DMA TV Hausa

DMA TV  Hausa Barkanku Da Zuwa Shafin Gidan Talabijin Ta DMA TV Hausa Matattaran Labarai Ingattatu Daga Majiya Mai Ingantattarciya

Mota mai dauke da Tankar man fetur ya sake faduwa a hanyan takalafiya dake karamar hukumar lapai a jahar neja a yau misa...
26/10/2025

Mota mai dauke da Tankar man fetur ya sake faduwa a hanyan takalafiya dake karamar hukumar lapai a jahar neja a yau misalin Karfe takwas na safe, amma cikin ikon Allah jam'ian masu aikin kashe wuta wato (fire service) dakuma jami'an Civil defense (NSCDC) sun iso wajen da gaggawa domin daukan matakin gaggawa kafun wuta ta tashi.

Jawabi daga Ahmad Adamu luya A Taron Tallafawa Yara marayu da Mata Aure da mazajensu s**a rasasu Domin dogaro da kansu
26/10/2025

Jawabi daga Ahmad Adamu luya A Taron Tallafawa Yara marayu da Mata Aure da mazajensu s**a rasasu Domin dogaro da kansu

Check out DMA TV Hausa’s video.

Kungiyar Sabon gari youth forum ta Gudanar Da Taron tallafawa Mutane 60 Yara kanana Marayu da Kuma matan aure wayan da m...
26/10/2025

Kungiyar Sabon gari youth forum ta Gudanar Da Taron tallafawa Mutane 60 Yara kanana Marayu da Kuma matan aure wayan da mazajensu sun rasu Ajiya Asabar

Taron dai Wanda aka gudanar a Makarantar U. B. E . Primary school Dake Anguwan kaje Cikin garin Minna Wanda Yasamu Halartan Mayan alummar Mutane maza da Mata

Hon Ahmad Adamu luya
Kansila Mai wakiltar Anguwan Sabon Gari word Yace Dalilin wanan Taron domin tallafawa rayiwar wasu Yara Wayanad iyayen su s**a kasance Masu da karfin turasu Makaranta Tare da baiwa Mata kudin da Zasu tallafawa rayiwarsu wajan Gudanar da sana'ar da zasu dogaro da kansu

Abubuwan da dai aka raba A Taron sune rigar Makarantar Yara tare da takardu Matan aure kuwa aka tallafamasu da tukawne suyar kosai da Kuma mangeda lita Daya da #5,000 domin su fara sana'ar da zasu dogaro da kansu.

Ahmad Adamu luya yayi Kira Ga Al'ummar Sabon Gari word da Su Shigo cikin kungiyar Sabon gari youth forum domin Gina Anguwan tare Inda yayi nuna takaicinsa Akan fukatar Kalubane da anguwan take fama da ita akan matsalar harka Shaye Shaye da Kuma Sara S**a Inda yayi janhakali ga matasa da su kaucewa yarkan Sara s**a suri sana'a da Kuma karatu domin su zama Abin Alfahari ga Al'ummar gobe

Tare da yiwa anguwan sabon gari fatan Alhairi Akan Allah Ubangiji ya zaunar da. Ita lafiya dama birnin Minna Baki Daya

DMA TV Hausa

DA DUMI-DUMI: ‘Yan sanda sun k**a manyan masu fataucin miyagun ƙwayoyi a Jihar Jigawa.Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Jigawa ...
22/10/2025

DA DUMI-DUMI: ‘Yan sanda sun k**a manyan masu fataucin miyagun ƙwayoyi a Jihar Jigawa.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Jigawa ta k**a wasu manyan masu fataucin miyagun ƙwayoyi uku a yayin wani samame da aka gudanar bisa bayanan sirri a sassa daban-daban na jihar.

Mai magana da yawun rundunar, SP Shiisu Lawan Adam, ne ya tabbatar da k**a mutanen cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai.

Ya bayyana cewa, samamen da aka gudanar ranar 18 ga Oktoba, 2025, ya haifar da nasarar k**a waɗanda tuni ‘yan sanda ke bibiyarsu saboda hannu da suke da shi wajen rarraba miyagun ƙwayoyi a cikin jihar Jigawa da wajen ta.

