Dan'uwa Rano TV

Dan'uwa Rano TV Sahihiyar kafa da ta ke kawo zafafan labarai da shirye-shirye da suka shafi mulki, siyasa da zamantakewa.

Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya karɓi Alhaji Aminu Jahun daga NNPP zuwa Jam'iyyar APC,Wannan sanarwa na zuwa n...
21/09/2025

Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya karɓi Alhaji Aminu Jahun daga NNPP zuwa Jam'iyyar APC,

Wannan sanarwa na zuwa ne ta bakin mai taimakawa Gwamna Malam Umar Namadi Daddy Ringim, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Ɗan'uwa Rano TV
21/09/2025

Ya ku ka kalli muƙamin da Ganduje ya samu ?
21/09/2025

Ya ku ka kalli muƙamin da Ganduje ya samu ?

Jami’ar European American University ta buƙaci Dauda Kahutu Rarara da ragowar waɗanda aka ce an karrama da digirin girma...
21/09/2025

Jami’ar European American University ta buƙaci Dauda Kahutu Rarara da ragowar waɗanda aka ce an karrama da digirin girmamawa a Abuja su tuntuɓe ta domin ta duba can-cantarsu na samun matsayin.

A wata sanarwa da jami’ar ta fitar a shafinta na yanar gizo, ta bayyana cewa muddin waɗanda ta ambata sun can-canci samun digirin, za ta karrama su da shi a taron yaye dalibai da za ta gudanar a Najeriya cikin watan Nuwamban 2025.

Kazalika ta ce babu wani kuɗi da za a buƙaci wani ya biya saboda a kaucewa ayyukan ƴan damfara, kuma tuni ta fara ɗaukar mataki don gano waɗanda s**a shirya abinda ta kira da damfara.

Wannan ya biyo bayan sanarwar da jami'ar ta fitar na nesanta kanta da taron karrama mutanen da digirin girmamawa, wanda ya gudana a birnin Abuja a jiya Asabar.

Ɗan'uwa Rano TV
21/09/2025

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bayyana ranar 8 ga watan Oktoba, 2025 a matsayin ranar ƙarshe ga Jihohi, Kwamitoci ko ...
21/09/2025

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bayyana ranar 8 ga watan Oktoba, 2025 a matsayin ranar ƙarshe ga Jihohi, Kwamitoci ko Ma’aikatar Kula da Walwalar Alhazai, da kuma kamfanonin da aka ba lasisi, su kai kuɗaɗen aikin Hajji na 2026.

A wata sanarwa da Mataimakiyar Darakta ta Sashen Bayani da Hulda da Jama’a na NAHCON, Hajiya Fatima Usara, ta fitar a ranar Lahadi, hukumar ta ce an sanya wannan wa’adi ne bisa tsarin kalandar aiki da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta fitar.

Usara ta bayyana cewa hukumomin Saudiyya sun ayyana tsakanin 6 zuwa 23 ga watan Satumba, 2025, a matsayin lokacin ƙulla kwangila da biyan kuɗi na sansanoni, yayin da aka sa 23–24 ga watan Satumba, 2025 domin hidimomi masu muhimmanci irin su sufuri da masauki.

Sanarwar ta ce Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Usman, tare da kwamishinoni da Sakataren hukumar, Dr. Mustapha M. Ali, za su tafi Saudiyya a ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, 2025, domin kammala yarjejeniyar hidima da hukumomin da abin ya shafa.

Mai magana da yawun hukumar ta kara da cewa Ma’aikatar Hajji ta Saudiyya ta sa ranar 12 ga watan Oktoba, 2025 a matsayin rana ta ƙarshe ta yin rajista da tura bayanan mahajjata.

Dan'uwa Rano TV
21/09/2025

Shugaban Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA), Janar Buba Marwa mai ritaya, ya ce ta'ammali d...
21/09/2025

Shugaban Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA), Janar Buba Marwa mai ritaya, ya ce ta'ammali da miyagun ƙwayoyi alama ce kuma ginshiki ne na rashin tsaro a ƙasar nan.

Marwa ya bayyana haka ne da daddare a ranar Asabar a Abuja, yayin taron bikin cika shekaru 38 da kammala makarantar soja ta Nigeria Military School (NMS) aji na 1982.

