MINNA TV 24

MINNA TV  24 Barkanku Da Zuwa Shafin Gidan Talabijin Ta MINNA TV 24 Matattaran Labarai Ingattatu Daga Majiya Mai Ingantattarciya

WhatsApp number 09046599842

INNALILLAHI WAINNA ILAIRRAJU.UNShugaban Wannan Kafar Ta MINNA TV  24 Allah Yamasa Rasuwa Muna fatan Allah Yajikansa Da R...
08/08/2026

INNALILLAHI WAINNA ILAIRRAJU.UN
Shugaban Wannan Kafar Ta MINNA TV 24 Allah Yamasa Rasuwa

Muna fatan Allah Yajikansa Da Rahama Allah Yasa Aljannace Makomarsa Ameen

Duk Da Tsawon Shekaru Takwas Da Aka Yi Ana Damawa Da Kai A Mulkin Buhari, Amma Babu Abinda Ka Taɓuka, Abin Kunya Ƙuri'u ...
07/08/2026

Duk Da Tsawon Shekaru Takwas Da Aka Yi Ana Damawa Da Kai A Mulkin Buhari, Amma Babu Abinda Ka Taɓuka, Abin Kunya Ƙuri'u 16 Ka Samu A Yayin Da Ka Fito Takara A Garinku, Martanin Mawaƙi Davido Ga Tsohon Hadimin Buhari, Bashir Ahmad

Yayin da shi kuma Bashir Ahmad ya mayar masa da martani cewa gasar Grammy guda nawa ka taɓa lashewa a cikin biyar ɗin da aka ba ka damar tsayawa takara?

Sarkin Musulmi Ba Shi Da Alaƙa Da Maganar Cewa A Sake Zaɓar Tinubu, Kuma Za Mu Bada Tukwicin Naira Milyan Biyar Ga Duk W...
07/08/2026

Sarkin Musulmi Ba Shi Da Alaƙa Da Maganar Cewa A Sake Zaɓar Tinubu, Kuma Za Mu Bada Tukwicin Naira Milyan Biyar Ga Duk Wanda Ya Kawo Mana Inda Sarkin Musulmi Ya Ce A Zaɓi Tinubu,

Inji Sheikh Ibrahim Alhasan Saeed Adam Jos da Ustaz Asadussunnah Amore

ALHAMDULILLAH__ fuskar daya daga cikin Yan'b'ndïgar da s**ayo ayari Kenan daren jiya ta wuraren dogon dawa.........🤗Inda...
06/08/2026

ALHAMDULILLAH__ fuskar daya daga cikin Yan'b'ndïgar da s**ayo ayari Kenan daren jiya ta wuraren dogon dawa.........🤗

Inda aka gwabza kazamin yaki tsakanin jajirtattun Yan bangar garin mangoro dake karamar hukumar Mariga da wayanan azzalumai

har aka Samu nasarar k**a mutun biyu a cikin su kuma da ranku Zan saka maku link din video a comment section

Allah ya Kara bawa jamai an tsaron mu nasara Alfarmar annabi saw ❤️❤️

Allah ya kawo mana zaman lafiya a kasar mu Nigeria

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umurci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da ta gaggauta komawa kotu domin janye u...
06/08/2026

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umurci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da ta gaggauta komawa kotu domin janye umarnin da ta samu na dakatar da asusun bankin Gwamnatin Jihar Osun.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Shugaban Ƙasar ya fitar, inda ya bayyana cewa ko da yake ba ya saba tsoma baki cikin ayyukan hukumomin yaƙi da cin hanci, ya damu da lokacin da aka ɗauki matakin, kasancewar Jihar Osun na gab da gudanar da zaɓen gwamna.

Tinubu ya ce bai san da matakin EFCC tun da farko ba, amma ya jaddada cewa bai k**ata a ɗauki wani mataki da zai haifar da zargin cewa Gwamnatin Tarayya na ƙoƙarin yin tasiri kan zaɓen jihar ba.

Saboda haka, Shugaban Ƙasar ya ce ya umarci EFCC da ta janye umarnin kotun tare da dakatar da duk wani mataki da ta ɗauka kan asusun Gwamnatin Jihar Osun, domin kare sahihancin tsarin dimokuraɗiyya da tabbatar da amincewar jama’a ga harkokin zaɓe.

