08/06/2026
Bayan samun goyon bayan Gwamnan Jahar Gombe, an amince da Jamilu Isyaku Gwamna, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a watan da ya gabata.
Yanzu a babban zaɓen 2027 Gwamna zai fafata da Bala Tinka na jam’iyyar ADC, da kuma Isa Pantami na jam’iyyar PDP, wanda dukkansu -Tinka da Pantami, sun koma sabbin jam’iyyunsu ne bayan sun gaza samun tikitin takara a APC.
Yayin da yake sanar da Gwamna a matsayin ɗan takarar APC, Gwamna Inuwa Yahaya, ya bayyana shi a matsayin gogaggen ɗan siyasa kuma ƙwararren ma’aikacin gwamnati da ke da karɓuwa a tsakanin al’umma, wanda a cewarsa Gwamna yana da amana da kuma tasirin da zai tabbatar wa jam’iyyar nasara a zaɓe mai zuwa.
Da yake nuna godiyarsa kan wannan amana, Jamilu Gwamna, ya yi alƙawarin ci gaba da ɗora wa kan nasarorin da gwamnatin Jahar Gombe ta samu tare da ɗaga martabar jahar zuwa wani sabon matsayi na ci gaba.
Samun tikitin jam’iyyar APC mai mulki wani muhimmin sauyi ne a tafiyar siyasar Gwamna, wanda tun a shekarar 2007 ya fara neman kujerar gwamnan jahar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar ANPP.
A lokacin yaƙin neman zaɓensa na 2007, Gwamna ya ziyarci shalkwatar Kamfanin LEADERSHIP Group, inda ya bayyana burinsa da hangen nesansa na ci gaban Jahar Gombe.
Shekaru kusan ashirin kenan yana jiran wannan dama inda samun tikitin jam’iyyar mai mulki, wanda bai taɓa samu a baya ba, ya kusantar da shi ga cikar burinsa na zama gwamna, abin da ma sunansa “Gwamna” ke nuni da shi.
A shekarar 2011, ya shaida yadda ɗan uwansa, Ibrahim Dankwambo, ya bar aikin gwamnati a matakin tarayya tare da samun tikitin PDP, wanda ya kai shi ga zama gwamnan jahar.
Bayan shekaru takwas, yanayin siyasa bai ba da damar wani ɗan uwa ya gaji wani a kujerar gwamna ba amma daga bisani, a shekarar 2022, bayan ya kasa samun tikitin PDP, Jamilu Gwamna ya fice daga jam’iyyar tare da mara wa wa’adin mulki na biyu na Gwamna Inuwa Yahaya baya.
Haske Radio Online.