AAG Hausa

AAG Hausa Barka da zuwa shafin (AAG Hausa) Kuci gaba da bibiyar wannan shafi domin samun labarai da dumi-duminsu dasauran al'amuran yau da kullum.

Gwamnatin Jihar Edo a Najeriya ta dakatar da ayyukan ƙungiyoyin sufuri na NURTW da kuma Retean bayan da aka gano cewa ma...
29/08/2025

Gwamnatin Jihar Edo a Najeriya ta dakatar da ayyukan ƙungiyoyin sufuri na NURTW da kuma Retean bayan da aka gano cewa magoya bayansu na karɓar haraji daga hannun masu ababen hawa.

KOFAR NA'ISA ISA  kenan dake cikin birnin kano
29/08/2025

KOFAR NA'ISA ISA kenan dake cikin birnin kano

SIYASA ME TSAFTA: Yadda Tsoffin Gwamnonin Jihar Jigawa Tare Da Gwamnan Jihar, Umar Nmadi, S**a Haɗu A Wajen Bikin Cikar ...
27/08/2025

SIYASA ME TSAFTA: Yadda Tsoffin Gwamnonin Jihar Jigawa Tare Da Gwamnan Jihar, Umar Nmadi, S**a Haɗu A Wajen Bikin Cikar Jihar Shekaru 34 Da Kirƙirar Jihar Jigawa.

Jirgin Kasan Abuja zuwa Kaduna ya yi hatsari Wani jirgin kasa da ke tafiya daga Abuja zuwa Kaduna ya yi hatsari a safiya...
26/08/2025

Jirgin Kasan Abuja zuwa Kaduna ya yi hatsari

Wani jirgin kasa da ke tafiya daga Abuja zuwa Kaduna ya yi hatsari a safiyar Talata, inda wasu daga cikin taragon jirgin s**a kife, lamarin da ya jefa fasinjoji cikin tashin hankali da firgici.

Rahotanni sun bayyana cewa hatsarin ya faru ne da misalin karfe 11 na safe, jim kaɗan bayan jirgin ya bar Abuja. Shaidu sun ce fasinjoji sun rika yin gudun ceton ransu cikin rudani da firgici.

A halin yanzu ba a tabbatar da adadin waɗanda s**a jikkata ba ko kuma mutanen da s**a rasa rayukansu. Sai dai jami’an tsaro sun isa wajen domin taimakawa wajen ceto.

Unguwar Hotoro bayan Police Station a Kano.Hotuna daga Aliyu Dalhat abubakar.
16/07/2025

Unguwar Hotoro bayan Police Station a Kano.

Hotuna daga Aliyu Dalhat abubakar.

Shugaban ƙasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya kai wata ziyarar aiki na yini guda ƙasar Benin da yammacin jiya Talata, ...
16/07/2025

Shugaban ƙasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya kai wata ziyarar aiki na yini guda ƙasar Benin da yammacin jiya Talata, da nufin ƙarfafa dangantaka da farfaɗo da haɗin gwiwa tsakanin Benin da Senegal.

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da bincike kan mutuwar wasu ɗalibai biyu a makarantar sakandare ta kwana da ke Bichi, b...
16/07/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da bincike kan mutuwar wasu ɗalibai biyu a makarantar sakandare ta kwana da ke Bichi, bayan da aka zargi wasu abokan karatun daliban da kai musu hari.

Kwamishinan Ilimi na jihar, Dr. Ali Makoda, ne ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin, domin gano gaskiyar abin da ya faru da kuma tabbatar da adalci ga iyalan waɗanda abin ya shafa.

Ɗaliban da s**a rasu su ne Hamza Tofawa da Umar Dungurawa, kuma rahotanni na nuna cewa wasu manyan ɗalibai ne s**a kai musu hari da wani ƙarfe mai suna “Gwale-Gwale”.

Sanarwar da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi, Balarabe Kiru, ya fitar ta ce an fara bincike domin gano hakikanin musabbabin rasuwar ɗaliban.

