AREWA TODAY

AREWA TODAY Kasance Damu Dan samun Ingantattun
*Labarai
*Rahotannin zaku iya bayyana ra ayoyinku ta wannan shafi cikin girmamawa bisa doka batare da cin zarafi ba

Ko jinjirin jaki bai kai matar nan taurin kai ba. Dama na san abunda zai faru kenan. Rigimar yanzu zata koma tsakanin Ab...
20/09/2025

Ko jinjirin jaki bai kai matar nan taurin kai ba. Dama na san abunda zai faru kenan. Rigimar yanzu zata koma tsakanin Abba Galadima da Presido. Ita kuma zata goyi bayan Presido ne. Shi Presido tsohuwar soyayya zata taso, shi kuma Abba Galadima zai nace kan mayar da matarsa.
Galadanci II

Sana'a Ce Ta Kawo Ni Garin Obajana Ba Yawon Baŕiki Bà, Cewar Fatima Umar, Direbar Tirelar Kamfanin Dangote
10/09/2025

Sana'a Ce Ta Kawo Ni Garin Obajana Ba Yawon Baŕiki Bà, Cewar Fatima Umar, Direbar Tirelar Kamfanin Dangote

Sheik Tijjani Usman Zangon Barebari Kenan, Shehin Da Ya Fara Yin Mauludin Manzon Allah S.A.W A NijeriyaWani abu da Shehi...
07/09/2025

Sheik Tijjani Usman Zangon Barebari Kenan, Shehin Da Ya Fara Yin Mauludin Manzon Allah S.A.W A Nijeriya

Wani abu da Shehi Na 'Yar Mota, shine duk ziyarar da yake kaiwa kasar Saudiyya bai taba taka kasar Madina da takalmi ba, ma'ana duk inda zai shiga babu takalmi yake yawo, hujjarsa kuma ita ce saboda a kasar Annabi SAW ya yi rayuwarsa.

Allah Ya kara kusanci.

Labarin Rariya

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa Shugaban Mulkin Sojin NijarJanar Abdoulramane Tchiani ya tallafa wa jarumin Kannywood Malam Na Ta...
03/09/2025

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa

Shugaban Mulkin Sojin NijarJanar Abdoulramane Tchiani ya tallafa wa jarumin Kannywood Malam Na Tala'ala wanda ke kwance a gadon asibiti.

Jarumin wanda ya tabbatar da hakan a wani bidiyo da ya fitar, ya ce Shugaban Ƙasar ya ƙirashi a waya kuma ya tura masa da kuɗaden da ya ce adadinsu ba zai faɗu ba a yanzu.

DA DUMI-DUMI: Jigawa za ta kasance jiha ta farko a Arewacin Najeriya da ta fara samar da wutar lantarki mai zaman kanta ...
31/08/2025

DA DUMI-DUMI: Jigawa za ta kasance jiha ta farko a Arewacin Najeriya da ta fara samar da wutar lantarki mai zaman kanta ta hanyar hasken rana.

Gwamnan jihar Jigawa ya kaddamar da tashar wutar lantarki mai amfani da hasken rana a Kafin Hausa.

Ana shirin bude tashoshin Hadejia, Kazaure, Gumel, Ringim da Dutse, a kokarin Gwamnan jihar na ganin an samar wa jihar Jigawa isasshiyar wutar lantarki domin inganta tattalin arzikin jihar.

Gwamnatin jihar Jigawa hade da kamfanin KEDCO, tare da hadin gwiwar kamfanin FEA s**a gina, za ta samar da megawatt 10 na wuta domin amfanin garuruwa fiye da 100 a fadin jihar Jigawa.

Idan aka kammala wannan aikin jihar Jigawa za ta kasance jiha ta farko a Arewacin Najeriya da ta fara samar da wutar lantarki mai zaman kanta ta hanyar hasken rana, abin da zai rage dogaro da wutar da ake samu daga babbar matattarar wuta ta (National Grid).

Daga Abba Sani Pantami ✍️

NAJERIYA TA MUTUM UKU CE - Inji Marigayi Malam Aminu KanoShashasha, Barawo, Mahaukaci *Shashasha - Bahaushe, kullum nasa...
29/08/2025

NAJERIYA TA MUTUM UKU CE - Inji Marigayi Malam Aminu Kano

Shashasha, Barawo, Mahaukaci

*Shashasha - Bahaushe, kullum nasa yake so ya mutu ya gaje shi, in zaka rataye dan uwansa shi zai baka igiya.

*Barawo - Bayerabe, in kaji yayi shuru to yana cutar ka, in yace a yi misaya to naka yafi.

*Mahaukaci - Inyamuri, yafi kowa morar kasar amma kuma baya iya zama a yankinsa, sai raina wasu amma kullum a raba kasa.

