
25/06/2025
Yanzu haka wani bidiyo yana yawo — Bello Turji, ɗan ta’adda da ya addabi Arewa, yana nuna gawarwakin sojojin Najeriya kamar wani gwarzo.
Wannan ba karamin bala’i ba ne.
Wannan kaskanci ne ga ƙasa baki ɗaya.
Wannan hujja ce — cewa gwamnatin Najeriya ta gaza, ba don ba za ta iya ba, sai don ba ta damu ba ne.
Me ya sa Turji ke yawo da bindiga a arewa?
Saboda ba ya barazana ga gwamnati.
Kai ne me mata barazana.
Matashin da ba shi da aiki.
Ƙaramar yarinya da yunwa ya hana ta bacci.
Malamin da ke yajin aiki.
Manomi da aka bari a hannun makiyaya.
Dan gwagwarmayar da ake wa barazana.
Kai ne barazanar — shiyasa aka fi saurin daukar mataki akanka, a maimakon Turji.
Mu faɗi gaskiya:
• Jinin waɗannan sojoji ba a hannun Turji kawai yake ba.
• Yana hannun Janarori, Gwamnoni da ’yan siyasa da s**a ci kuɗin tsaro da makamai s**a bar Arewa cikin tashin hankali.
• Yana hannun manyan Arewa da s**a mara wa Bola Tinubu baya don ya cigaba da mulki a 2027, alhalin makabartu na cigaba da cika da matasanmu.
‘Yan Gaskiya ba za su yi shiru ba.
Mun la’anci wannan aika-aika.
Mun yi juyayin sojojin da aka kashe.
Bugu da kari — mun tuhumi gwamnatin da ta kyale Turji yayi wannan kisan.
Ga matasan Arewa:
Idan Turji na iya ɗaukar bindiga, gwamnati kuma ta kyale shi, to mu ma za mu ɗauki gaskiya — mai kaifi fiye da harsashi:
✊🏽 Zaman shiru ya ƙare.
Karfin Jama’a - Sabuwar Duniya