Babban Sakataren Ma’aikatar, Bashir Muhammad, wanda ya wakilci kwamishinan yayin da ya kai ziyarar gani da ido zuwa makarantar, yace gwamnati za ta tabbatar da gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci.

“Kar ku ɗauki doka a hannunku. Idan wani abu ya faru, ku sanar da malamai ko shugabannin makaranta domin daukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Dan Majalisar Tarayya ya Maka Wasu Matasan Mazabarsa A Gaban Kotu A Kano Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Bagw...
11/06/2025

Dan Majalisar Tarayya ya Maka Wasu Matasan Mazabarsa A Gaban Kotu A Kano

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Bagwai da Shanono a Jihar Kano, Hon. Yusuf Ahmad Badau, ya maka wasu matasa a gaban kotu, wadanda ke karkashin kungiyar Bagwai/Shanono Together for Progress, bisa zargin kafa kungiya ba bisa ka’ida ba da kuma bata masa suna.

Wannan mataki na zuwa ne bayan da kungiyar ta shigar da koke a kansa gaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (ICPC) da kuma kwamitin ladabtarwa da sauraron korafe-korafe na Majalisar Tarayya.

Kungiyar ta bayyana a cikin korafinta cewa akwai bukatar a binciki ayyukan mazabar da s**a kai kimanin Naira biliyan daya, inda s**a zargi dan majalisar da karkatar da kudade da kuma kin aiwatar da ayyukan yadda ya kamata. Ayyukan da ake magana a kansu sun hada da gyaran hanyoyi, tallafin matasa, da kuma samar da kayayyakin more rayuwa.

Sai dai yayin da AREWA UPDATE ta tuntubi lauyan dan majalisar, Barrister M. M. Sani, ya bayyana cewa sun dauki matakin gurfanar da matasan ne a kotu bisa hujjojin cewa kungiyar ba ta da rajista da kuma cewa ta ke bata sunan dan majalisar ta kafafen yada labarai da kuma gaban hukumomi.

Ya ce, “Aikin dan majalisa shi ne wakilci da kokarin samar da ayyuka ga al’ummarsa, amma ba shi ne ke aiwatar da ayyukan kai tsaye ba. Abin mamaki ne yadda s**a cakuda ayyukan da ba su da alaka da dan majalisar domin kawai su gina zargi a kansa.”

Barrister Sani ya kara da cewa matakin da kungiyar ta dauka yana da illa ga mutunci da martabar dan majalisar a idon jama’a da hukumomi, wanda hakan ya tilasta musu daukar matakin shari’a domin kare martabarsa da mutuncinsa a bainar jama’a.

Yanzu haka dai ana jiran yadda kotu za ta gudanar da shari’ar, yayin da al’umma a yankin Bagwai da Shanono ke ci gaba da sa ido kan cigaban da rikicin siyasar ya dauka.

KOTU TA UMARCI GWAMNATIN KANO TA BIYA TIAMIN HOSPITAL DIYYAR NAIRA BILIYAN 2.6Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke hukuncin ...
21/05/2025

KOTU TA UMARCI GWAMNATIN KANO TA BIYA TIAMIN HOSPITAL DIYYAR NAIRA BILIYAN 2.6

Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke hukuncin cewa matakin da gwamnatin jihar ta dauka na kwace fili da rushe ginin asibitin zamani da kamfanin Tiamin Multi Services Global Limited ke ginawa a unguwar Gyadi-Gyadi, karamar hukumar Tarauni, ya sabawa doka.

Kotun ta umarci gwamnatin jihar da ta biya kamfanin diyya da ta kai Naira biliyan 2.635 sakamakon wannan take hakki.

A cewar bayanan kotu, gwamnatin da ta gabata a karkashin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ce ta kwace filin tare da rushe gine-ginen da aka kusa kammalawa a wancan lokaci.

Kamfanin Tiamin ya shigar da kara tun a watan Oktoba na shekarar 2019, yana neman diyya kan abin da ya bayyana a matsayin take hakkin mallaka da rushe asibitinsa ba tare da bin ka’idojin doka ba.

