Arewa Media 24/7

Arewa Media 24/7 News24/7 | Advertisements | Public Awareness | Entertainment Programs | Political Analysis| Breaking News

A ganinku, ya k**ata hukumomin tarayya irin su FRSC su riƙa aiki a titunan cikin jiha, ko kuwa wannan ya k**ata a bar sh...
08/07/2025

A ganinku, ya k**ata hukumomin tarayya irin su FRSC su riƙa aiki a titunan cikin jiha, ko kuwa wannan ya k**ata a bar shi ne ga hukumomin sufuri na jihohi kawai?

Fitaccen lauya, Barrister Abba Hikima Fagge, ya shigar da ƙara a gaban kotu a matsayin ƙarar kare muradun jama'a (public interest litigation) yana kalubalantar Hukumar Kiyaye Afkuwar Hadurra ta Ƙasa (FRSC) saboda ci gaba da gudanar da ayyukanta a titunan cikin Jihar Kano ba tare da sahalewar doka ba.

A cikin ƙarar da ya shigar, lauya Abba Hikima ya bayyana cewa FRSC ba ta da hurumin gudanar da aiki a kan titunan cikin jiha, saboda wannan aikin na cikin ikon hukumomin sufuri na jihohi.

Ya ce kasancewar su a titunan Kano yana tauye 'yancin walwala da zirga-zirga na 'yan ƙasa, wanda kundin tsarin mulki ya basu.

“Wannan batu ne na doka da kare haƙƙin jama’a. Idan aka bar irin wannan, zai iya zama barazana ga dimokuraɗiyya da walwalar jama’a,” in ji Barrister Hikima.

MARTANI GA MAWAKI RARARAWai Rarara yace zai iya kayar da Alhaji Atiku Abubakar da jam’iyyar ADC idan ya tsaya takarar Sh...
08/07/2025

MARTANI GA MAWAKI RARARA

Wai Rarara yace zai iya kayar da Alhaji Atiku Abubakar da jam’iyyar ADC idan ya tsaya takarar Shugaban Kasa a 2027 ? Wannan magana ba karamin Abin takaici bane abin Allah wadai ne mawaki k**arka yayi wannan furuci na rashi da'a,

Rarara, ka sani, shugabancin kasa ba rawa bane, ba waka bane, ba kida bane, kuma ba shirme bane. Ilimi ne, sanin mak**ar mulki ne, hangen nesa ne, da kuma kwarewa wajen jagorantar al’umma masu hankali da mutunci, ba dabbobi ba ne da za ka tara su kace kana jagorantarsu.

Ni a matsayina na Amb. Imran Abdullahi (Barden Samarin Nigeria), Shugaban Kungiyar Atiku Door to Door Mobilization, ina fada maka a fili: Jahili ba zai jagoranci Nigeria ba! Idan kai mawaki ne mai daukar nauyin wakar tallar wasu, ka tsaya akan aikinka, ka guji zagin mutanen kirki da ka raina a baka.

Nigeria batayi lalacewa ba har sai mawaki lalatacce kalamansa zai ce yana neman shugabancin kasa. Mun sani siyasa ba ta wasa bace, kuma Najeriya ba filin rawa bane da zaka rika tsalle-tsalle kana kirari.

Muna da tabbacin Atiku Abubakar, mai hangen nesa, ilimi da nagartaccen tarihin aiki, ya fi cancanta fiye da duk wani mawaki da yake daukar siyasa a matsayin hanyar wasan kwaikwayo.

Don haka, idan kai mawaki ne, kayi wakarka, amma ka sani shugabancin kasa na bukatar ilimi, hikima, mutunci da sanin mak**ar mulki, ba waka da rawa ba Allah ya kara tabbatar da nasarar Alhaji Atiku Abubakar a 2027.

✍️
Amb. Imran Abdullahi (Barden Samarin Nigeria) Shugaban Kungiyan Atiku Door to Na Kasa baki daya

08/07/2025

Yau Shekaru 14 da kotun koli ta sake tabbatar wa yar wasan hausa (Kannywood) Rabi Isma'il (Rabi Acid) hukuncin kisa.

