Bahrul faidah

Bahrul faidah أَلَا يَـا رَسُولَ اللهِ فَانظُــــرْلِحَــــالِنَا

وَمُـدَّ لَنَـــا بِالْفَيْـــضِ خَـيْــرًا مُّؤَبَّــدُ

𝙄'𝙢 𝙢𝙪𝙖𝙬𝙞𝙮𝙖 𝙢𝙖𝙨𝙤𝙮𝙞𝙣 𝙜𝙖𝙪𝙨𝙞
𝙄'𝙢 21 𝙤𝙡𝙙 𝙞'𝙢 𝙡𝙞𝙫𝙞𝙣𝙜
𝙞𝙣 𝙠𝙖𝙣𝙤

23/08/2026
sufanci ba matsayin duniya ba ne ko na siyasa ballantana wani ya zauna yace dole wane yafi wane,kubar Allah da bayin sa,...
22/08/2026

sufanci ba matsayin duniya ba ne ko na siyasa ballantana wani ya zauna yace dole wane yafi wane,kubar Allah da bayin sa, zai iya yuyuwa wanda ka ke wulakanta shi yafi wanda kake daukaka shi a wurin Allah.

da ace zama da manyan bayin Allah na sa mutanen kirki cikin rudun raiana wasu bayin Allah,to da sahabban maaiki ba su je wurin SAYYIDI Uwaisul Qarni neman Addua' da albarka wurin sa ba,domin sun zauna da mafi girman halitta.

hanyar Allah wani abu ce mai cike da jarabawa tare da rusa manufar Nafsu baki guda,domin jarabta Annabi musa zuwaga Khidru bayan ga shi yana magana da Allah, hakan wani babban karatu ne da raddi ga duk mai kokarin wulakanta bayin Allah abisa tunanin sa ko don ya tozarta wasu.

hanyar sanin Allah acikin bayin sa tana da girma da fadi ba kamar yadda tunanin mu ke ba mu ba.

kullun bayin Allah suna cewa:

a kwai wanda duniya ta san su ,to ammma da kaje malakutu ba za ka taba jin su ba.

a kwai wanda duniya bata taba sanin su ba,amma da kaje malakutu sai kaji sunayen su.

akwai wanda a kwai sunan su aduniya da malakutu.

duk da kowane mutum yana fassara rayuwa ne ko Addini abisa aladar da tamai tasiri ko manufar nafsu,to ammma babu mai gane manufar Allah abisa haqiqa sai wanda ya wuce tasirin alada da nafsu.
Bahrul faidah ✍️✍️✍️

Ga kadan daga chikin wata kissa ta maulanmu SHEIKH IBRAHIM NIASSE 👇👇👇👇WATA RANAA birnin Lagos Nigeria, wata Mata sunanta...
09/08/2026

Ga kadan daga chikin wata kissa ta maulanmu SHEIKH IBRAHIM NIASSE 👇👇👇👇
WATA RANA

A birnin Lagos Nigeria, wata Mata sunanta Dr. Maryam ta kasance babbar likitace amma a lokacin ba Musulma ba ce sai Allah ya jarabceta da wata matsananciyar rashin lafiya. Anyi mata gwaje-gwaje da magunguna a wurare da ƙasashe daban-daban amma ba'a sami waraka ba

Daga ƙarshe aka kaita wajen Shehu Sanin Auwal (RTA) domin neman taimako sai yace nima ina da Shehi, kuje wajansa Nan take s**a nufi birnin madinatu Kaolack domin ganawa da Maulanmu Sheikh Alhaji Ibrahim Niasse (RTA) da s**a isa, s**a zo da manyan akwatunan kuɗi domin bayar da kyauta Amma Maulana Shehu Ibrahim Niasse (RTA) ya nuna rashin sha'awar sa ga dukiya, yace Bana son kuɗinku. Sharadina guda ɗaya ne, idan Allah Ya bata lafiya ku musulunta."

Sai s**a amince cewa ita da mijinta tare da 'ya'yan su zasu shiga musulunci idan ta samu lafiya Shehu (RTA) ya ɗauki Tasbihinsa, ya sanya shi cikin ruwa, yayi addu'a sannan ya bata ruwan Tasha, tana sha sai ta fara amai mai ƙarfi Bayan ɗan lokaci wani abin mamaki ya fito daga bakinta.

