Haske Radio Online

Haske Radio Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Haske Radio Online, Radio Station, No. 5 Naibawa Gidan FIAT, Kano.
(1)

Kafar yaɗa labarai mai zaman kanta da take yada shirye-shiryen ta a internet a kowane lokaci cikin awa 24 a harshen Hausa

Ku aiko mana da rahotanin abubuwan dake faruwa a yankunan ku cikin hoto ko a rubuce ta wannan lambar +2348169744760 ko a WhatsApp.

An gudanar da jana’izar jama’a a ranar 8 ga watan Agusta a ƙauyen Efeyi da ke jihar Benue, arewa ta tsakiyar Najeriya, i...
09/08/2026

An gudanar da jana’izar jama’a a ranar 8 ga watan Agusta a ƙauyen Efeyi da ke jihar Benue, arewa ta tsakiyar Najeriya, inda aka yi wa mutum 16 da ake zargin wasu ƴanbindiga s**a kashe jana’iza, k**ar yadda jaridar Vanguard mai zaman kanta ta ruwaito.

Rahotanni sun ce an kashe mutanen ne lokacin da aka kai hari a ƙauyen a ranar 28 ga watan Yuli, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici tare da tilasta wa da dama daga cikinsu tserewa domin tsira da rayukansu.

Mazauna kauyen sun bayyana harin a matsayin mummunan hari da aka kai ba tare da wani dalili ba.

Harin ya faru ne watanni bayan da wasu ‘yan bindiga s**a kashe mutane da dama a wasu kauyuka da ke cikin gundumar Ugboju, a ƙaramar hukumar Otukpo.

A wajen jana’izar, ’yan uwa, shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, shugabannin siyasa da malaman addini sun hallara domin yin bankwana da wadanda aka kashe.

Wani limamin Cocin Katolika ne ya jagoranci addu’o’in jana’izar, kafin a sauke akwatunan gawarwakin wadanda aka kashe cikin kaburburansu, yayin da ’yan uwa da makusanta ke kuka da alhini.

Jihar Benue, wadda ke yankin Middle Belt na Najeriya, na fama da rikice-rikice da s**a samo asali musamman daga hare-haren ramuwar gayya da satar shanu tsakanin makiyaya, wadanda galibinsu Musulmi ne, da manoma, wadanda galibinsu Kiristoci ne.

Haske Radio Online.

Iran ta ce tattaunawar da take yi da Oman kan sababbin tsare-tsaren gudanar da zirga-zirga a Mashigar Hormuz na tafiya y...
09/08/2026

Iran ta ce tattaunawar da take yi da Oman kan sababbin tsare-tsaren gudanar da zirga-zirga a Mashigar Hormuz na tafiya yadda ya k**ata.

Sai dai babban jami'in tsaro na Tehran, Mohammad Bagher Zolghadr, ya yi gargaɗin cewa ba za a sake buɗe mashigar ruwan ba har sai Amurka ta amince da wasu sharuɗɗa guda shida.

Daga cikin sharuɗɗan akwai sassauta takunkumin tattalin arziki da aka ƙaƙaba wa Iran, da biyan diyya kan asarar yaƙi, da kuma kawo ƙarshen toshe tashoshin jiragen ruwan ƙasar da Amurka ke yi.

Wakilin BBC ya ce abin da muka ji daga shugaban tsaron shi ne sai an cimma wadannan bukata idan har za a sake bude Mashigar Hormuz Tun da farko, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya ce Iran da Oman sun yi kusa sosai da cimma yarjejeniya kan wata sabuwar hanya ta zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar ta Hormuz.

A halin da ake ciki kuma, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta ce Iran ta kai harin makami mai linzami kan ɗaya daga cikin jiragen ta na ruwa na dakon mai.

Haske Radio Online.