A ranar 8 Ga Watan Yuli 2011, kotun koli ta tabbatarwa jarumar Kannywood hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Rabi Isma'il (wacce ake yiwa lakabi da Rabi Acid) yar Asalin Jihar Edo ce, amma haifaffiyar Tudun Wada a Kano ce, ta fito a fina-finan Kannywood wanda su ka hada da Tsumagiya, da Aya, da Manakisa. A ranar Kirsimetin shekarar 2002, Rabi ta tunkuda saurayinta Alhaji Ibrahim Zazu cikin ruwan Tiga, in da rai yayi halinsa. Amma kafin ta tunkudashi shi cikin ruwan, sai da ta ba shi alewa cakuletin Ekiles wacce tayiwa cushe da maganin bacci. Sai da Rabi ta tabbatar ya fita a hayyacinsa sannan ta lalube aljihunsa ta kwashe kudi naira dubu dari, kana ta tunkudashi cikin ruwan.

Wannan dama dai ya nuna da niyar kisa ta tura Auwalu Zazu cikin ruwan. Jami'an binkice sun gano rabi ta aikata hakane domin ta gaje dukiyarsa. Kasancewarsa hamshakin maikudi.

Don haka a ranar 5 ga Junairun shekarar 2005 babbar kotun jihar Kano ta sami Rabi Acid mai lambar fursuna k/22c da laifin kisan kai. Mai shari'a Halliru Muhammad Abdullahi ya yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, sai dai Rabi ta daukaka kara a kotun daukaka kara da ke Kaduna. A nanma dai kotun ta sake tabbatar wa da Rabi laifinta. Daga nan kuma sai ta sake daukaka kara zuwa kotun koli da ke Abuja. In da a rana mai k**ar ta yau 8 ga watan Yuli 2011 kotun koli ta tabbatar mata hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Alkalan kotun guda bakwai karkashin mai shari'a Francis fiddodi Tabai, sunce sun gamsu da hujjujin da aka bayar a kotun farko, don haka su ka sake tabbatar mata da hukuncin Kksa ta hanyar rataya. Sai dai k**ar a Fim! A ranar 16 ga watan disambar 2011, sai Rabi Isma'il tayi batan dabo daga gidan yarin Hadejia, in da aka neme ta kasa ko sama aka rasa.

Bayanai sunce a kurkukun Kano aka fara daureta kafin daga baya a mayar da kurkukun Kaduna lokacin da ta daukaka kara. In da a can ne Rabi Isma'il ta zama Jar wuya, in da ta rika safarar sigari da kwaya da Wiwi. Har ma anyi zargin Rabi tana sheke ayar ta ne da manyan jami'an gidan yarin a lokacin da ta ke a tsare.

Bayan da kotun koli ta yanke mata hukuncin kisa sai a ka sauya mata matsuguni zuwa gidan kurkukun Hadejia. A Hadejian ne ta yaudari wani babban Ganduroba, su ka tsunduma cikin kogin soyayya. Ana wannan halin ne ta ke shaida masa cewa ta mallaki Miliyoyin Naira, kuma da zai nema mata bizar Amurka ya fitar da ita daga kurkuku za ta aure shi," su ta re a can suyi ta cin duniyarsu da tsinke. Haka kuwa a kai a ranar 16 ga watan Disambar 2011, sai jami'in nan yayi hanyar da Rabi ta bi ta sulale daga kurkukun.

Sai dai a ranar 21 ga watan mayun 2017, jami'an tsaron DSS Su ka cafke Rabi Isma'il a kan iyakar Najeriya da Jamhuriyyar Benin.
A cewar mai magana da yawun hukumar gidan yarin, Francis Enobore, jami’an leken asiri na hukumar kula da gidajen yari ta Najeriya ne s**a sake k**a Ismail tare da goyon bayan jami’an tsaro na DSS.

Daga nan su ka mika ta ga hukumar kula da gidajen Kurkuku ta kasa, a in da su ka sa ma mata gurbi a gidan kurkukun Kuje da ke Abuja. Shi kuma Ganduroban da ya taimaka mata ta tsere, an rage masa mukami tare da sauya masa wajen aiki. Hakan dai bai wa abokan aikinsa sa yawa dadi ba! Kasancewar laifinsa ya cancanci kora da gurfana a gaban Kotu.

Izuwa yanzu dai ba ni da labarin wani hali Rabi Isma'il (Rabi Acid) ta ke ciki.