Marigayi Malam Aminu Kano. Allah ya gafarta masa.

Me za ku ce?

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Najeriya ta bawa matashiya Nafisa Abdullahi kyautar Naira dubu 200k, itace matashiyar da ta ci g...
28/08/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Najeriya ta bawa matashiya Nafisa Abdullahi kyautar Naira dubu 200k, itace matashiyar da ta ci gasar Turanci ta duniya.

Me za ku ce?

Nifa ko Dangote ne yazo neman aurena yace min ba zanyi aiki ko kasuwanci ba, sai dai ya kara gaba. Domin ba zan juri cew...
28/08/2025

Nifa ko Dangote ne yazo neman aurena yace min ba zanyi aiki ko kasuwanci ba, sai dai ya kara gaba. Domin ba zan juri cewa ya bani kudi zanyi guduwawa ko kyauta ga wayanda suke bukata ko ihisani ba daga wajena.

Note:

Wannan ra'ayi na ne.👂

Atiku ya ce zai tsaya takara a zaben 2027 don ceto 'yan NajeriyaTsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar yace ...
25/08/2025

Atiku ya ce zai tsaya takara a zaben 2027 don ceto 'yan Najeriya

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar yace zai tsaya takara a babban zaben Najeriya na 2027 domin fitar wa 'yan Najeriyxa kitse daga wuta.

Shin ya kuka ji da wannan?

'Yan majalisar wakilai 48 da Sanatoci 5 ne s**a yi zaman dumama kujera ba su ba da wata gudunmuwa a zauren majalisar dok...
25/08/2025

'Yan majalisar wakilai 48 da Sanatoci 5 ne s**a yi zaman dumama kujera ba su ba da wata gudunmuwa a zauren majalisar dokokin Nijeriya ba cikin shekara daya, in ji rahoton jaridar Daily Trust'Yan majalisar wakilai 48 da Sanatoci 5 ne s**a yi zaman dumama kujera ba su ba da wata gudunmuwa a zauren majalisar dokokin Nijeriya ba cikin shekara daya, in ji rahoton jaridar Daily Trust

Sarkin Musulmi ya aiyana ranar Litinin 25 ga watan Agusta ta zama 1 ga watan Rabi'ul Auwal 1447.Shugaban Kwamitin Bayar ...
24/08/2025

Sarkin Musulmi ya aiyana ranar Litinin 25 ga watan Agusta ta zama 1 ga watan Rabi'ul Auwal 1447.

Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addinin Musulunci a Majalisar Sarkin Musulmin kuma Wazirin Sakkwato Farfesa Sambo Wali Junaid ya fitar da bayanin cewa ba a samu ganin jinjirin watan Safar ba a ranar Asabar a Najeriya.

"Kwamitin Ganin Wata na Ƙasa da na Harkokin Addini a Majalisar Sarkin Musulmi ba su samu bayanin fitar sabon watan Rabi'ul Auwal ba a ranar Asabar 29 ga watan Safar.

“Dob haka Lahadi 24 ga watan Agusta za ta zama 30 ga watan Safar 1447," a cewarsa.

Ya ƙara da cewa Sarkin Musulmi ya aiyana Litinin a matsayin farkon watan Rabi'ul Auwal bayan amincewa da rahoton rashin ganin wata da aka bayar.

Aminiya✍️

Masu Garkuwa da Mutane Sun Yi Hatsari Bayan Karɓar Kuɗin Fansa a NasarawaRahotanni sun bayyana cewa wasu da ake zargi da...
18/08/2025

Masu Garkuwa da Mutane Sun Yi Hatsari Bayan Karɓar Kuɗin Fansa a Nasarawa

Rahotanni sun bayyana cewa wasu da ake zargi da masu garkuwa da mutane sun yi hatsari da motarsu kirar Peugeot 406 dauke da bindigogi, a daidai garin Angwan Mayo da ke kusa da Karamar Hukumar Kokona, jihar Nasarawa.

Lamarin ya faru ne a safiyar yau, lokacin da ake zargin sun karɓi kuɗin fansa daga hannun waɗanda s**a yi garkuwa da ’yan uwansu.

Sai dai abin mamaki, bayan hatsarin, ’yan ta’addan sun tsere, amma sun bar kuɗin da s**a karɓa da kuma bindigogin da suke ɗauke da su a cikin motar.

Farfesa Akyala Ishaku, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya yaba da gaggawar da jami’an tsaro s**a nuna. A cewarsa, sojoji da ’yan sanda sun isa wurin cikin hanzari tare da ɗaukar matakan da s**a dace.

~ Funtua Post News

Address

No 25. . B/Market
Kano
RARIYA

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA TODAY posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share