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Najeriya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙuduri aniyar kawo ...
09/08/2026

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Najeriya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen zazzabin cizon sauro tare da ƙara zuba kuɗaɗe a fannin kiwon lafiya, domin rage dogaro da tallafin ƙasashen waje.

Gidan talabijin na NTA ya ruwaito Pate ya bayyana hakan ne a Abuja yayin da yake karɓar tawagar kwamitin amintattu na Malaria Consortium, wadda ta kai ziyara ma’aikatar domin taya Najeriya murnar raguwar yawan yara masu ɗauke da kwayar cutar daga kashi 42 cikin 100 a shekarar 2010 zuwa kashi 15 cikin 100 a 2025.

Haske Radio Online.

Allah yayiwa mahaifiyar ɗaya daga cikin ma'aikatan Fa'ida FM Radio Malam Madori rasuwa, Comrade Umar Baban Yaya Sabon gi...
09/08/2026

Allah yayiwa mahaifiyar ɗaya daga cikin ma'aikatan Fa'ida FM Radio Malam Madori rasuwa, Comrade Umar Baban Yaya Sabon gida.

Muna addu'ar Allah yaji kan ta da rahama.

Haske Radio Online.

‎Rahotanni sun ce dakarun gwamnatin Yemen sun kai hare-haren jiragen sama marasa matuka kan sansanonin Houthi a lardin A...
09/08/2026

‎Rahotanni sun ce dakarun gwamnatin Yemen sun kai hare-haren jiragen sama marasa matuka kan sansanonin Houthi a lardin Ad Dali da ke kudancin kasar.

‎Dakarun Southern Armed Forces sun ce hare-haren sun lalata sansanonin soji, maboya, ramukan karkashin kasa da motocin yaki, tare da jikkata ko kashe mayakan Houthi da dama.

‎Houthi ba ta fitar da martani kan wannan ikirari ba.

Haske Radio Online.

09/08/2026

Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka, Pentagon, ta umarci kamfanonin kayan tsaro na ƙasar su hanzarta ƙera mak**ai tare da bayar da su a yayin da yaƙin Iran ya kusa ƙarar da muhimman mak**ai na Washington, a cewar wani rahoto na kafar watsa labarai.

‎Rahotanni daga kafafen yada labarai na Malaysia sun ce hukumomin kasar sun k**a wani kwantena da ake zargin yana dauke ...
09/08/2026

‎Rahotanni daga kafafen yada labarai na Malaysia sun ce hukumomin kasar sun k**a wani kwantena da ake zargin yana dauke da kayayyakin da za a kai Isra’ila a tashar Tanjung Pelepas da ke jihar Johor a ranar 7 ga Agusta.

‎Firaministan Malaysia, Anwar Ibrahim, ya yabawa jami’an tsaron kan iyaka bisa matakin, yana mai cewa kasar ba za ta zama hanyar wucewar kayayyakin da za su iya tallafa wa Isra’ila ba.

‎Hukumar ta ce kayayyakin na iya saba dokar kwastam ta Malaysia wadda ta haramta fitar da kayayyaki zuwa Isra’ila kai tsaye ko ta wata kasa.

Haske Radio Online.

‎Rahotanni sun ce Majalisar Wakilan Amurka ta amince da wani kuduri da ke bukatar Shugaba Donald Trump ya dakatar da kai...
09/08/2026

‎Rahotanni sun ce Majalisar Wakilan Amurka ta amince da wani kuduri da ke bukatar Shugaba Donald Trump ya dakatar da kaiwa Iran hare-hare ba tare da amincewar Majalisa ba.

‎Kudurin, wanda ’yar Majalisa Pramila Jayapal ta gabatar, ya samu kuri’u 214 kan 208, tare da goyon bayan wasu ’yan Republican hudu.

Haske Radio Online.

Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar ...
09/08/2026

Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar Bahar Maliya.

Kakakin rundunar sojin ƙungiyar, Yahya Saree, ya ce harin da aka kai kan matatar man fetur ta Aramco da ke Jazan, martani ne kan kutsen da Saudiyya ke yi a arewa maso yammacin Yemen.