✍️ Muhammad Cisse

Duniya Lambun Shagali: Adnan Oktar Malamin Addinin Islama Na Kasar Turkiyya Wanda Aka Yankewa Daurin Shekaru 8,658 Sabod...
07/07/2025

Duniya Lambun Shagali: Adnan Oktar Malamin Addinin Islama Na Kasar Turkiyya Wanda Aka Yankewa Daurin Shekaru 8,658 Saboda Laifin Badala

A ranar 17 ga Nuwamba, 2022, an yanke masa hukuncin daurin shekaru 8,658 a gidan yari saboda ya jagoranci gungun masu aikata laifukan badala, yin leken asiri na siyasa da na soja, lalata da kananan yara, da sauran tuhume-tuhume.

Wata kotu a birnin Istanbul ta yanke hukuncin daurin shekaru 8,658 a gidan kaso ga wani ma’aikacin gidan talabijin da ya kewaye kansa da wasu mata masu sanye da kayan kwalliya da ya kira ‘ya'yan kyanwa.

Adnan Oktar, wanda aka bayyana a matsayin "shugaban kungiyar asiri", ya jagoranci shirye-shiryen talabijin da mata ke kewaye da shi yayin da yake wa'azin halitta da dabi'un mazan jiya.

Ya kuma buga littafai cikin harsuna da dama a duniya, karkashin sunan alkalamin Harun Yahya.

An k**a Adnan Oktar mai shekaru 66 da daruruwan mabiyansa a shekarar 2018 bayan wani samame da 'yan sanda s**a kai a Villa dinsa, ya nuna cewa yana gudanar da wata kungiyar masu aikata laifuka a karkashin wata kungiyar asiri ta addinin Islama wadda ta yi kamfen na kin jinin juyin juya hali na kasa da kasa, da gidajen buga littattafai da kafafen yada labarai daban-daban.

An kuma rufe tasharsa ta A9 TV ta yanar gizo.

Muhammad Cisse

Sarkin Kano Ado: Wani Gari Yafi Gaban KunuAnce wata rana sarkin Kano Ado ya dawo daga tafiya, ya biyo ta Katsina Road, s...
07/07/2025

Sarkin Kano Ado: Wani Gari Yafi Gaban Kunu
Ance wata rana sarkin Kano Ado ya dawo daga tafiya, ya biyo ta Katsina Road, sai yake cewa Sarki Waziri (Danrimi), akwai wani gida na anan, da na mallaka tun kafin in zama sarki, amma ban kara waiwayarsa ba, ban sani ba ko zan gane shi?! Sarki Waziri yace " Allah ya taimaki sarki, sai sai inzo in duba" sarki yace "gidan kane? Gida nane, zan zo in duba kayana da kai na.
Bayan yan kwanaki, rannan da dare sai sarki ya sa aka kira masa Danrimi, yace masa yazo ya raka shi unguwa. S**a tafi, Danrimi na jan mota, sai Katsina Rd, su shiga nan, su shiga nan, har s**a zo daidai wani gida. Sarkin Kano ya umarci Danrimi ya tsaya, yace masa "ai kuwa wannan ne gidan, tabbas"
S**a fito, s**a saka akayi musu sallama da maigidan cikin dare. Maigidan ya fito, s**a gaisa. Sarkin Kano ya kalle shi yace " wannan gidan ka ne?" Yace "eh" yace masa saya kayi ko kuma baka akayi? Yace gaskiya asali gidan mahaifinmu ne muka gada. Sarki yace masa " kai dan wane ne( ya fadi sunan maigidan), yace eh. Kafin ya mutu bai bar muku wasiyya ba? Sarki ya tambayi maigidan. Yace "eh ya bar mana wasiyya, yace gidan nan na wani mutum ne Malam Ado".
Sarki yace masa " to nine malam Ado, kuma ba zuwa nayi don in tashe ku ba, na sayi wannan gida sama da shekara 40 da s**a wuce, kuma ni na saka mahaifinku a ciki, Amma abinda nake so da kai, gobe kazo fada, muje gaban sarki da kai, saboda a tabbatar da wannan magana, komai ayi shi da hukuma yafi amfani. Amma kar ka ji komai, ba tashinku zanyi ba". Maigidan ya amsa yace "to Allah ya kaimu". Sarki yace masa, In kazo ka nemi Sarki Waziri, zai kaimu gaban sarki da kai, sai a tabbatar da maganar.
Da safe maigida ya tafi fada, yaje ya nemi Sarki Waziri, aka kai shi office din sarki waziri. Ya gabatar da kansa, sarki Waziri yace " kaine?" Yace "eh nine" yace "to jira"
Da sarki ya zauna a fada aka kira bawan allahnan, shi dai yana ta zura ido baiga malam Ado ba. Har aka kai shi gaban sarki.
Sarki yace masa " kaine muka je gidan

Hukumar kiyaye Afkuwar Hadurra ta kasa reshan jahar Kano ta tabbatar da mutuwar mutane 21 a wani Mummunan hadarin mota d...
07/07/2025

Hukumar kiyaye Afkuwar Hadurra ta kasa reshan jahar Kano ta tabbatar da mutuwar mutane 21 a wani Mummunan hadarin mota da ya ritsa da matafiya 24 akan titin Zaria zuwa kano, a tsakanin wata motar dakon kaya kirar Daf da kuma wata motar haya kirar Toyota Hummer dauke da matafiya a cikinta.