Ya nuna cewa shan miyagun ƙwayoyi na ƙara ta’addanci, tayar da ƙayar baya da aikata miyagun laifuka, tare da raunana iyalai, ɓata baiwa da lalata tarbiyyar jama’a.

Shugaban NDLEA ya bayyana cewa, a cikin shekaru biyu da s**a gabata, hukumar ta ƙwace fiye da ƙwayoyin tramadol biliyan 1.8, robar maganin codeine miliyan 400, da kuma ƙwayoyin Captagon 500,000 da aka ɓoye a cikin injuna da ake zargin za a aika wa ƴan ta’adda.

Marwa ya jaddada cewa ladabi da hali nagari sune kariya mafi inganci kan muguwar ɗabi’ar shan miyagun ƙwayoyi, yana mai kira ga iyalai, makarantu, ƙungiyoyin addini, ƙungiyoyin agaji da kafafen yada labarai da su tashi tsaye wajen yaƙi da wannan matsala.

Dan'uwa Rano TV
21/09/2025

Shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya yi gargaɗi kan karya yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi ts...
21/09/2025

Shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya yi gargaɗi kan karya yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi tsakanin al’ummomi a jihar Katsina da shugabannin ƙungiyoyin ƴan bindiga.

Majiyarmu ta ruwaito cewa Sheikh Gumi, wanda ya shahara da kira ga tattaunawa a matsayin hanya mafi ɗorewa wajen kawo ƙarshen ta’addanci, ya sake jaddada matsayarsa bayan wasu tattaunawar sulhu da aka gudanar a wasu sassan jihar.

A ƴan makonnin nan, jami’an ƙananan hukumomi, sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma a wuraren da ƴan bindiga s**a addaba suna gudanar da tattaunawa da shahararrun shugabannin ƴan bindiga.

Da yake mayar da martani kan irin wannan shirin sulhu a ƙaramar hukumar Sabuwa, Sheikh Gumi ya yi kira ga jami’an tsaro da shugabannin al’umma da kada su lalata wannan yarjejeniya.

Ya buƙaci gwamnati ta yi mu’amala da ƙungiyoyin makiyaya masu ɗauke da makamai a Arewa da irin tsarin da aka yi amfani da shi wajen mayar da tsoffin ƴan tawayen yankin Neja Delta cikin al’umma.

Dan'uwa Rano TV
21/09/2025

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya nuna goyon bayansa ga korar Abdulmum...
21/09/2025

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya nuna goyon bayansa ga korar Abdulmumin Jibrin daga jam’iyyar, tare da yabawa reshen Kano na jam’iyyar bisa wannan mataki.

DAILY NIGERIAN ta tuna cewa a wata tattaunawa da aka yi da shi kwanan nan a wani gidan jarida na yanar gizo mai suna DCL, Jibrin ya bayyana aniyarsa ta barin jam’iyyar NNPP.

Daga baya, a ranar 6 ga watan Satumba, shugaban NNPP na Kano, Hashimu Dungurawa, ya sanar da korar Jibrin a wani taron manema labarai a Kano, yana mai zargin sa da yawan s**ar jam’iyya da shugabanninta a kafafen yaɗa labarai.

Da yake jawabi a ranar Alhamis lokacin da ya karɓi ziyarar goyon baya daga dattawa da masu riƙe da sarautun gargajiya daga mazaɓar Ƙiru/Bebeji a gidansa da ke Kano, Kwankwaso ya ce korar Jibrin ta zo a kan gaɓa, kuma mataki ne da ya dace.

Jigon na NNPP ya ƙara da bayyana cewa jam’iyyar za ta fito da ɗan takara mafi ƙarfi domin maye gurbin Jibrin a zaɓen 2027.

Dan'uwa Rano TV
21/09/2025

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa Consultative Forum (ACF) reshen Jihar Kano ta rantsar da sabbin shugabannin zartarwa da aka za...
21/09/2025

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa Consultative Forum (ACF) reshen Jihar Kano ta rantsar da sabbin shugabannin zartarwa da aka zaɓa domin jagorantar harkokin ƙungiyar na tsawon shekaru uku masu zuwa.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa an gudanar da rantsuwar ne a lokacin taron shekara-shekara na ƙungiyar (AGM) a Kano, inda manyan masu ruwa da tsaki s**a halarta.

