NKK Hausa

NKK Hausa Labarai da Jaridu da Hausa

Koken  Nura Kasafi Ga Gwamnati 👇 Allah yasa Ta duba Ayi Aikin 👇👇Dole Fa Hankalin Mu Ya Tashi Akan Harkar Nan Sama Da She...
04/06/2025

Koken Nura Kasafi Ga Gwamnati 👇 Allah yasa Ta duba Ayi Aikin 👇👇
Dole Fa Hankalin Mu Ya Tashi Akan Harkar Nan Sama Da Shekara 10 Muna Kiraye Korayen Azo Ayi Mana Aikin Titunan Mu Amma An Wafantar Damu.

Mun Zaɓi Ɗan Majalisar Tarayya Na APC Ya Kasa.
Mun Zaɓi Ɗan Majalisar Jaha Na APC Ya Kasa
Mun Zaɓi Senator Na APC Ya Kasa

A 2023 Akwai Ɗan Unguwarmu Da Ya Futo Takarar Majalisar Tarayya Amma Muka Kayar Dashi Mu Tura Wakili.

Yau Shekara Biyu Wakili Na Jam'iyar NNPP Wanda Ya Samu Nasara Da Gagarumin Rinjaye a Gayawa Duk Da Cewa Akwai Badaru Umar Gayawa Haka Muka Ƙi Zaɓar Shi Muka Zaɓi Wakili Amma Ya Wafantar Damu.

Dukkan Waɗanda Muke Da Ƙwarin Gwiwa Akan Su Duk Sun Kasa Gwamna Ya Fara Rage Wasu Ayyukan Amma Fa a Halin Da Gayawa Take Ciki Indai Ba Gaba Ɗaya Akayi Aikin Nan Ba Za'a Dena Ƙorafi Ba Saboda Babu Inda Baya Buƙatar Agajin Gaggawa.

Yak**ata Akawo Mana Ɗauki😭
Nura Kasafi ✍️✍️

Wata Sabuwa 👇👇 Jan Hankali ga rundunar yansandan NigeriaWannan hoto da kuke gani dake nuna wasu matasa biyu da yansandan...
01/06/2025

Wata Sabuwa 👇👇
Jan Hankali ga rundunar yansandan Nigeria

Wannan hoto da kuke gani dake nuna wasu matasa biyu da yansandan Nigeria ke Neman su ruwa a jallo ba kayan kowa s**a sata ba kuma basu yiwa kowa komai ba, Babban laifin su bai wuce kasancewar su jajirtattun matasa Masu neman abin kan su ba ta hanyar da dokar Nigeria ta tanada, sai kuma watakila dan sun kasance Masu karamin karfi da s**a ki yadda wani babban kamfani yazo har kasar su yana kokarin murkushe su ba.

Fiye da shekara kenan wani babban kamfani na yan asalin India yayi karar Wadannan matasa wadanda sune Suke da mallakin kamfanin ganyen shayin Y and Z kan cewar sun Satar masa samfurin ganyen shayin su( k**ar yadda Coca Cola s**a taba yin karar Pop Cola)

amma da aka bincika a ofishin trade mark sai aka tabbatar da cewar Y and Z sun bi duk Wata ka’ida hasali Ma hukumar ce ta basu raiista da wannan suna da tambarin da suke amfani da shi

amma abin takaici Wadannan indiyawa wadanda ke ganin suna da karfi suna ta biye biye kan lallai sai sun ci zarafin Wadannan matasa idan har basu Yi saranda sun daina wannan Sana’a ba.

Tun wancan lokaci ake ta kai kawo har sun fara gajiyar da matasan, amma abin mamaki wai kare da tallan tsire jami’ai na ta basu kariya da kokarin muzgunawa Wadannan matasa ta hanyar Yi musu barazana irin wannan.
Kun san dai yadda me Karfi ke fin kwarjin a idon galiban Mahukuntan kasar Nan

Ina rokon Babban sufeton yansandan kasar nan IGP Kayode Egbetokun da ya shiga maganar nan da Kansa domin tabbatar da adalci da kaucewa yin amfani da karfin iko wajen muzgunawa Masu karamin karfi.

