19/04/2026
Rikicin PDP Ya Tilasta Shekarau Komawa APC – Me Ke Tafe?
Tsohon gwamnan Kano kuma tsohon Sanatan Kano ta Tsakiya, Ibrahim Shekarau, ya sanar da komawarsa tare da magoya bayansa zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), bayan ficewa daga People's Democratic Party (PDP).
Wannan mataki ya biyo bayan wani muhimmin zama na majalisar Shura da aka gudanar a gidansa da ke Mundubawa, inda aka yi zurfin nazari kan makomar siyasarsu. Rahotanni sun nuna cewa rikice-rikicen cikin gida da s**a dabaibaye PDP ne s**a tilasta daukar wannan matsaya, yayin da aka bayyana cewa babu wata mafita a halin yanzu.
👉 Wannan sauyi na iya sauya akalar siyasar Kano da ma Arewa gaba ɗaya.
💬 Tambaya: Wannan dawowa APC zai ƙara ƙarfi ne ko kuma zai haifar da sabon rikici a siyasa?