Shehu (RTA) ya umarci a ƙone abin nan nan take da ikon Allah, bayan anyi haka sai matar ta miƙe cikin ƙoshin lafiya, tamkar ba itace kefama da ciwo ba nan take ita da mijinta da 'ya'yanta s**a karɓi addinin Musulunci wannan yana nuni da yadda Maulana Sheikh Ibrahim Niasse (RTA) ya kasance mai sadaukarwa ga addini, ba mai neman dukiya ko abin duniya ba

Allah ka Albarkaci Rayuwar mu domin Albarkar Sheikh Ibrahim Niasse (RTA) Ka biya mana bukatun mu na alkairi duniya da lahira kabar mu da sonsa duniya da lahira Ameen🤲thumma Ameen🤲

Bahrul faidah ✍️

Nayi matuƙar tsorata da aikin da ya gabata yau Lahadi 02-08-2026 da abin da gani a aikin gayyar Masallacin Madinatu Shei...
03/08/2026

Nayi matuƙar tsorata da aikin da ya gabata yau Lahadi 02-08-2026 da abin da gani a aikin gayyar Masallacin Madinatu Sheikh Muhammad Ngibrima Zilma'arif Nguru.

Bakomai akayi na damuwa ko tashin hankali ba, a'a kawai naga iyalan (Matan) Maulana Khalifa Shehu Fatihul Aglaƙ (Rta) suna ɗaukar kwangiri akan su suna hawa sama suna kai kwababben siminti.

Duk da cewa mun saba ganin ƙannensa maza da mata, ƴaƴansa maza da mata, amma dai lallai aikin yau yazo da wani irin ishara da ramzy, wadda ni dai ban taba gani ba.

Allah mun tuba da ganin aikin mu, mun tuba da ganin munyi ko anyi damu, Allah saboda buwayar wannan Dattijon da yake jagorantar masallacinka maɗaukaki ka amintar damu.

Bahrul faidah ✍️✍️

SHIEKH IBRAHIM INYASS (RA) WA'AZIN SA:Shaihu Ibrahim (RA) ya shagaltu da shiriya da koyarwa da kuma gyara dan Adam, kauy...
03/08/2026

SHIEKH IBRAHIM INYASS (RA) WA'AZIN SA:

Shaihu Ibrahim (RA) ya shagaltu da shiriya da koyarwa da kuma gyara dan Adam, kauyen da ya assasa Madina Baye- wanda ke wajen Kaolack ya zama fitilar ilimi da gyarawa.

Kiran Shaihu Ibrahim (RA) bai tsaya nan ba; ya zagaya kasashen Afirka, da kasashen musulmi, da sauran kasashe da dama, yana yada addinin Allah, da kira zuwa ga Musulunci da kyawawan kalmomi, da yada iliminsa a tsakanin al'umma, yana muhawara da malamai domin bayarwa da samun fa'ida.

Ya ziyarci cibiyoyin ilimi na addinin muslunci daban-daban da s**a hada da Mauritania, Morocco, Tunisia, Jami'ar Al-Azhar ta Masar, Hijaz a Saudi Arabia, Pakistan, India, da China, kuma yana cikin kungiyoyi da dama na duniya da s**a sadaukar da kai wajen daukaka addinin Musulunci.

Ya kasance mataimakin shugaba, kuma daga baya shugaban kungiyar musulmi ta duniya a birnin Karachi na kasar Pakistan, wanda ya kafa kungiyar hadin kan musulmi ta duniya, shugaban kungiyar masu wa'azin addinin musulunci ta Tarayyar Afirka, kuma memba ne a kungiyar hadin kan jami'o'in Musulunci ta Duniya a Rabat kasar Morocco, mamba a majalisar koli ta harkokin addinin musulunci a birnin Alkahira, mamba a cibiyar bincike ta addinin muslunci a birnin Alkahira, kuma mamba a majalisar koli ta addinin musulunci a kasar Aljeriya, da kuma yin aiki a wasu kungiyoyi
Bahrul faidah ✍️✍️✍️


Assalamualaikum da farko muna godiya ga Allah sakamakon kyakykyawar gwamnati da muka samu da ta dauki almajirai wato mah...
30/07/2026

Assalamualaikum da farko muna godiya ga Allah sakamakon kyakykyawar gwamnati da muka samu da ta dauki almajirai wato mahaddata al qur Ani mai girma wajen koya musu sana u I a qarqashin (hon. Mai mala buni) bisa kyakykyawar manufarta akan almajirai da Kuma daliban islamiyya qarqashin jagorancin (DR) malan Umar abubakar duba ga matsayinsa na shugaban almajirai na JAHAR YOBE Baki Daya Allah ya Saka masa da alkhairi

Wanda insha allahu yanzu haka suna sa ran tafiya I T F Wanda aka fi sani da practical Wanda aka horas dasu na tsawon watanni hudu Wanda Kuma zasu dauki wasu kwanaki suna Yi Wanda idan sundawo za abawa kowa kayan aiki da Kuma jari Wanda zai dogara da kansa Wanda sunkai adadin almajirai 200 Wanda Babu abinda zamu ce ga gwamnatin jahar yobe ta hon mai mala buni sai dai godiya
Bahrul faidah ✍️✍️✍️

SHEHU TIJJANI ABUL ABBAS (16)Me Shehu Tijjani ya ce a kan Haƙiƙar Muhammadiyya?Shehu Tijjani yana cewa ita ce tushen sam...
28/07/2026

SHEHU TIJJANI ABUL ABBAS (16)

Me Shehu Tijjani ya ce a kan Haƙiƙar Muhammadiyya?