Nayi mamakin ganin yadda Jami’an yansanda s**a Yi uwa da makarbiyya cikin wannan lamari tare da yada hotunan Wadannan matasa kai kace abokan Turji ne, kullum Kira ake ga matasa su k**a Sana’a amma kuma babu wani cikakken tsari na kare mutumcin ka,Ban sani ko dan matasan yan arewa ne tun da dai wani lokacin an fi mai da su karkatacciyar kuka.
Ina Kira ga mai girma DSP Barau I Jibril da sauran yan majalisu da ma duk wani me hali da yayi amfani da matsayin sa wajen taimakon Wadannan matasa yan Kano.
Idan baku mance ba k**ar yadda na faro a farko kamfani Pop Cola ma ba Dan Masu shi gwaskaye ba ne da yanzu Suma Ana Fama da su, domin yanzu ko kana da gaskiya Akan iya amfani da iko wajen muzguna maka har kaji cewar Ma ka hakura da kasuwnacin ka kawai saboda wani yana ganin cewar baka isa kayi irin nasa ba.
Dan Allah yan uwa ku taimaka da Neman hakkin wadannan matasa ta hanyar Kira ga IGP da Majalisun kasar nan da su shiga maganar domin Neman halak ba laifi bane.
Nasiru Salisu Zango ✍️ Allah yasa mudace

Tirkashi Wata Sabuwa 👇👇🤔🤔Yadda wani Miji Yayiwa Matarsa Mugun Duka  Har Ya Kumbura Mata Fuska Saboda Ta Zagi Mahaifiyar ...
12/05/2025

Tirkashi Wata Sabuwa 👇👇🤔🤔
Yadda wani Miji Yayiwa Matarsa Mugun Duka Har Ya Kumbura Mata Fuska Saboda Ta Zagi Mahaifiyar shi

Ku Bayyana Mana Ra'ayinku Jama'a Yayi Dai Dai Ko Baiyi Dai Daiba
Allah Yasa mudace


14/02/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Real King Sadeeq, Ibrahim Kumar Khan

22/01/2025

Babbar shela ga sababbin manyan masoyana! Ahmad Lawal

22/01/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Ishaq Rich, Muhammad Ibrahim, Basiru Sahabi Illela, Sidiya Diaby, Bashir Jibril, King EsmaEel A Adam, Abksadiq Yariman Shairai, Kherdeejerh Ibn Abouberker, Auwal Abbas, Zahraddeen Ismail

Shawara Daga Jamila Ibrahim👇👇Da ace ga mahaifiyar ka chan tana bin maza ko ga mahaifin ka chan Yana bin kananan yara bay...
19/01/2025

Shawara Daga Jamila Ibrahim👇👇
Da ace ga mahaifiyar ka chan tana bin maza ko ga mahaifin ka chan Yana bin kananan yara bayan rasuwar mijinta ko bayan rasuwar matarsa gwara ace Sun sake aure Koda Sun tsufa ...

Kowa da kalar kwayoyin halittar sa , wani har tsufansa yanada sha'awa Yana bukatar ko tana bukatar kulawar namiji ko Yana bukatar kulawar mace ...

Kuna cutar da iyayenku Baku sani ba sabida babanku ya rasu kuce mamanku bazata sake aure ba , ita Kuma sabida tsoron Kar kuzo Kuna cin mutuncin mijinta sai ta hakura da auren gaba Daya Amma a zuciyar ta a takure take , daga baya sabida bazata iya jurewa ba ta dinga aikata zina a boye ..

Yanzu fisabilillahi kunyi mata adalci kenan ?

Idan iyayenku suna single Kuma ba tsufa s**ayi sosai ba kuyi masu tayin aure , ku nemowa babanku mata kuyi masa aure akwai kulawar da matansa kawai ne zata iya , Yana bukatar yayi Hira da mace , Yana bukatar wacce zata dinga debe masa kewa kafin lokacin mutuwar sa yazo ...

Hak**a mamanku duk wani kulawa da zaku Bata bazai Kai ace tanada miji kusa da ita ba 😄

Kuyiwa Allah Kar ku bari iyayenku su fada hallaka ko su mutu da cuta , wani ma namiji cuta ce ke sanadiyar tafiyar sa lahira sabida datti ya makale masa a mara kullun kuta yawon asibiti da tsoho karshe ace stroke ne da sauransu 😅

Wlh akwai matsalar da iyayenmu ke Jin nauyin gaya mana , a matsayinmu na masu hankali ya k**ata mu gane damuwar su ba tareda Sun ce mana komai ba ...

