Abubakar sani Ahmad

Abubakar sani Ahmad Long life and prosperity

Yanzu haka wani bidiyo yana yawo — Bello Turji, ɗan ta’adda da ya addabi Arewa, yana nuna gawarwakin sojojin Najeriya ka...
25/06/2025

Yanzu haka wani bidiyo yana yawo — Bello Turji, ɗan ta’adda da ya addabi Arewa, yana nuna gawarwakin sojojin Najeriya kamar wani gwarzo.

Wannan ba karamin bala’i ba ne.
Wannan kaskanci ne ga ƙasa baki ɗaya.
Wannan hujja ce — cewa gwamnatin Najeriya ta gaza, ba don ba za ta iya ba, sai don ba ta damu ba ne.

Me ya sa Turji ke yawo da bindiga a arewa?
Saboda ba ya barazana ga gwamnati.

Kai ne me mata barazana.
Matashin da ba shi da aiki.
Ƙaramar yarinya da yunwa ya hana ta bacci.
Malamin da ke yajin aiki.
Manomi da aka bari a hannun makiyaya.
Dan gwagwarmayar da ake wa barazana.

Kai ne barazanar — shiyasa aka fi saurin daukar mataki akanka, a maimakon Turji.

Mu faɗi gaskiya:
• Jinin waɗannan sojoji ba a hannun Turji kawai yake ba.
• Yana hannun Janarori, Gwamnoni da ’yan siyasa da s**a ci kuɗin tsaro da makamai s**a bar Arewa cikin tashin hankali.
• Yana hannun manyan Arewa da s**a mara wa Bola Tinubu baya don ya cigaba da mulki a 2027, alhalin makabartu na cigaba da cika da matasanmu.

‘Yan Gaskiya ba za su yi shiru ba.
Mun la’anci wannan aika-aika.
Mun yi juyayin sojojin da aka kashe.
Bugu da kari — mun tuhumi gwamnatin da ta kyale Turji yayi wannan kisan.

Ga matasan Arewa:
Idan Turji na iya ɗaukar bindiga, gwamnati kuma ta kyale shi, to mu ma za mu ɗauki gaskiya — mai kaifi fiye da harsashi:

✊🏽 Zaman shiru ya ƙare.
Karfin Jama’a - Sabuwar Duniya

04/08/2024

# Nigeria Abubakar sani Ahmad Abubakar Sani Turaki

Wata kotun tarayya a Legas ta kori wata kara da ta nemi a cire rubutun Ajami daga jikin takardun kudin Nijeriya, naira.K...
17/07/2024

Wata kotun tarayya a Legas ta kori wata kara da ta nemi a cire rubutun Ajami daga jikin takardun kudin Nijeriya, naira.

Kotun karkashin Mai Shari’a Yellin Bogoro ta ce lauyan da ya shigar da karar ya gaza gabatar da gamsassun hujjoji cewa rubutun yana nuna Nijeriya tana bin tsarin addinin Musulunci, sabanin kasancewarta wacce ba ruwanta da addini, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

Lauyan da ya shigar da karar a 2020, Cif Malcolm Omirhobo, ya bukaci kotun ta umarci Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sauya rubutun ajami daga jikin kudin kasar zuwa na Ingilishi, wanda shi ne harshen da aka amince da shi a hukumance, ko kuma a sauya da daya daga harasan Nijeriya uku, Hausa ko Yaruba ko Igbo.

A yayin shari’ar dai, Babban Bankin Nijeriya ya musa da’awar da mai shigar da karar ya yi na cewa, amfani da Ajami a jikin kudin kasar na nuna Nijeriya ta karkata zuwa ga addinin Musulunci.

05/05/2024
05/05/2024

Idan Allah Yana Son bawa, Sai ya sa ƙaunarsa A cikin Zuƙatan Bayin Allah, Sai Su So shi.

Idan kuma Allah ba ya Son bawa, Sai ya Sanya ƙiyayyar A cikin Zuƙatan Bayin Allah, sai su ƙi shi. ✍️✍️

Address

Dorayi
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abubakar sani Ahmad posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share