyar hadin kan musulmi ta duniya, shugaban kungiyar masu wa'azin addinin musulunci ta Tarayyar Afirka, kuma memba ne a kungiyar hadin kan jami'o'in Musulunci ta Duniya a Rabat kasar Morocco, mamba a majalisar koli ta harkokin addinin musulunci a birnin Alkahira, mamba a cibiyar bincike ta addinin muslunci a birnin Alkahira, kuma mamba a majalisar koli ta addinin musulunci a kasar Aljeriya, da kuma yin aiki a wasu kungiyoyi
Bahrul faidah ✍️✍️✍️