15/08/2026
Muslim-Muslim Ticket Ba Shi Ne Amsa Ga Talakawa
Amfani da batun Muslim-Muslim wajen neman kuri’a ko kare wannan gwamnati ba zai maye gurbin abin da gwamnati ta cimma ba. Idan bayan shekaru uku har yanzu ana komawa kan wannan batu maimakon a nuna nasarori, to ya dace ’yan ƙasa su tambaya:
1. Me gwamnati ta yi don inganta rayuwar talakawa?
2. Me ta yi don inganta tattalin arziki da ci gaban ƙasar?
3. Me ta yi wajen inganta ilimi da kiwon lafiya?
A ƙarshe, ba addini ko kabila ne ya k**ata su zama ma’aunin zaɓe ba. Ayyuka, gaskiya, adalci da yadda rayuwar talakawa ta inganta su ne abin da ya k**ata ’yan ƙasa su duba kafin su yanke hukuncin wanda za su zaɓa.
Kuma shawarata ga Sheikh Yahaya Jingir shine : Kai uba ne, malami ne, kuma jagora ne. Ya k**ata ka san cewa duk abin da kake faɗa ko yi kana da alhakin sa a gaban Allah. Ka ji tsoron Allah, ka faɗi gaskiya, ka tsaya kan adalci, domin kada abin da ake ganin nasara a duniya ya zama tarko a Lahira.
Allah Ya shiryar da mu zuwa gaskiya, Ya ba ƙasarmu adalci da shugabanni nagari. 🤲🇳🇬