A hukuncin da Mai shari’a Ibrahim Karaye ya yanke a ranar Laraba, kotun ta bayyana cewa kwace filin da gwamnatin Kano ta yi a ranar 3 ga Satumba, 2021, ta hanyar wasika daga Hukumar Kula da Filaye ta Jihar Kano, ya saba da kundin tsarin mulki da kuma dokar mallakar fili ta ƙasa (Land Use Act).

Mai shari’a Karaye ya jaddada cewa gwamnatin jihar ta dauki matakin ne ba tare da bai wa kamfanin damar kare kansa ba, lamarin da ya sa kwace filin da kuma rushe ginin s**a zama babu inganci a idon doka.

Kotun ta kuma soki gwamnatin jihar bisa matakin rushe ginin yayin da karar ke gaban kotu, tana mai bayyana hakan a matsayin saba wa doka da kuma abin kyama.

Kasashen Nijar da Mali sun sanya hannu kan wasu muhimman yarjejeniyoyi da s**a shafi samar da man fetur, musamman domin ...
17/05/2025

Kasashen Nijar da Mali sun sanya hannu kan wasu muhimman yarjejeniyoyi da s**a shafi samar da man fetur, musamman domin yankunan arewacin Mali.

Wannan yarjejeniya na daga cikin wata sabuwar dabarar haɗin gwiwa da manyan shugabannin ƙasashen biyu s**a ƙaddamar, domin tabbatar da wadataccen makamashi da zaman lafiya a yankin Sahel.

Daga yanzu, Mali za ta daina dogaro da man fetur daga Aljeriya, inda za ta rika tsayan mai kai tsaye daga Nijar.

Sabuwar motar Mawaki Dauda Kahutu Rarara, mai suna Changan UNI-V wadda kamfanin Changan Auto na China ke kerawa. A ganin...
17/05/2025

Sabuwar motar Mawaki Dauda Kahutu Rarara, mai suna Changan UNI-V wadda kamfanin Changan Auto na China ke kerawa.

A ganinku farashinta zai iya kaiwa Nawa.

Wike ya ce ba zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 ba, zai Marawa Tinubu baya Nyesom Wike, Ministan Babban Birnin Tara...
17/05/2025

Wike ya ce ba zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 ba, zai Marawa Tinubu baya

Nyesom Wike, Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, ya bayyana cewa ba zai tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2027 ba domin yin gogayya da Shugaba Bola Tinubu.

A wata hira da ya yi da BBC Pidgin, Wike ya ce babu wani ɗan siyasa da zai iya kalubalantar Tinubu a zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Akwai muhawara a cikin jam’iyyar adawa ta PDP kan batun karkatar da tikitin shugaban kasa zuwa kudancin Najeriya a zaben 2027, domin gabatar da ƙalubale mai ƙarfi ga Tinubu.
Wike ya sha kaye a zaɓen fidda gwani na PDP a 2022 inda Atiku Abubakar ya doke shi kuma ya zama ɗan takarar jam’iyyar a zaben 2023.

Ya ce: “Ba zan sake tsayawa takara ba. Ba zan tsaya takara da wanda nake aiki da shi ba. Wa zai ci zabe in ba shi ba?”

A wata sanarwa dangane da rikicin da ke cikin jam’iyyar PDP, Wike ya bayyana ƙuntatawarsa da halayen wasu daga cikin mambobin jam’iyyar tare da s**ar manufofin jam’iyyar adawar.

Ya ce: “Kai adawa kake yi; adawa ba ta nuna isa da raini. Jam’iyya mai mulki ce ke nuna isa da raini domin tana da iko.”

“Wa ke cikin PDP? Achike Udenwa, tsohon gwamnan Imo. Babu ko ɗan majalisa guda da ya samu. Babu ko ɗan majalisar tarayya daya. Bai ba jam’iyyarsa koda kashi 3 cikin 100 na ƙuri’u ba, amma yana yin barazana.”

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AAG Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share