15/01/2025
Allah Sarki Rayuwa Tuna Baya 😭😭
Ranar tunawa da mazan jiya
A rin wannan rana ta yau, wato 15-01-1966, kimanin shekaru 59 da s**a wuce, aka kashe Firimiyan yankin Arewacin Najeriya, Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto, da kuma Firaminista Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa, bayan wani juyin mulki da sojoji s**a yi, a ƙarƙashin jagoranci Manjo Chukwuemeka Kaduna Nzeogwu.Tabbas ƴan Arewa ba zasu taɓa mantawa da wannan rana ta 15-01-1966 ba, saboda wannan rana ita ce ranar aka tarwatsa arewa, aka tarwatsa haɗin kan Arewa, aka tarwatsa zaman lafiyarta da kuma cigaban Arewa. Kamar yanda yake a tarihi, Sir. Ahmadu Bello Sardauna yayi iyakar ƙokari wajen haɗa kan Arewa, yayi ƙoƙari wajen samarwa da Arewa wata alƙibla ta siyasa da zamantakewa ta rayuwa.
Sir. Ahmadu Bello Sardauna yayi ƙoƙarin kambama darajar hausawa ƴan Arewa, wanda ta hakane s**a bambanta da sauran ƴan Nigeria ta hanyar suturar su, abincin su, ɗabi'ar su da kuma al'adun su Irin gudunmuwar da Sir. Ahmadu Bello Sardauna ya bayar wajen cigaban yankin Arewacin Najeriya yasa ya zama abin misali da kwaikwayo a gaba-ɗaya sassan yankin Arewa.
Shima Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa yayi ƙoƙari sosai wajen ganin cewa Najeriya ta zama ƙasa ɗaya al'umma ɗaya, yayi ƙoƙari sosai wajen haɗa kan ƴan Najeriya A Kowace ranar 15 ga watan Janairu, rana ce ta musamman ga ɗaukacin jama'ar jihohin Arewa, musamman akan kisan gillar da aka yiwa waɗannan bayin Allah ƴan kishin ƙasa, wato Sir. Ahmadu Bello Sardauna da Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa, bisa la'akari da irin gagarumar gudunmawar da s**a bada wajen gina ƙasar ba tare da nuna wani bambancin ƙabilanci na siyasa ba, ballantana ma na addinai.
Allahu Akbar! Muna roƙon Allah (S.W.T) ya gafartawa mazan jiya Amen
Allah yasa mudace Duniya Da Lahira amen
NKKK HAUSA✍️