Babu ruwanka da mijin mamanka ko matar babanku , ku basu space su kula da juna , ku cire kishinku ku ajiye gefe daya , kaima lokacin ka na zuwa zaka tsufa kuma zaka bukacin hakan , idan naka yayan s**a hanaka aure ko s**a matsawa matarka ko s**a matsawa mijinki bazakuji dadi ba ...

Masu wannan halin na wlh mama bazata Kara yin aure ba sai ku gyara halayyar ku ..

Ita da tace zata Kara auren ai ta fiku sanin matsalar ta
NKKK HAUSA✍️🙏
Allah yasa mudace

Da Dumi Dumi Jawabi Daga Bakin Sarkin Kano Muhammad Sunusi II 👇👇👇Sarkin ya bayyana haka ne a wajen taron tinawa da fitac...
15/01/2025

Da Dumi Dumi Jawabi Daga Bakin Sarkin Kano Muhammad Sunusi II 👇👇👇
Sarkin ya bayyana haka ne a wajen taron tinawa da fitaccen lauyan nan dan gwagwarmaya na Najeriya, Chief Gani Fawehinmi karo na 21 a jihar Lagos


Tirkashi Abun Babu Dadi😭😭👇👇YANZU MUKE SAMUN LABARIN MARYAM TA JE ABUJA KARBAN iPhone 16 KO? LISSAFI YA KWABE!, DARASIN R...
15/01/2025

Tirkashi Abun Babu Dadi😭😭👇👇
YANZU MUKE SAMUN LABARIN MARYAM TA JE ABUJA KARBAN iPhone 16 KO? LISSAFI YA KWABE!, DARASIN RAYUWA!
Dazu da safe, Manajan gidan hotel na Palasa dake yankin Gwagwalada Abuja ya kai kara ofishin 'yan sanda na Gwagwalada bayan wani mutum ya mutu a dakin hotel din da ya k**a shi da wata karuwa Sunan wanda ya mutu Lawal Ibrahim, sunan karuwarsa kuma Maryam Abba daga birnin Dutsen Jihar Jigawa, wanda sun hadu a social media watanni uku da s**a wuce Abinda ya faru shine, Lawal ya kira Maryam zuwa Abuja, jiya da Daddare ya sauketa a Palasa Hotel s**ayi zina, da Garin Yau Laraba ya waye da misalin karfe 6 na safe s**a sake yin zina, Maryam tace suna cikin yin zina ya fado daga kanta ya suma numfashinsa ya dauke, ta yayyafa masa ruwa bai farfado ba Shine sai ta sanar da ma'aikatan gidan hotel din akazo aka daukeshi aka kai asibiti inda Likita ya tabbatar da Lawal Ibrahim ya mutu, A yanzu haka Maryam tana hannun 'yan sanda an kaita zuwa Force CID Abuja don tabbatar da bincike akan musabbabin mutuwar abokin fasikancinta, abubuwa da aka samu sun hada da kankana da miyagun kwayoyi masu kara karfin jima'i
Darasin da zamu dauka anan shine:
Maryam 'yar Jihar Jigawa ne daga birnin Dutse, ta yiwa iyayenta karya ta taho Abuja domin ayi lalata da ita, abokin lalata ya mutu a kanta lokacin da suke cikin yin fasikanci, Allah ne Kadai ya san ranar da zata kubuta daga wannan tuhuma na kisan kai da ake mata Mutane mu ji tsoron Allah, babu wanda ya san a wani irin yanayi ajali zai zo masa, tabbas akwai abin takaici ace mutum musulmi yayi mummunan karshe irin wannan Matansa da 'ya'yansa da iyayensa, da 'yan uwa da abokansa duk sai sun yi da na sanin saninsa a rayuwa
Haka ita ma yanzu Maryam sai tayi nadamar zuwanta duniya, domin yanzu lissafi ya kwabe mata, iyayenta da 'yan uwanta da sauran samarinta da take yaudara duk zasu san halin da take ciki
Allah yasa mudace Duniya Da Lahira Amen ya Allah
NKKK HAUSA✍️