YANZU-YANZU: Mayakan Kawance Kasar Saudiya Sun Kai Hari Ta Sama Yankin Sana'a Na Kasar Yemen Kamfanin dillancin labarai ...
05/08/2026

YANZU-YANZU: Mayakan Kawance Kasar Saudiya Sun Kai Hari Ta Sama Yankin Sana'a Na Kasar Yemen

Kamfanin dillancin labarai na Rasha, TASS, ya ruwaito cewa da sanyin safiyar yau jiragen yaƙin kawancen da Saudiyya ke jagoranta sun kai hari ta sama kan sansanin sojin sama na Al-Dailami da ke arewacin birnin Sana'a, babban birnin Yemen. Har yanzu ba a fitar da cikakken bayani kan irin barnar da harin ya yi ko adadin waɗanda s**a jikkata ko s**a mutu ba.

Manufofin Tinubu Na Bunƙasa Masana’antu Na Samar da Ayyukan Yi – Mohammed IdrisMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Al...
05/08/2026

Manufofin Tinubu Na Bunƙasa Masana’antu Na Samar da Ayyukan Yi – Mohammed Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bunƙasa masana’antu a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata na taimakawa wajen samar da ayyukan yi, ƙirƙire-ƙirƙire da damarmakin tattalin arziki ga ‘yan Nijeriya.

Idris ya bayyana hakan ne yayin rangadin Tawagar Yaɗa Labarai ta Fadar Shugaban Ƙasa zuwa Hukumar Bunƙasa Kimiyya da Injiniya ta Ƙasa (NASENI) da ke Abuja, inda ya ce manufar rangadin ita ce bai wa jama’a damar ganin ayyukan gwamnati kai tsaye.

Ya bayyana NASENI a matsayin muhimmiyar hukuma wajen bunƙasa masana’antun cikin gida ta hanyar kimiyya, fasaha da injiniya, musamman a fannonin mak**ashi mai sabuntawa, aikin gona na zamani da ƙirƙire-ƙirƙire.

Shima Babban Jami’in Gudanarwa na NASENI, Khalil Suleiman Halilu, ya ce hukumar na ƙoƙarin gina masana’antu masu ɗorewa ta hanyar ƙera kayayyaki a cikin gida, inda ya bayyana cewa an kafa sama da masana’antu 20 a ƙarƙashin sabon tsarin hukumar.

Al'ummar Mokwa Sun Haɗa Kai Sun Gina Magudanar Ruwa Da KansuAl'ummar Kpege Wayata tare da 'yan kasuwa da ke kan titin Mo...
04/08/2026

Al'ummar Mokwa Sun Haɗa Kai Sun Gina Magudanar Ruwa Da Kansu

Al'ummar Kpege Wayata tare da 'yan kasuwa da ke kan titin Model Station Road a Mokwa sun haɗa kai wajen gina magudanar ruwa (culvert) a yankin Yagbagba Chamber domin magance matsalar hanyar da ta addabi mazauna yankin.

An yabawa wannan mataki a matsayin abin koyi na haɗin kai da kishin ci gaban al'umma, inda mazauna s**a ɗauki nauyin aikin domin samar da mafita mai ɗorewa ga jama'a.

Mazauna yankin sun kuma gode wa duk waɗanda s**a bayar da gudummawar kuɗi, kayan aiki da ƙoƙari wajen tabbatar da nasarar aikin, suna mai jaddada cewa haɗin kai ne mabuɗin ci gaban Mokwa.

DIRKASHI: Wata ƙungiyar matasan jahar Gombe sun kai koke tare da bukatar EFCC da ICPC su binciki Farfesa Isa Ali Pantami...
04/08/2026

DIRKASHI: Wata ƙungiyar matasan jahar Gombe sun kai koke tare da bukatar EFCC da ICPC su binciki Farfesa Isa Ali Pantami bisa Kadarori da ya mallaka a Najeriya Abuja da Jiddah

NASRUMILLAH: Mataimakin shugaban ƙasurgumin ɗan bindiga Muhammad Gwaska, mai suna Abubakar Dattiya, na daga cikin 'yan b...
01/08/2026

NASRUMILLAH: Mataimakin shugaban ƙasurgumin ɗan bindiga Muhammad Gwaska, mai suna Abubakar Dattiya, na daga cikin 'yan bindiga shida da s**a mutu sak**akon ɓarkewar cutar kwalara a sansanin Gwaska da ke ƙaramar hukumar Anka ta jihar Zamfara. Rahotanni sun ce cutar ta bazu cikin sansanin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar waɗannan 'yan bindiga cikin ɗan ƙanƙanin lokaci.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MINNA TV 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MINNA TV 24:

Shortcuts

Share