SP Shiisu ya ce a lokacin samamen, jami’an ‘yan sanda sun gano nau’o’in miyagun ƙwayoyi daban-daban.

Kayan da aka kwato sun haɗa da:
Exol (13,505), D5 (1,583), Tramadol (3,572), Diazepam (565), Rubber Solution (2,469), tabar wiwi (block da wraps 886), Suck and Die, Akuskura, Farin Malam (340), da sauran miyagun ƙwayoyi da abubuwan maye (1,042).

An gano waɗanda aka k**a da sunayensu k**ar haka: Muhammad Garba, Musa Garba, da Hudu Ma’ilu, dukkansu mazauna ƙauyen Guneri, gundumar Malamawa, daga Jamhuriyar Nijar.

Ya ƙara da cewa waɗanda aka k**a suna hannun ‘yan sanda yanzu haka ana gudanar da cikakken bincike a kansu, kuma za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala binciken farko.

Kwamishinan ‘yan sanda ya yaba da ƙwazon jami’an da s**a gudanar da samamen tare da jaddada matsayar rundunar kan rashin sassauci ga laifukan da s**a shafi fataucin miyagun ƙwayoyi.

Haka kuma, ya roƙi jama’a da su ci gaba da ba da goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci don taimakawa wajen gano da kuma k**a masu aikata laifuka.

Mai Martaba Etsu Nupe Alhaji (Dr.) Yahayya Abubakar CFR  ya halarci taron babban majalisar sarakunan gargajiya ta Arewa ...
22/10/2025

Mai Martaba Etsu Nupe Alhaji (Dr.) Yahayya Abubakar CFR ya halarci taron babban majalisar sarakunan gargajiya ta Arewa (NTRC), karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III. Wanda ake gudanar da taron a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, na tsawon kwanaki biyu domin tattauna muhimman batutuwa da ke shafar yankin, musamman yadda za a magance matsalar tsaro a Arewa maso Yamma.

Allah bamu lafiya da zaman lafiya a wannan yaki na Arewa da ma kasa baki daya

’Yansanda a Jihar Enugu sun k**a wani matashi mai shekara, mai suna Chinecherem Ugwuagu, wanda ya sanya kayan NYSC domin...
21/10/2025

’Yansanda a Jihar Enugu sun k**a wani matashi mai shekara, mai suna Chinecherem Ugwuagu, wanda ya sanya kayan NYSC domin yin basaja wajen aikata fashi da makami.

Kakakin ’yansanda na jihar, SP Daniel Ndukwe, ya ce an k**a shi a kan hanyar Enugu zuws Onitsha tare da wani babur da ya sato, kaya, katin ATM, da kuma bindigar bogi da ska haɗa da kwali.

Bincike ya nuna cewa Ugwuagu ya shiga gidan wani mutum a 9th Mile, cikin Karamar Hukumar Udi, inda ya tsoratar da shi da bindigar ƙarya sannan ya sace abubuwan da aka samu a wurinsa kafin ya yi ƙoƙarin tserewa cikin kayan NYSC.

’Yan sandan da ke sintiri a hanya s**a lura da shi s**a k**a shi. Za a gurfanar da shi a kotu bayan an kammala bincike.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Enugu, CP Mamman Bitrus Giwa, ya yabawa jami’an da s**a yi aikin da sauri, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba da sahihan bayanai don taimakawa wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Yau, 20 ga Oktoba, 2025, shekaru 14 kenan da aka kashe Muammar Gaddafi a ramin bututun ruwa a Sirte, Libya.Nijer Hausa 2...
20/10/2025

Yau, 20 ga Oktoba, 2025, shekaru 14 kenan da aka kashe Muammar Gaddafi a ramin bututun ruwa a Sirte, Libya.
Nijer Hausa 24

Mai Martaba  Alhaji Umar Bago Tafida |||,  ya nada Adamu Tukura mawogi A Matsayin Sabon Sarkin dogarai  Lapai Nada Sabon...
20/10/2025

Mai Martaba Alhaji Umar Bago Tafida |||, ya nada Adamu Tukura mawogi A Matsayin Sabon Sarkin dogarai Lapai

Nada Sabon Sarkin dogaran Yabiyo Bayan Rasuwar tshon Sarkin dogaran Lapai Wanda yarasatu a watan September

Madarasatul Aisha Academy Farhu Mahd Zarah walimat Sauke Kahuta Minna
19/10/2025

Madarasatul Aisha Academy Farhu Mahd Zarah walimat Sauke Kahuta Minna

Check out DMA TV Hausa’s video.