Ma'aikatar mak**ashi ta Saudiyya ta ce jami'an kashe gobara sun yi nasarar kashe gobarar da ta tashi a wurin.

Mayaƙan Houthi sun sanar da kafa katanga ta ruwa kan Saudiyya a watan da ya gabata, lamarin da ya sake rura wutar rikicin tare da ƙara matsin lamba kan samar da mak**ashi a duniya, wanda yaƙin Iran ya haifar.

A gefe guda kuma, babbar hukumar tsaron Iran ta yi gargadin cewa ba za a bude mashigar ruwan Hormuz ba har sai Amurka ta amince da wasu bukatu guda shida, ciki har da sassauta takunkuman da aka ƙaƙaɓawa Iran, biyan diyya kan barnar yakin, da kuma kawo karshen katangar da aka sanya wa tashoshin jiragen ruwa na Iran.

Haske Radio Online.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ce za ta fara sarrafa abubuwan tsara iyali a cikin ƙasar domin ƙarfafa lafiyar jama’ar ƙa...
09/08/2026

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ce za ta fara sarrafa abubuwan tsara iyali a cikin ƙasar domin ƙarfafa lafiyar jama’ar ƙasar da kuma amfani da jama’ar ƙasar mai yawan matasa a matsayin abin haɓaka tattalin arziki mai dorewa.

Wata sanarwar mataimakin daraktan watsa labarai da hulɗa da jama’a na ministan lafiyar Najeriya, Prof. Muhammad Ali Pate, Ado Bako, ya fitar ranar Jumma’a ta bayyana cewa gwamnatin ƙasar ta kafa wani kwamiti tsakanin ma’aikatun gwamnati domin ciyar da shirin gaba, k**ar yadda kafar Channels ta Najeriya ta ruwaito.

Farfesa Pate ya bayyana shirin a matsayin wani muhimmin mataki ga Najeriya da ma sauran yankin Afirka kudu da Sahara, yana mai jaddada cewa sarrafa kayayyakin a cikin gida zai rage dogaro kan kayayyakin da ake shigowa da su da samar da ayyukanyi ga matasa ‘yan Najeriya da kuma samar da kima ta tattlin arziki a cikin ƙasar.

Yayin da yake ƙaddamar da kwamitin a Abuja, Pate ya ce jama’ar ƙasar su ne kadarar ƙasar mafi girma kuma dole a sauya su zuwa albarkatu masu samar da abubuwa da za su iya kawo ci-gaba da wadatar ƙasar.

Ministan lafiyar ya ce an kafa dandalin kwamitin ne da zummar cim ma fatan Shugaba Tinubu na samar da Najeriya mai wadata da zaman lafiya da ya mayar da hankali kan mutane, yana mai jaddada cewa yawan jama’ar Najeriya da ke daɗa ƙaruwa zai iya zama muhimmiyar kadara ko kuma nauyi dangane da irin jarin da aka zuba a kiwon lafiya da ilimi da ƙarfafa mutane da kuma yanayin ayyuka.

Ya ce Najeriya, wadda take da kimanin yawan mutane da s**a kai miliyan 230 million kuma yawnacinsu matasa ne, inda take ƙara miliyoyin mutane zuwa cikin yawan jama’arta a ko wace shekara kuma an yi kiyasin cewa adadin mutane ƙasar zai kai miliyan 450 zuwa miliyan 500 nan da shekarar 2050.

Saboda haka ministan ya jaddada bukatar da ke akwai ta zuba jari da gangan wajen inganta jarin rayuwar mutane don tabbatar da cewa adadin jama’r da ke ƙaruwa yana da lafiya da ilimi da ƙwarewa da kuma iya samar da ababe ga tattalin arziki.

Haske Radio.

Address

No. 5 Naibawa Gidan FIAT
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Haske Radio Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category