DMS HAUSA 24

DMS HAUSA 24 D M S HAUSA 24 Jarida ce Mai yada
shirye-shirye a kafar Facebook da YouTube. a halin yanzu cikin Harshen HAUSA, daga Kano.

Jarida ce da ta kudiri aniyar kawo mu ku sahihan Labarai daga ko ina cikin duniya.

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi gudanar da bincike kan kisan fararen hula a NajeriyaShugaban hukumar kare haƙƙin bil’ada...
13/05/2026

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi gudanar da bincike kan kisan fararen hula a Najeriya

Shugaban hukumar kare haƙƙin bil’adama na Majalisar Ɗinkin Duniya Volker Turk, ya buƙaci a gudanar da bincike na musamman game da kisan fararen hular da aka samu a Arewacin Najeriya, bayan hare-haren da dakarun ƙasar da na Chadi s**a kai kan ƴan ta’adda.

Rahotanni sun nuna cewar masinta da dama ne s**a rasa rayukansu a harin da sojojin Chadi sun kai a yankin Tafkin Chadi, wanɗanda mahukunta N'Djamena s**a zarga da taimakawa ƴan ta’addan Boko Haram.

A cikin sanarwar da Volker Turk ya fitar, ya kuma ce akwai buƙatar a gudanar da bincike na musamman, kan yadda aka kashe fararen hula a harin da jirgin saman sojin Najeriya ya kai kasuwar Tumfa da ke yankin ƙaramar hukumar Zurmi a jihar Zamfara, wanda rahotanni s**a ce sama da mutum ɗari s**a mutu.

Kafin wannan kira na Majalisar Ɗinkin Duniya, anji dama Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adam ta Amnesty International na Allah wadai da wannan hari.

RFI HAUSA

An kirkiro jihohin Daura, Gobir Da Katsina Da Wasu Guda 8 A Jamhoriyar NigerA yanzu, adadin jihohi a Jamhoriyar Nijar ya...
12/05/2026

An kirkiro jihohin Daura, Gobir Da Katsina Da Wasu Guda 8 A Jamhoriyar Niger

A yanzu, adadin jihohi a Jamhoriyar Nijar ya tashi Daga 8 zuwa 19 kamar yadda wani darakta da ya wakilci ministan cikin gida Janar Mohamed Toumba ya sanar a gaban Majalisar Shawara ta ƙasar a wannan talata.

Daftarin da ke sanar da ƙirƙiro jihohin da ya gabatar wa majalisar, na nuni cewa aƙalla kowace daga cikin jihohin ƙasar 8 an raba ta zuwa gida biyu, wasu kuwa uku yayin da aka ƙirƙiri sauran ta hanyar cire ƙananan hukumomi daga wasu jihohi tare da dunƙule su a matsayin jiha ɗaya.

A cewar minista Toumba, jihar Maradi ta asali, ƙarƙashin wannan tsari, an raba ta zuwa uku don samar da jihohin Katsina, Gobir da kuma Tazar, kamar dai yadda aka raba jihar Damagaram/Zinder gida uku don samar da jihohin Daura, Damagaram da kuma Damergou.

Wani abu sabo game da lamarin shi ne canza wa illahirin jihohin suna in ban da birnin Yamai da zai ci gaba da riƙe sunansa a matsayin fadar gwamnatin ƙasar

Madogara: RFI HAUSA

Nuhu Ribadu na Nan daram kan muƙaminsa -Fadar Shugaban KasaFadar shugaban Najeriya ta fitar da wata sanarwar cewa, Nuhu ...
12/05/2026

Nuhu Ribadu na Nan daram kan muƙaminsa -Fadar Shugaban Kasa

Fadar shugaban Najeriya ta fitar da wata sanarwar cewa, Nuhu Ribadu yana nan a matsayinsa na babban mashawarcin tsaron ƙasar.

Wata majiya daga fadar shugabancin ƙasar da ta nemi a sakaya sunanta, ta shaidawa jaridar PRNigeria cewa, nada Adeyinka Famadewa da Shugaba Tinubu ya yi a matsayin mashawarcin tsaron kasar na musamman a cikin gida, ba yana nufin an cire Ribadu daga muƙaminsa bane.

Fadar Shugaban ƙasar ta tabbatar da cewa jita-jitar maye gurbin Ribadu ƙarya ce, tare da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa na haɗin gwiwar hukumomin tsaro da sarrafa bayanan sirri.

Majiyar ta ce, sabon ofishin Adeyinka an ƙirƙire shi ne don ya taimaka wajen ƙarfafa tsaron cikin gida, wanda ya haɗa da harkokin shige da fice, da tsaron hanyoyin sufuri.