Walimar Saukar Karatu Alqur'ani Mai girma   Madarasatul Aisha Academy Farhu Mahd Zarah Dake Anguwan Sauke Kahuta Minna
19/10/2025

Walimar Saukar Karatu Alqur'ani Mai girma Madarasatul Aisha Academy Farhu Mahd Zarah Dake Anguwan Sauke Kahuta Minna

Check out DMA TV Hausa’s video.

Hotuna: Yadda Hukumar Kula da Yawon Buɗe Ido ta jihar Kano, haɗin gwuiwa da hukumomin jami'an NDLEA, da na rundunar 'Yan...
19/10/2025

Hotuna: Yadda Hukumar Kula da Yawon Buɗe Ido ta jihar Kano, haɗin gwuiwa da hukumomin jami'an NDLEA, da na rundunar 'Yansanda a daren ranar Asabar, s**a kai samame wani gidan shan sh**ha mai suna Arfat da ke ƙwaryar Kano, inda s**a cika hannu da matasa dake shaye-shaye tare da rufe gidan.

Rundunar Sojin Najeriya ta yi ƙarin bayani kan zargin yunƙurin juyin mulkiRundunar Sojin Najeriya ta yi ƙarin bayani kan...
19/10/2025

Rundunar Sojin Najeriya ta yi ƙarin bayani kan zargin yunƙurin juyin mulki

Rundunar Sojin Najeriya ta yi ƙarin bayani kan zargin yunƙurin juyin mulki
A cikin martaninsu na farko tun bayan yada labarin zargin yunƙurin juyin mulki a kan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Hedikwatar Tsaron Najeriya (DHQ) ta bayyana cewa soke wasu bukukuwa na bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai ba shi da alaƙa da zargin yunƙurin juyin mulki.

Ko da yake sanarwar ba ta karyata kai tsaye cewa wasu jami’an soja ba su da hannu a cikin zargin yunƙurin ba, ta ce binciken da ake yi kan jami’ai 16 da aka k**a “tsari ne na cikin gida da ake gudanarwa akai-akai domin tabbatar da ladabi da ƙwarewa a cikin rundunar.”

Sojojin sun ce an kafa kwamitin bincike domin gudanar da cikakken bincike kan jami’an da abin ya shafa, kuma “ Za a fidda komai a fili game da sak**akon binciken”.

PREMIUM TIMES ta buga cewa kimanin jami’an soja 20 aka k**a bayan hukumomin tsaro sun samu bayanai kan zargin shirin juyin mulki. Rahotanni sun nuna cewa k**a jami’an ya fara ne da mutum 16 a ƙarshen watan Satumba.

Sahara Reporters ce ta fara yada labarin zargin yunƙurin, kuma majiyoyin soja sun tabbatar wa jaridar cewa an k**a jami’an ne bisa zargin wannan shiri.

A cikin sanarwar ta, DHQ ta mayar da hankali ne kan rahoton Sahara Reporters da ya ce an soke liyafar bikin ranar ‘yancin kai ta 1 ga Oktoba saboda wannan zargi.

A cewar sanarwar, an soke bikin ne “domin bai wa Shugaba Tinubu damar halartar muhimmin taron ƙasa da ƙasa a waje, da kuma bai wa sojoji damar ci gaba da ƙoƙarinsu wajen yaƙar ta’addanci, da sauransu.

“Rundunar Sojojin Najeriya na son ta fayyace cewa dukkan zarge-zargen da wannan kafar yada labarai ta yi ƙarya ne kuma na son tada hankali,” in ji sanarwar.
“Soke bikin yana da dalilai na gudanarwa kawai, ba shi da alaƙa da wani yunƙurin juyin mulki.”

DHQ ta roƙi ‘yan Najeriya su yi watsi da abin da ta kira “ƙarya da makiyan ƙasa ke yadawa,” tare da sake jaddada biyayyarta ga Kundi

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DMA TV Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DMA TV Hausa:

Share