Allah Sarki Rayuwa Tuna Baya 😭😭Ranar tunawa da mazan jiyaA rin wannan rana ta yau, wato 15-01-1966, kimanin shekaru 59 d...
15/01/2025

Allah Sarki Rayuwa Tuna Baya 😭😭
Ranar tunawa da mazan jiya
A rin wannan rana ta yau, wato 15-01-1966, kimanin shekaru 59 da s**a wuce, aka kashe Firimiyan yankin Arewacin Najeriya, Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto, da kuma Firaminista Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa, bayan wani juyin mulki da sojoji s**a yi, a ƙarƙashin jagoranci Manjo Chukwuemeka Kaduna Nzeogwu.Tabbas ƴan Arewa ba zasu taɓa mantawa da wannan rana ta 15-01-1966 ba, saboda wannan rana ita ce ranar aka tarwatsa arewa, aka tarwatsa haɗin kan Arewa, aka tarwatsa zaman lafiyarta da kuma cigaban Arewa. Kamar yanda yake a tarihi, Sir. Ahmadu Bello Sardauna yayi iyakar ƙokari wajen haɗa kan Arewa, yayi ƙoƙari wajen samarwa da Arewa wata alƙibla ta siyasa da zamantakewa ta rayuwa.
Sir. Ahmadu Bello Sardauna yayi ƙoƙarin kambama darajar hausawa ƴan Arewa, wanda ta hakane s**a bambanta da sauran ƴan Nigeria ta hanyar suturar su, abincin su, ɗabi'ar su da kuma al'adun su Irin gudunmuwar da Sir. Ahmadu Bello Sardauna ya bayar wajen cigaban yankin Arewacin Najeriya yasa ya zama abin misali da kwaikwayo a gaba-ɗaya sassan yankin Arewa.
Shima Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa yayi ƙoƙari sosai wajen ganin cewa Najeriya ta zama ƙasa ɗaya al'umma ɗaya, yayi ƙoƙari sosai wajen haɗa kan ƴan Najeriya A Kowace ranar 15 ga watan Janairu, rana ce ta musamman ga ɗaukacin jama'ar jihohin Arewa, musamman akan kisan gillar da aka yiwa waɗannan bayin Allah ƴan kishin ƙasa, wato Sir. Ahmadu Bello Sardauna da Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa, bisa la'akari da irin gagarumar gudunmawar da s**a bada wajen gina ƙasar ba tare da nuna wani bambancin ƙabilanci na siyasa ba, ballantana ma na addinai.
Allahu Akbar! Muna roƙon Allah (S.W.T) ya gafartawa mazan jiya Amen
Allah yasa mudace Duniya Da Lahira amen
NKKK HAUSA✍️


15/01/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Deeja Dogara, Umar Ibrahim Umar, Balkisu Malami Saliha, Mu'azu Abdulsalam

Da Dumi Dumi Yanzu Yanzu Za a kara kudin man fetur😭 Man Fetur  na iya tsada fiye da yadda ake sayarwa yanzu, kasancewar ...
14/01/2025

Da Dumi Dumi Yanzu Yanzu Za a kara kudin man fetur😭 Man Fetur na iya tsada fiye da yadda ake sayarwa yanzu, kasancewar masu tashoshin mai sun kara farashi da kimanin kaso 4.74 cikin 100.
Wannan karin farashin ya biyo bayan tashin farashin danyen mai a kasuwannin duniya, ciki har da Bonny Light na Najeriya, wanda ya tashi zuwa $80 kowanne ganga a wannan makon daga $73 a makon da ya gabata
Vanguard ta rawaito cewa tuni wasu tashoshin mai, k**ar Swift Depot, su ka kara farashin lodin man fetur zuwa N950 kan kowacce lita daga N907 kowanne lita. Tashar Wosbab ma ta kara farashinta zuwa N950 daga N909 kowanne lita Haka zalika, tashar Sahara ta kara farashin ta zuwa N950 kowanne lita daga N910, yayin da Shellplux ta kara zuwa N960 kowanne lita daga N908 kowanne lita Allah yasa mudace
NKKK HAUSA✍️

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NKK Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share