A wata sanarwa da Mai magana da yawun Hukumar kiyaye Afkuwar Hadurra ta kasa Abdullahi Labaran ya fitar anan kano ya ce mutane 21 sun mutu asak**akon k**awa da wuta da motocin biyu su ka yi jimkadan da afkuwar hadarin, a inda kuma Jami’an ceto su ka garzaya da mutun uku zuwa Asibiti.

Sanarwar ta ce Sak**akon Binciken farko-farko ya dora Alhakin afkuwar hadarin akan Direban Motar hayar da matafiya su ke cikinta kirar Totota Hummer a sak**akon aron Hannu da ya yi har kuma su ka yi taho mu gama da juna a daidai Kasuwar Dogo da ke a Dakatsalle anan kano.

Shin wadanne matakai ya k**ata a dauka domin magance yawaitar hadurra akan titin zaria zuwa kano musamman adaidai Dakatsalle?

Shin Direbobi ya k**ata a dorawa laifi kokuwa har da Gwamnati?

YANZU-YANZU: Gwarazan mayakan Yamen, sun fara mayar da martani ba kakkautawa kan Isra'ila, bayan wani sabon harin bazata...
07/07/2025

YANZU-YANZU: Gwarazan mayakan Yamen, sun fara mayar da martani ba kakkautawa kan Isra'ila, bayan wani sabon harin bazata da Isra'ila ta kai wasu sassan birnin Yamen.

📸—Arewa Media 24/7

WUTA SALLAU:  "Aikin Gwamnati Da Siyasa Ba Hanyar Arziki Ba ne, Duk Wanda Kaga Ya yi Arziki Don Yayi Aikin Gwamnati Ko K...
07/07/2025

WUTA SALLAU: "Aikin Gwamnati Da Siyasa Ba Hanyar Arziki Ba ne, Duk Wanda Kaga Ya yi Arziki Don Yayi Aikin Gwamnati Ko Kuma Ya yi Siyasa To Mafi Yawa Daga Cikinsu Barayi ne"

Cewar- Sanata Ali Ndume Daga Jihar Borno.

Me Zakuce?

POTISKUM LGA.YOBE STATE– MARKET UPDATE.!Alhamdulillah! Prices of grains such as beans, millet, sorghum, and red beans ha...
07/07/2025

POTISKUM LGA.
YOBE STATE– MARKET UPDATE.!

Alhamdulillah! Prices of grains such as beans, millet, sorghum, and red beans have significantly dropped this week!

Grain Prices at Potiskum Grain Market, Yobe State , June 29th, 2025

Maize (Masara)
– ₦45,000 to ₦46,000

Millet (Gero)
– ₦52,000 to ₦55,000

Sorghum – Small Load (Dawa Ɗan Lodi)
– ₦38,000 to ₦40,000

Sorghum – Kaura Type (Dawa Kaura)
– ₦47,000 to ₦48,000

White Beans (Farin Wake Misra & Manya)
– ₦90,000 to ₦86,000

Red Beans – Large (Jan Wake Manya)
– ₦90,000 to ₦95.000

Roselle (Zobo – Dried Flower)
– ₦20,000 to ₦21,000

Guna (Local Grain)
– ₦44,000 to ₦45,000
– ₦33,000 to ₦35,000 (variant)

Rice (Shinkafa)
– Polished: ₦125,000
– Broken/Processed: Price varies

Akwaro (Local Grain)
– ₦30,000 to ₦32,000
– Dan Ngalda variety: ₦21,000 to ₦23,000

Groundnut (Gyada)
– ₦130,000 to ₦135,000

Gangala (Local Dry Produce)
– ₦180,000 to ₦183,000

Wala/Wuyo Sorghum
– ₦40,000 to ₦41,000

May Allah continue to ease our affairs – Ameen.

See you next week for another market update!