Cikin waɗanda aka rantsar akwai: Dr. Goni Faruk-Umar da aka sake zaɓa a matsayin Shugaba, Hajiya A’ishatu Maijama’a a matsayin Mataimakiyar Shugaba, Alhaji Abubakar Idris-Ahmad Mataimakin Shugaba da kuma Dr. Aminu Usman-Jibrin a matsayin Sakataren Ƙungiya.

NAN ta kuma ruwaito cewa ƙungiyar ta rantsar da mambobin kwamitin amintattu da sauran shuwagabanni.

Dan'uwa Rano TV
21/09/2025

"Ina cikin mutane 89 da muka kwashe sama da kwanaki 120 muna ƙoƙarin kafa jam’iyyar APC.Saboda haka, tutar APC ba za ta ...
21/09/2025

"Ina cikin mutane 89 da muka kwashe sama da kwanaki 120 muna ƙoƙarin kafa jam’iyyar APC.

Saboda haka, tutar APC ba za ta cika ba sai da sunana, Kawu Sumaila.

Shekara goma muka yi muna yaƙi da gwamnatin PDP, kunga kuwa mu muka kawo adawo ta gaskiya.”

Ɗan’uwa Rano TV
21/09/2025

Rarara ya bayyana wannan matsayi nasa ne ta bakin babban hadiminsa Rabi'u Garba Gaya, wanda ya wallafa a shafinsa na Fac...
21/09/2025

Rarara ya bayyana wannan matsayi nasa ne ta bakin babban hadiminsa Rabi'u Garba Gaya, wanda ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce Kperogi ya ɓata sunan Jami'ar da kuma shi (Dr.) Dauda Kahutu Rarara

Me za ku ce a kan wannan sabuwar dambarwa?

Dan'uwa Rano TV
21/09/2025

Jaridar Daily Nigerian ta Rawaito cewa: A ranar Asabar, 20 ga Satumba, 2025, aka gudanar da wani bikin karramawa a Nicon...
21/09/2025

Jaridar Daily Nigerian ta Rawaito cewa: A ranar Asabar, 20 ga Satumba, 2025, aka gudanar da wani bikin karramawa a Nicon Luxury Hotel, dake birnin tarayya Abuja inda aka ce an bai wa fitaccen mawaƙin siyasarnan Dauda Kahutu Rarara da wasu mutum uku digirin girmamawa daga European-American University (EAU).

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda, da wasu jami’ai sun halarci taron.

Sai dai jami’an EAU sun fitar da sanarwa a shafinsu na yanar gizo inda s**a ce ba su da hannu a wannan taro, kuma ba su taɓa bai wa Rarara ko sauran mutanen da aka lissafo digiri a wannan makaranta ba.

Sun bayyana cewa waɗanda s**a shirya bikin sun yi amfani da sunan jami’ar ne cikin yaudara, ba tare da izini ko sahalewar su ba.

Sun kuma nesanta kansu daga wasu mutanen da aka ce sun wakilci jami’ar a Najeriya, ciki har da Musari Audu Isyaku, wanda ya ce shi ne wakilin Arewa — jami’ar ta ce ba shi da wata alaƙa da su.

Idris Aliyu, wanda aka gabatar a matsayin mamba na "Governing Council" — jami’ar ta bayyana cewa ba su da irin wannan kwamitin, kuma sun soke duk wata matsayarsa da ta danganci jami’ar saboda wannan zamba.

Sun kuma sake tunatarwa cewa tsohuwar shugabar jami’ar, Dr. Josephine Egbuta, wacce aka kora tun da dadewa, ba ta da wata alaka da jami’ar.

A ƙarshe, jami’ar ta ce tana shirin shigar da ƙara a Najeriya domin hukunta masu shirya wannan bikin na bogi da kuma hana ci gaba da buga takardun bogi da sunanta.

Ɗan'uwa Rano TV
21/09/2025

Ina matasan ƙasarnan ya ku ka kalli batun na ƊanBello ?
20/09/2025

Ina matasan ƙasarnan ya ku ka kalli batun na ƊanBello ?

Address

Office N04 Kademi Plaza, Sabuwar Gandu Junction By Gidan Maza
Kano

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00

Telephone

+2348085199917

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dan'uwa Rano TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dan'uwa Rano TV:

Share