AAG Hausa

AAG Hausa Barka da zuwa shafin (AAG Hausa) Kuci gaba da bibiyar wannan shafi domin samun labarai da dumi-duminsu dasauran al'amuran yau da kullum. 07066719596

16/08/2026

Kalli Yanda aka yiwa wasu Gwamnonin Arewa Ihu a Jihar OSUN akan hanyarsu ta ficewa daga Jihar.

14/08/2026

An gano wani asibiti na bakin hanya da ake kula da marassa lafiya a cikin kwata a jahar Legas.

Vanguard News.

’Yan Najeriya na ci gaba da zama a gidajen yarin SaudiyyaJakadan Najeriya a Saudiyya, Ambasada Gambo, yace anci gaba da ...
07/08/2026

’Yan Najeriya na ci gaba da zama a gidajen yarin Saudiyya

Jakadan Najeriya a Saudiyya, Ambasada Gambo, yace anci gaba da tsare wasu ’yan Najeriya a gidajen yarin Saudiyya bayan kammala hukuncinsu, saboda rashin biyan tara.

NiDCOM ta ce za ta tallafa wajen ganin an magance matsalar tare da taimaka wa ’yan Najeriya da abin ya shafa.

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi taron karɓar masu sauya sheƙa daga APC zuwa NDC Kwankwasiyya A KanoJagoran tafiyar Kwa...
02/08/2026

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi taron karɓar masu sauya sheƙa daga APC zuwa NDC Kwankwasiyya A Kano

Jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya karɓi wasu masu sauya sheƙa daga jam'iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Madobi da ke Jihar Kano, waɗanda s**a sanar da komawarsu tafiyar NDC Kwankwasiyya.

An karɓi tawagar ne a gidan Sanata Kwankwaso da ke kan titin Miller a birnin Kano, inda s**a bayyana mubaya'arsu tare da alƙawarin ci gaba da mara wa tafiyar cikakken baya.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNAllah Ya yi wa Kosan Waƙa rasuwa bayan fama da rashin lafiya.Muna roƙon Allah Ya jiƙan...
02/08/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah Ya yi wa Kosan Waƙa rasuwa bayan fama da rashin lafiya.

Muna roƙon Allah Ya jiƙansa da rahama, Ya yafe masa kura-kuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa.

SHUGABAN ƘUNGIYAR MATASAN SARARIN GEZAWA YAYI KIRA GA MATASA DASU RUNGUMI ZAMAN LAFIYA.‎Shugaban Ƙungiyar Matasan Sarari...
01/08/2026

SHUGABAN ƘUNGIYAR MATASAN SARARIN GEZAWA YAYI KIRA GA MATASA DASU RUNGUMI ZAMAN LAFIYA.

Shugaban Ƙungiyar Matasan Sararin Gezawa a karamar hukumar Gezawa Comred Abubakar Shu'aibu(P.R.O) yayi kira ga matasa dasu rungumi zaman lafiya.

‎P.R.O yayi wannan kirane Yayin wani zaman tattaunawa da kungiyar ta gudanar kan yadda za'a bullo da dabaru na wayarwa da matasa Kai,

‎Yace Yana dakyau Matasa su zauna lafiya sukuma mai da hankalinsu bangaren neman na kansu dakuma gujewa fitintunun zamani.

INEC Ta Wallafa Takardun Shaidar Karatu da Bayanai na Peter Obi da Sanata Rabiu Musa KwankwasoHukumar Zaɓe Mai Zaman Kan...
01/08/2026

INEC Ta Wallafa Takardun Shaidar Karatu da Bayanai na Peter Obi da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta wallafa takardun shaidar karatu da bayanan sirri na Mista Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC a zaɓen shekarar 2027, tare da na abokin takararsa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Wallafa takardun na daga cikin tanadin Dokar Zaɓe, wadda ta wajabta wa INEC nuna takardun shaidar karatu da bayanan sirri da 'yan takara s**a gabatar domin bai wa jama'a damar dubawa, tare da ba da damar shigar da ƙorafi ko ƙalubale bisa tanadin doka idan akwai dalili.

~ATP English

Jarumin Kannywood Adam A. Zango ya rabu da matarsa Maimuna Pretty.
31/07/2026

Jarumin Kannywood Adam A. Zango ya rabu da matarsa Maimuna Pretty.

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya gana, da Sanata Rufai Sani Hanga.~DC Hausa
29/07/2026

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya gana, da Sanata Rufai Sani Hanga.

~DC Hausa

JAMI'AN TSARO SUN SAMU NASARAR K**A MATAR DA AKE ZARGI DA SACE JARIRI A ASIBITIN GEZAWA.​Jami’an tsaro a Jihar Kano sun ...
29/07/2026

JAMI'AN TSARO SUN SAMU NASARAR K**A MATAR DA AKE ZARGI DA SACE JARIRI A ASIBITIN GEZAWA.

Jami’an tsaro a Jihar Kano sun samu nasarar damƙe wata mata da ake zargi da satar wani sabon jariri daga Asibitin Gezawa, mako guda bayan faruwar lamarin.

​Yadda Lamarin Ya Faru
​Bayanai sun nuna cewa wadda ake zargin ta shiga sashen da ake kula da mata da ma'aikata bayan haihuwa ne a makon da ya gabata, inda ta yi amfani da damar rashin tsaro ko ɗauke hankalin ma'aikata ta gudu da jinjirin wanda aka haifa ba a daɗe da hakan ba.

​Satar jaririn ta jefa iyayen yaron da sauran al'umma cikin tsananin damuwa da alhini, wanda hakan ya sa hukumar 'yan sanda tare da sauran jami'an tsaro tsaurara bincike da gudanar da binciken diddigi a fadin yankin.

​Kama Matar Da Matsayin Jaririn A Yanzu
​Bayan gudanar da gagarumin bincike na sirri da bin sahu, jami'an tsaro sun sa kafa a inda wadda ake zargin take boye, wanda hakan ya kai ga k**a ta tare da ceto jaririn yana da rai lafiya.

​A yanzu haka, jaririn yana ƙarƙashin kulawar hukumar 'yan sanda domin tabbatar da tsaro da lafiyarsa yayin da ake kammala hanyoyin mika shi ga iyayensa na ainihi.

​Jawabin Hukuma:
"Nasarar k**a wannan mata shaida ce ta sadaukarwar jami’anmu wajen kare rayukan jama’a. Muna tabbatar wa al'umma cewa za a gurfanar da wadda ake zargi gaban shari'a domin ta fuskanci hukunci bayan kammala bincike."

Nan gaba kaɗan, za mu kawo muku cikakken rahoto da ƙarin bayani kai tsaye daga Hukumar 'Yan Sanda ta Jihar Kano dangane da wannan al'amari.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AAG Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share