Shehu Tijjani yana cewa ita ce tushen samuwar halittu baki ɗaya, kuma ita ce hanyar da Allah Ya sanya dukkan halitta take ci gaba da wanzuwa.

Saboda haka, wannan haƙiƙa tana nan a ko'ina cikin halitta, kuma ba ta taƙaitu ga wani lokaci ko wani wuri ba.

Yayin da Shehu Tijjani ya ƙara da sharhin wannan baiti daga ƙasidar Hamziyyah ta Imam al-Būṣīrī:

"Kai ne fitilar kowace ni'ima; babu wani haske da yake bayyana face daga haskenka, wanda shi ne hasken haskaka baki ɗaya."

Sai ya ce:

"Manzon Allah shi ne fitila mai haskakawa ga kowace halitta da Allah Ya halitta, ba tare da banbanci ba, a kowane zamani da kowane hali. Babu wani haske, shiriya ko walƙiyar ilahi da take bayyana a ko'ina cikin sararin samaniya sai ta hanyar haskensa. Kuma dukkan halittu suna rayuwa ne da taimakon haskensa ba tare da wani keɓantacce ba."

Wannan yana nuna cewa hasken Annabi ya game dukkan halitta, domin Allah Ya sanya shi ya zama hanyar da falalolinsa da rahamarsa suke bayyana ga duniya.

Shehu Tijānī ya ci gaba da bayyana wannan ma'ana wajen bayanin alaƙar Haƙiƙar Muhammadiyya da darajoji da matsayai.

Shehu Tijjani ya ce salatin da Allah Maɗaukaki Ya yi wa Annabinsa wanda Alƙur'ani ya ambata yana daga cikin manyan asiran da s**a shafi samuwar halitta da kuma kasancewar tasirin Muhammadiyya a ko'ina cikin halitta.

Ba wai Manzon Allah yana da alaƙa da dukkan halittu kaɗai ba; a'a, yana da kusanci da kowace halitta fiye da yadda ita kanta take da kanta.

Lokacin da aka tambayi Shehu -Tijānī ma'anar fadin Allah Madaukaki:

"Annabi ya fi kusa da muminai fiye da kawunansu."

Sai ya amsa cewa:

"Allah Ya ba Manzon Allah cikakken iko da tasarrufi a kan dukkan matakai na halitta da kowane abin da Ya halitta. Yana da hukunci da umarni a cikin kowace halitta, gwargwadon yadda Allah Ya so. Dukkan halittu ko manya ko ƙanana, ko abin da ake iya gani ko wanda ba a iya gani duk suna da matsayi a wurin Allah. Kuma ta wannan fuskar ne Manzon Allah yake kusa da kowace halitta fiye da yadda take kusa da kanta."

Bahrul Faidah ✍️✍️✍️

Yau Laraba, Shekaru 53 cif da rasuwar, Gwarzon Waliyyin Allah, Sheikh Muhammadu Ngibirima Zulma Arif (R.A) Ya rasu ranar...
22/07/2026

Yau Laraba, Shekaru 53 cif da rasuwar, Gwarzon Waliyyin Allah, Sheikh Muhammadu Ngibirima Zulma Arif (R.A) Ya rasu ranar Laraba, 07 Safar, 1395H, 19 Fabrairu, 1975M, Bayan Sallar Asuba a wannan gari na Nguru

Shekaru Hamsin da uku sun shuɗe da rasuwarsa, amma har yau hasken iliminsa, tarbiyyarsa da kyawawan ayyukansa na ci gaba da haskaka zukatan al'umma.

Allah Ya ƙara ɗaukaka darajarsa, Ya yalwata masa rahama, Ya haɗa mu da shi a Aljannatul-Firdaus, Āmīn 🙏🤲🏻

Bahrul Faidah ✍️

SHEHU DAHIRU USMAN BAUCHI (R.T.A) - Idan zai Tafsiri baya duba littafi.- Hannunsa rike da charbi yana ja lokaci guda.- B...
18/07/2026

SHEHU DAHIRU USMAN BAUCHI (R.T.A)

- Idan zai Tafsiri baya duba littafi.

- Hannunsa rike da charbi yana ja lokaci guda.

- Ba zai zaman Tafsiri daya zuwa biyu ba sai wasu sun zo sun Musulunta.

- Duk abinda zai fadi, komin tsawon bayani, baya manta kan ayar da ya tsaya.

- Duk inda mai jan baki yayi tuntube, take yake tayar dashi.

🌿 Bahrul faidah ✍️🌿

Address

Badawa Layout
Kano
654321

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bahrul faidah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bahrul faidah:

Shortcuts

Share