Haske Radio Online

Haske Radio Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Haske Radio Online, Radio Station, No. 5 Naibawa Gidan FIAT, Kano.

Kafar yaɗa labarai mai zaman kanta da take yada shirye-shiryen ta a internet a kowane lokaci cikin awa 24 a harshen Hausa

Ku aiko mana da rahotanin abubuwan dake faruwa a yankunan ku cikin hoto ko a rubuce ta wannan lambar +2347089474852 ko a WhatsApp.

08/06/2026

Jam’iyyar NDC ta sanar da ɗaukar wasu muhimman matakai da nufin karfafa dimokuradiyya a cikin jam’iyyar da tabbatar da ladabtarwa da kuma gina ta a matsayin babbar kafa ta siyasa gabanin zaɓuka masu zuwa.

08/06/2026

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya yi kira da a koma tattaunawar yarjejeniyar tsagaita wuta bayan sabuwar tashin hankalin da ya ɓarke a tsakanin Iran da Isra’ila.

Bayan samun goyon bayan Gwamnan Jahar Gombe, an amince da Jamilu Isyaku Gwamna, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyy...
08/06/2026

Bayan samun goyon bayan Gwamnan Jahar Gombe, an amince da Jamilu Isyaku Gwamna, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a watan da ya gabata.

Yanzu a babban zaɓen 2027 Gwamna zai fafata da Bala Tinka na jam’iyyar ADC, da kuma Isa Pantami na jam’iyyar PDP, wanda dukkansu -Tinka da Pantami, sun koma sabbin jam’iyyunsu ne bayan sun gaza samun tikitin takara a APC.

Yayin da yake sanar da Gwamna a matsayin ɗan takarar APC, Gwamna Inuwa Yahaya, ya bayyana shi a matsayin gogaggen ɗan siyasa kuma ƙwararren ma’aikacin gwamnati da ke da karɓuwa a tsakanin al’umma, wanda a cewarsa Gwamna yana da amana da kuma tasirin da zai tabbatar wa jam’iyyar nasara a zaɓe mai zuwa.

Da yake nuna godiyarsa kan wannan amana, Jamilu Gwamna, ya yi alƙawarin ci gaba da ɗora wa kan nasarorin da gwamnatin Jahar Gombe ta samu tare da ɗaga martabar jahar zuwa wani sabon matsayi na ci gaba.

Samun tikitin jam’iyyar APC mai mulki wani muhimmin sauyi ne a tafiyar siyasar Gwamna, wanda tun a shekarar 2007 ya fara neman kujerar gwamnan jahar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar ANPP.

A lokacin yaƙin neman zaɓensa na 2007, Gwamna ya ziyarci shalkwatar Kamfanin LEADERSHIP Group, inda ya bayyana burinsa da hangen nesansa na ci gaban Jahar Gombe.

Shekaru kusan ashirin kenan yana jiran wannan dama inda samun tikitin jam’iyyar mai mulki, wanda bai taɓa samu a baya ba, ya kusantar da shi ga cikar burinsa na zama gwamna, abin da ma sunansa “Gwamna” ke nuni da shi.

A shekarar 2011, ya shaida yadda ɗan uwansa, Ibrahim Dankwambo, ya bar aikin gwamnati a matakin tarayya tare da samun tikitin PDP, wanda ya kai shi ga zama gwamnan jahar.

Bayan shekaru takwas, yanayin siyasa bai ba da damar wani ɗan uwa ya gaji wani a kujerar gwamna ba amma daga bisani, a shekarar 2022, bayan ya kasa samun tikitin PDP, Jamilu Gwamna ya fice daga jam’iyyar tare da mara wa wa’adin mulki na biyu na Gwamna Inuwa Yahaya baya.

Haske Radio Online.

Rahotanni daga wasu majiyiyo masu karfi na nuni da cewa jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, na d...
08/06/2026

Rahotanni daga wasu majiyiyo masu karfi na nuni da cewa jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, na duba yiwuwar ficewa daga jam’iyyar NDC bayan sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar da bangaren Kwankwasiyya ya gabatar a Jihar Kano.

A cewar rahoton, lamarin ya samo asali ne daga takaddamar da ta kunno kai kan yarjejeniyar rabon tikitin takara tsakanin bangaren jam'iyyar da aka tarar da kuma bangaren Kwankwasiyya.

Yarjejeniyar dai ta tanadi bai wa bangaren Kwankwasiyya kaso 60 cikin dari na tikitin takara, yayin da bangaren jam'iyyar da aka tarar zai samu kaso 40 cikin dari.