Majiyar ta ce, Famadewa zai yi aiki ne ƙarƙashin Ribadu don inganta tsarin tsaron ƙasar, ba tare da katsalandan a ayyukan da kundin tsarin mulki ya bai wa ofishin mashawarcin tsaron ba.

Adeyinka Famadewa tsohon Manjo Janar ne wanda ya ƙware a fannin bayanan sirri da dabarun yaƙi da ta'addanci, kuma ya taɓa zama babban jami'i a ofishin mai ba wa shugaban ƙasa shawara tsakanin shekarar 2015 zuwa 2021.

Wannan naɗin na Famadewa wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin Tinubu wajen sake fasalin tsaro don fuskantar matsalolin garkuwa da mutane, ta'addanci, da sauran barazanar tsaro da ke addabar Najeriya.

RFI HAUSA

Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan KanoAn rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsa...
05/05/2026

Murtala Garo Ya Sha Rantsuwar K**a Aiki A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano

An rantsar da Alhaji Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakin gwamnan Kano

Gwamnan Jihar ta Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ne ya jagoranci rantsar da shi yau talata a fadar gwamnatin Jihar.

An gudanar da bikin ne a dakin taro na Ante Chamber da ke cikin Gidan Gwamnati, inda manyan jami’an gwamnati, jiga-jigan jam’iyya, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar s**a halarta.

Bayan da Babbar Alkalin Jihar, Mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jagoranci rantsar da shi, gwamnan ya bukaci sabon mataimakin gwamnan da ya mutunta kundin tsarin mulki tare da gudanar da ayyukansa cikin gaskiya, jajircewa da kuma rikon amana.

Gwamna Yusuf ya jaddada muhimmancin hadin kai da aiki tare a harkokin mulki, inda ya bayyana cewa nasarar gwamnatinsa na dogara ne da kokarin hadin gwiwa da kuma jajircewar hidimtawa al’ummar Jihar Kano.

A nasa jawabin, tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana kwarin gwiwa ga sabon mataimakin gwamnan, yana mai cewa zai bayar da gudunmawarsa wajen bunkasa jihar.

A jawabin karbarsa, Alhaji Murtala Sule Garo ya gode wa gwamnan da al’ummar Jihar Kano bisa amincewar da s**a yi da shi, tare da yin alkawarin yin aiki tukuru domin tallafawa manufofin ci gaban gwamnati.

Ya kuma tabbatar da cewa zai yi amfani da kwarewarsa wajen tabbatar da ingantacciyar hidima ga jama’a, tare da inganta zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a fadin jihar.

I've just reached 20K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏...
07/04/2026

I've just reached 20K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗🎉

03/04/2026
Sabon Jagoran Addinin Iran Ya Kuɓuta daga Hare-Hare Sau BiyuWani ɗan majalisar ƙasar Iran ya bayyana cewa sabon jagoran ...
14/03/2026

Sabon Jagoran Addinin Iran Ya Kuɓuta daga Hare-Hare Sau Biyu

Wani ɗan majalisar ƙasar Iran ya bayyana cewa sabon jagoran addinin ƙasar, Mojtaba Khamenei, ya kuɓuta daga hare-hare biyu da aka kai masa.

A cewar kamfanin dillancin labaran gwamnatin Iran, ɗan majalisar da ke wakiltar Jahrom, Mohammad Reza Rezaei Kochi, ya ce Mojtaba Khamenei yana tare da Ali Khamenei lokacin da aka kai hari kan gidan jagoran addinin, amma ya tsira daga yunƙurin kashe shi.

Kochi ya ƙara da cewa an sake kai wani hari a wani asibiti a lokacin da sabon jagoran addinin ke wurin, amma Amurka da Isra’ila ba su cimma burinsu ba.

Sai dai ɗan majalisar bai bayyana sunan asibitin ko takamaiman wurin da aka kai harin ba.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana a wata hira da tashar Fox News cewa sabon jagoran Iran ya samu rauni a ranar farko ta hare-haren da Amurka da Isra’ila s**a kai.

Trump ya ce yana kyautata zaton cewa Mojtaba Khamenei na raye, amma an ji masa rauni.

A jiya kuma aka wallafa saƙon farko daga sabon jagoran addinin, inda ya ce Iran za ta ɗauki fansar mutanenta da aka kashe a hare-haren da Isra’ila da Amurka s**a kai wa ƙasar.

BBC Hausa

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DMS HAUSA 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share