Compiled by: Idriss Zakari Yobe
Date: 04th Al-Muharram 1446 / 29th June 2025

GASKIYAR MAGANA KAN SABON FARASHIN YIN SIM-SWAP ,BVN , DA NIN Jiya ake ta rade-radin mai da farashin SIM-SWAP wadda ake ...
07/07/2025

GASKIYAR MAGANA KAN SABON FARASHIN YIN SIM-SWAP ,BVN , DA NIN
Jiya ake ta rade-radin mai da farashin SIM-SWAP wadda ake kira welcome back to dole sai ka biya kudi Naira dubu hamsin .

Salmanul Paris ya ziyarci masu aikin sim card a wannan safiyar domin tabbatar da wannan magana kuma dukkan su sun tabbatar mana da cewa tabbas ne yanzu idan za ka yi welcome back to sai ka biya Naira dubu hamsin cif-cif .

BVN Dubu tamanin yayin da katin shaidar dan kasa kuma naira dubu talatin.

Wannan na nufin idan wayar ka ta fadi ko aka sace maka , to tabbas sai ka nemi dubu hamsin na simcard kadai kafin ka fara neman kudin sayar wata sabuwar wayar.

DA ƊUMI-DUMINSA.Daga Birnin Tarayya Abuja Tsohon gwamnan jihar Kano Sen. Rabi'u Musa Kwankwaso Yaba Jagorantar taron mas...
06/07/2025

DA ƊUMI-DUMINSA.

Daga Birnin Tarayya Abuja Tsohon gwamnan jihar Kano Sen. Rabi'u Musa Kwankwaso Yaba Jagorantar taron masu ruwa da tsaki Dan kafa wata sabuwar ƙungiya ta masu kishin ƙasa da s**a shirya mai suna (The National Movement) wanda ya ƙunshi manyan jiga-jigan ƴan siyasa da ƴan kasuwa da ƙungiyoyin fararen hula.

Daga cikin jiga-jigan ƴan siyasar dake tafiyar sun haɗa da:

- Tsohon gwamnan jihar Kano HE Rabiu Kwankwaso, Kano

- Tsohon gwamnan jihar Kogi H.E Captain Idris Wada.

- Tsohon gwamnan jihar Edo H.E Lucky Ignedion.

- Tsohon gwamnan jihar Kebbi H.E Adamu Alero.

- Tsohon gwamnan jihar Jigawa H.E Saminu Turaki.

- Tsohon gwamnan jihar Cross-river H.E Donald Duke.

- Tsohon gwamnan jihar Cross-river H.E Liyal Imoke.

- Tsohon gwamnan jihar ƙwara H.E Abdulfatah Ahmed.

- Tsohon gwamnan jihar Bayelsa H.E Serika Dicson.

-Tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa Prof. Attahiru jega.

-Tsohon shugaban hukumar bada tallafi ga jami'oin Najeriya Dr. Abba Bichi.

-Tsohon ministan matasa da wasanni Barr. Solomong Dalung.

-Prof. Pat Utomi

-Buba Galadima

-Sen. Rufai Hanga

Gwamnatin Shugaba Tinubu Na Tattaunawa Kan Dawo Da Tallafin Mai Gwamnatin tarayya karkashin shugaba Bola Ahmed Tinubu na...
05/07/2025

Gwamnatin Shugaba Tinubu Na Tattaunawa Kan Dawo Da Tallafin Mai

Gwamnatin tarayya karkashin shugaba Bola Ahmed Tinubu na duba yiwuwar dawo da tallafin mai ko kuma duba hanyoyin da za su saukaka farashin man fetur a kasar nan.

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnati ta fara tuntubar masana da masu ruwa da tsaki a harkar albarkatun mai domin gano mafita mai dorewa ga wahalhalun da 'yan kasa ke fuskanta sak**akon tsadar man fetur.

Wani jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa “ba lallai a kira shi dawo da tallafi kai tsaye ba, amma ana nazarin yadda za a rage wa talaka raɗaɗin hauhawar farashin mai”.

Kamar yadda kowa ya sani, cire tallafin mai a shekarar 2023 ya haifar da karin farashi a kowane sashe na rayuwa – daga sufuri zuwa abinci. Wannan ne yasa gwamnatin ke kokarin yin gyara don rage wa jama’a nauyi.

📌 Me kuke tunani?
Dawo da tallafi, ko a nemo wata dabara da zata rage farashi?

Address

Arewa Media
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share