28/01/2026
Salisu Yahaya Hotoro : Ayyukan Abba Gida-Gida na Ci Gaba Har Yanzu Suna Gudana a Kano
Babban Mai Ba Gwamnan Jihar Kano Shawara kan Kafofin Sadarwa, Salisu Yahaya Hotoro, ya ce duk da adawa da s**a fuskanta a shekarar 2016, a yau babu wanda zai fito ya musanta cewa manyan ayyukan ci gaba da Kwankwasiyya ta shahara da su wannan Gwamnatin ta Abba bata ci gaba da gudanar da su ba a wannan jihar.
Hotoro ya bayyana cewa a wancan lokaci, sa muke adawa muna zargin gwamnati da sauka daga turbar Kwankwasiyya ne, musamman kan shirye-shiryen Auren Zawarawa, tura matasa kasashen waje domin karatu, gina ajujuwa a makarantu, ci gaba da aikin titin 5km, ciyar da dalibai, koyar da sana’o’i tare da basu jari, saka fitulun kan tituna, da baiwa mata da matasa jari domin dogaro da kai, da kuma sauran ayyukan raya kasa.
Ya ce a yanzu kuwa, “Alhamdulillah, duk karyar mutum ko wanene shi, bai isa ya fito ya ce ba a aiwatar da wadannan muhimman ayyuka ba,” in ji Hotoro.
Sai dai ya zargi wasu da cewa sun kasa fito wa fili su bayyana hujjojinsu ga al’umma, inda a cewarsa s**a dunkule wasu abubuwa da ke faruwa a boye s**a sanya musu suna “Cin Amana.”
“Tun da ba za su iya fitowa su gayawa duniya gaskiyar abin da ke faruwa ba, to mu za mu bayyana wa duniya, domin al’umma su zama alkalai tsakanin mu da su, Insha Allah,” in ji Salisu Yahaya Hotoro.
Ya jaddada cewa gwamnatin Kano karkashin Abba Kabir Yusuf na ci gaba da aiwatar da manufofin jin kai da raya kasa domin amfanin al’umma baki ɗaya.