Ammasco Radio 90.7 FM

Ammasco Radio 90.7 FM Barka da zuwa shafin “Ammasco Radio” Gaskiya Tushen Nasara. Gidan Radio da ke Mayar Da Hankali Wajen Bunƙasa Matasa!

Kungiyar kwallan kafa ta Barcelona ta samu nasara Akan Newcastle daci 2-1, Inda dan wasa Rashford ya lashe kyautar Gwarz...
18/09/2025

Kungiyar kwallan kafa ta Barcelona ta samu nasara Akan Newcastle daci 2-1, Inda dan wasa Rashford ya lashe kyautar Gwarzon dan wasa a wasan Wato Man of the match !!

Shin ya kuke ganin kokarin wannan dan wasa?

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai je jihar Kaduna gobe juma'a domin halatttar ɗaurin auren Nasirudden Yari da Safiyya Sh...
18/09/2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai je jihar Kaduna gobe juma'a domin halatttar ɗaurin auren Nasirudden Yari da Safiyya Shehu. Nasirudden dai ɗa ne ga Sanata Abdul'aziz Yari mai wakiltar yammacin Zamfara.

Shugaban zai kuma ziyarci matsar tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari inda zai koma Abuja a gobe juma'a

Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya bayyana haka ne a hirarsa da gidan talabijin na Channels. Ya ce tun...
18/09/2025

Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya bayyana haka ne a hirarsa da gidan talabijin na Channels.

Ya ce tuni yan ƙasa ke ganin alfanun matakan raya tattalin arziƙi da shugaban kasa Bola Tinubu ke ɗauka tin bayan hawansa mulki.

A farkon bincike an ɗauka raunin ba mai tsanani ba ne, amma ƙarin gwaje-gwaje sun nuna cewa lamarin na iya ɗaukar lokaci...
18/09/2025

A farkon bincike an ɗauka raunin ba mai tsanani ba ne, amma ƙarin gwaje-gwaje sun nuna cewa lamarin na iya ɗaukar lokaci kafin ya murmure gaba ɗaya.

Wannan na nufin matashin tauraron na iya daina buga wasanni na wani lokaci, kuma hakan babban koma baya ne ga Barcelona a wannan muhimmin lokaci na kakar wasa ta bana. (Mundo Deportivo)

Ya kuke ganin rashin Dan wasan ga Barcelona?

Atiku Abubakar wanda tsohon mataimakin shugaban Najeriya ne, yana mayar da martani ne kan cikar wa‘adin dokar ta-ɓaci da...
18/09/2025

Atiku Abubakar wanda tsohon mataimakin shugaban Najeriya ne, yana mayar da martani ne kan cikar wa‘adin dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya ayyana a jihar Rivers.

A cewarsa, matakin Tinubu kan gwamnan da majalisar dokokin jihar tun asali ba a yi shi bisa tsarin doka ba.

Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Mak**ashi ta Ƙasa (ECN) Dakta Mustapha Abdullahi ya ce wutar lantarkin mai ƙarfin Mega...
18/09/2025

Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Mak**ashi ta Ƙasa (ECN) Dakta Mustapha Abdullahi ya ce wutar lantarkin mai ƙarfin Megawatt huɗu (4MW) za ta bai asibitin damar rabuwa da layin wutar lantarki na ƙasa baki ɗaya.

Dakta Abdullahi ya ce aikin na daga cikin manufofin ‘Renewed Hope’ agenda na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa wannan tsari zai kawo ƙarshen matsalar yawan yanke wuta a asibitin, lamarin da a baya ya haddasa asarar rayukan marasa lafiya guda uku a lokacin da ayyukan asibitin s**a tsaya cak.

“Da wannan tsari, ba za a sake samun irin waɗannan matsaloli ba. Burinmu shi ne mu samar da mak**ashi mai tsafta da nagarta, wanda zai ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiya tare da inganta rayuwar ƴan Najeriya”, in ji shi.