Sai dai rahotannin sun ce sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar da bangaren Kwankwasiyya ya gabatar ya janyo rashin gamsuwa daga bangaren, wanda ya nuna rashin amincewarsa da matakin.

Majiyoyin sun ambato cewa akwai alamun bangaren Kwankwasiyya na nazarin wasu zabuka na siyasa gabanin zaben 2027, ciki har da yiwuwar komawa jam’iyyar PRP domin bai wa magoya bayan tafiyar damar shiga takara karkashin wata jam'iyya.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ko shugabannin bangaren Kwankwasiyya da ke tabbatar da ficewa daga jam'iyyar NDC.

Haske Radio Online.

Wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan ‘yancin addini ta fara wata ziyarar aiki ta makonni biyu a Najeriya a ...
08/06/2026

Wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan ‘yancin addini ta fara wata ziyarar aiki ta makonni biyu a Najeriya a daidai lokacin da ake ce-ce-ku-ce a duniya dangane da ‘yancin addini da kuma matsalolin tsaro a ƙasar ta Afirka mafi yawan jama’a.

Nazila Ghanea, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan ’yancin addini ta isa Najeriya a ranar Litinin domin gudanar da wata ziyara da za ta kai zuwa Abuja, Kano, da kuma Jos a Jahar Filato.

Haske Radio Online.

Dan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi Allah wadai da yadda wasu kafafen yaɗa labarai ke yi wa Ful...
08/06/2026

Dan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi Allah wadai da yadda wasu kafafen yaɗa labarai ke yi wa Fulani kuɗin goro kan matsalolin da s**a shafi tsaro da kuma garkuwa da mutane a Najeriya.

Peter Obi ya bayyana haka cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a safiyar yau Litinin.

Ya ce ba dai-dai ba ne a riƙa danganta laifukan ta'addanci ga ƙabila gaba ɗaya, yana mai cewa hakan yana haifar da rarrabuwar kai kuma ba adalci ba ne ga sauran ’yan ƙabilar.

Haske Radio Online.

08/06/2026

Dakarun juyin juya halin Iran, IRGC, sun ce sun ƙaddamar da hare-haren ramuwar gayya da makamai masu linzami kan cibiyoyin man Isra'ila da ke Haifa.

Wani rahoto da aka gabatar ya bankado wani yanayi mai tayar da hankali a wani Asibiti da ke Jihar Kano, inda aka gano ce...
08/06/2026

Wani rahoto da aka gabatar ya bankado wani yanayi mai tayar da hankali a wani Asibiti da ke Jihar Kano, inda aka gano cewa wasu mata masu nakuda suna haihuwa a kan leda sakamakon ƙarancin kayan aiki da rashin wadatattun kayan more rayuwa a cibiyar lafiyar.

Rahoton ya nuna cewa matsalar ta jefa mata masu juna biyu cikin mawuyacin hali, tare da haifar da damuwa kan lafiyarsu da ta jariran da suke haifa. Haka kuma, an bayyana cewa ƙarancin gadaje da wasu muhimman kayayyakin jinya na daga cikin matsalolin da asibitin ke fuskanta.

Lamarin ya jawo martani daga al'umma da masu fafutukar kare haƙƙin mata, inda s**a yi kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki da su gaggauta ɗaukar matakan da s**a dace domin inganta harkokin kiwon lafiya a asibitin.

Masu ruwa da tsaki sun jaddada cewa samar da ingantattun kayan aiki da kyakkyawan muhalli a asibitoci na da matuƙar muhimmanci wajen kare lafiyar mata masu juna biyu da jarirai.

Ana sa ran hukumomin da abin ya shafa za su gudanar da bincike tare da ɗaukar matakan da s**a dace domin magance matsalar.

Daga Samira Sa'ad Zakirai.

08/06/2026

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqaei, ya ce Amurka ce ke da alhakin hare-haren da Isra’ila ta kai wa Iran.

Kakakin Jam'iyyar NDC, na ƙasa Ibrahim Waya ne ya bayyana haka, wanda ya ce wannan shi ne dalilinsu na sauya sunayen 'ya...
08/06/2026

Kakakin Jam'iyyar NDC, na ƙasa Ibrahim Waya ne ya bayyana haka, wanda ya ce wannan shi ne dalilinsu na sauya sunayen 'yan takara a wasu ƙananan hukumomin Kano.

A cewarsa tun farko akwai alƙawarin kaso 60/40 da aka yi tsakanin jam'iyya da Rabi'u Kwankwaso, wanda gudun rikici ne yasa s**a ɗauki matakin na gaggawa kuma hatta babban jagoran Jam'iyyar ya sanya baki game da lamarin.

Haske Radio Online.

Address

No. 5 Naibawa Gidan FIAT
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Haske Radio Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category