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar da sak**akon jarrabawar wannan shekara ta 2025.S...
18/09/2025

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar da sak**akon jarrabawar wannan shekara ta 2025.
Sak**akon ya nuna cewa kashi 60.26 cikin 100 na waɗanda s**a samu kiredita biyar zuwa sama ciki har da darussan Lissafi da Turanci.
Shugaban hukumar Farfesa Ibrahim Wishishi ya shaida wa BBC cewa jihar Kano ce kan gaba a yawan ɗaliban da s**a samu nasara a jarrabawar a faɗin wuraren da hukumar ke shirya jarrabawar da s**a haɗa da wasu ƙasashen Afirka.
Cikin wata sanarwa da gwamnatin Kanon ta fitar ta ce wannan ne karon farko cikin shekara 25 da jihar ta samu wannan nasara.
Shugaban na NECO ya ce cikin ɗalibai 1,358,339 da s**a rubuta jarrabawar, yayin da 818,492 ne s**a samu kiredit a darussa biyar da s**a haɗa da Turanci da Lissafi.

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta k**a Ifeanyi Eze Okorienta, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar IPOB mai neman ...
17/09/2025

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta k**a Ifeanyi Eze Okorienta, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar IPOB mai neman ɓallewa daga Najeriya.

Dakarun sun damƙe kwamandan wanda ake yi wa laƙabi da "Gentle de Yahoo, sun kuma kwato mak**ai da s**a hada da bindigogi kirar Turai da albarusai da kuma kakin sojoji da na 'yan sanda.

Jama'an tsaron sun bayyana cafke Eze a matsayin wani babban koma-baya ga ƙungiyar ta IPOB da sashen ƙungiyar mai ɗauke da mak**ai da ke kudu-maso-gabashin ƙasar.

Jami’ar European American University zata karrama fitaccen mawaki, Dauda Kahutu Rarara, da digirin girmamawa.Wannan karr...
17/09/2025

Jami’ar European American University zata karrama fitaccen mawaki, Dauda Kahutu Rarara, da digirin girmamawa.

Wannan karramawar ta zata ɗora masa sabon laƙabi na Dr. Dauda Kahutu Rarara, za dai a bashi ne a matsayin girmamawa kan rawar da yake takawa wajen bunƙasa al’adu da nishadantar da jama’a a Najeriya, k**ar yadda jaridar Leadership Hausa s**a wallafa.

Ku kasance da Ahmad Umar Musa a Zangon dare na sashin gabatar da shirye-shiryen gidan radiyon Ammasco Yau Laraba 17 09 2...
17/09/2025

Ku kasance da Ahmad Umar Musa a Zangon dare na sashin gabatar da shirye-shiryen gidan radiyon Ammasco Yau Laraba 17 09 2025

Aliko Dangote ya faɗi hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai a matatar mansa da ke Legas.Hamshaƙin attajirin na Af...
17/09/2025

Aliko Dangote ya faɗi hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai a matatar mansa da ke Legas.

Hamshaƙin attajirin na Afirka ya kuma ce direbobin tankokin man na kamfaninsa na da damar shiga ƙungiyar NUPENG ba tare da an tursasa musu ba.

Hakan ya biyo bayan cikakken bincike da hukumomin kasar Saudiya s**a gudanar, tare da tabbatar da cewa mutanen da ake za...
17/09/2025

Hakan ya biyo bayan cikakken bincike da hukumomin kasar Saudiya s**a gudanar, tare da tabbatar da cewa mutanen da ake zargin basu da laifi, bayan sun shafe makonni 4 a tsare.

Waɗanda aka saki sun haɗa da Hajiya Maryam Hussain Abdullahi, Hajiya Abdullahi Bahijja Aminu, da Malam Abdulhamid Sadiq.

Rahotonni sun bayyana cewa a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano aka sanyawa mutanen miyagun kwayoyi a cikin kayansu, yayin da suke shirin tafiya zuwa kasar Saudiya domin gudanar da aikin Umara, inda suna isa birnin Jiddah aka k**a su.

Address

Media House Plaza Sani Marshall Road
Kano
700282

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ammasco Radio 90.7 FM posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category