Arewa Media 24/7

Arewa Media 24/7 Arewa Media 24/7 is a news and information platform focused on Northern Nigeria, providing continuous coverage of current events.

They have a presence on social media platforms like Facebook and WhatsApp, sharing updates and news with their audience.

Ministan Abuja Nyesom Wike, da matarsa Mai Shari’a Eberechi Suzzette JCA, na murna ya yin da za a shigar da ɗansu na far...
23/09/2025

Ministan Abuja Nyesom Wike, da matarsa Mai Shari’a Eberechi Suzzette JCA, na murna ya yin da za a shigar da ɗansu na farko Jordan Nyesom-Wike (kiran zuwa Bar) a matsayin Lauyan Kotun Koli ta Nijeriya a yau Talata.

Na sake fahimtar wani abu a wannan rayuwar. Duk abinda kaga ɗan adam ya yarda da abinda ka faɗa masa, to kaso mai yawa (...
20/09/2025

Na sake fahimtar wani abu a wannan rayuwar. Duk abinda kaga ɗan adam ya yarda da abinda ka faɗa masa, to kaso mai yawa (roughly 90%) yayi daidai da ra'ayin sa ne. Zai yi wahala ka faɗawa mutum wani abu na gaskiya ya yarda da kai matuƙar bai yi daidai da ra'ayin sa ba komin zahirin gaskiyar abinda ka faɗa ɗin. Mostly ɗan adam yana yarda da kai ne idan abinda kake faɗa masa ɗin shine abinda yake so. Zan baka misali da abinda zaka fahimta. Sau tari zaka ga ɗaliban mazahabar izala zai yi matuƙar wahala su yarda da abinda ɗan ɗarika zai faɗa musu koda gaskiya ce. Mostly ko sauraren su ma basa yi ballantana su gasƙata abinda malaman ɗariƙar suke faɗa. Haka zalika zai yi matuƙar wahala kaga ɗaliban mazahabar ɗarika sun yarda da abinda 'yan izala suke faɗa saboda kusan kowa daga cikin su ba wanda ya yarda da abinda ɗaya zai faɗa koda gaskiyar ce saboda basu yi tarayya a ra'ayi iri ɗaya ba.

Wannan abin shine gaskiyar magana ta kowacce irin fuska idan ka ɗauko duk wani abu a wannan rayuwar. Idan ka ji mutum yace yau dai wane ka faɗi gaskiya, to bawai daman baka faɗar gaskiyar bane a baya. A'a, a yanzu ne ka faɗi abinda yayi daidai da ra'ayin sa ne shiyasa zuciyar sa ta aminta da cewa yanzun ne ka faɗi gaskiyar. Wani koda gaskiyar ce ka ke faɗa a kullum, shi a karan kansa bazai taɓa yarda ba koda gaskiyar ce saboda kaine ka faɗa kuma bata yi daidai da ra'ayin sa ba. Amma da wani ne daban zai maimaita exactly abinda ka faɗa ɗin, 200% zai yarda saboda zuciyarsa ta cire duk wani personal sentiment a tattare da wancan ɗin ba kai ba.

Wannan dalilin ne yasa indai kana yin wani abu da kasan cewa har zuciyar ka tsakanin ka da Allah kake yi bisa adalci, to kar ma ka tilastawa kanka cewa lallai dole sai kowa ya yarda da kai. Wanda zai fahimce ka zai fahimce ka koda babu manyan hujjojin daka bashi. Wani kuma komin hujjar ka bazai taɓa yarda da kai ba koda a fadar Annabi aka rene ka saboda tarbiyyar ka.

Ameer Salihu Koko (RPHP, EMT)

Dan-Majlisar tarayya ne a Kasar nan, dazu na dauki hoton sa da uniform din Agaji a Masallacin Juma'ah na Sultan Bello-Ka...
19/09/2025

Dan-Majlisar tarayya ne a Kasar nan, dazu na dauki hoton sa da uniform din Agaji a Masallacin Juma'ah na Sultan Bello-Kaduna, ko wa ye ze fada mana sunan shi da jihan shi?

Wai shi wancan mai jan wandon yana nan ne KO baya nan???????👀👀👀👀👀👇👇👇
19/09/2025

Wai shi wancan mai jan wandon yana nan ne KO baya nan???????👀👀👀👀👀👇👇👇

Sanata Kwankwaso ya kuma koka kan irin wahalar da s**a sha wajen kafa APC amma yace a tsohuwar Gwamnatin marigayi Buhari...
19/09/2025

Sanata Kwankwaso ya kuma koka kan irin wahalar da s**a sha wajen kafa APC amma yace a tsohuwar Gwamnatin marigayi Buhari ko gutseren goro basu rabauta dashi ba. Haka PDP ya zarge ta da wufantar dashi duk da wahala da s**a yi mata tsawon Lokaci.

Ya kara da cewa yana son shiga APC amma abun tambayar a wane matsayi zai shiga.
Yace Lokaci ya wuce da wasu zasu lulluba musu bargo ko ayi musu jan biri ta baya a harkar Siyasar Najeriya dole sai an zauna a tebur anyi Alkawari yadda baza a tabar dasu a kowacce irin tafiya ba.

Trump zai hana Tinubu tazarce' -In ji Arangee Yayin da ake tunkarar babban zaben na 2027, wani mai amfani da shafin Face...
18/09/2025

Trump zai hana Tinubu tazarce'
-In ji Arangee

Yayin da ake tunkarar babban zaben na 2027, wani mai amfani da shafin Facebook, Onyee Arangee, ya wallafa wani faifan bidiyo na mintuna uku da ya yi ikirarin cewa shugaban Amurka Donald Trump zai tsoma baki a zaben Najeriya.

A cewar mai magana a bidiyon, Trump baya son Shugaba Bola Tinubu kuma ya sha alwashin yin duk abin da zai iya domin ya hana shi yin tazarce. Bidiyon ya samu karbuwa sosai inda ya tara 5,500 likes, 325 comments, 446 shares da kuma sama da kallo 25,000.

Bincike ya fallasa gaskiya
Rejoice Taddy, ta shafin Dubawa, ta gudanar da bincike domin gano sahihancin wannan ikirari, na cewar Donald Trump zai kitsa faduwar Tinubu a zaben na 2027.

Abin da aka gano shi ne cewa babu wata shaida daga manyan kafafen labarai a Najeriya ko na kasashen waje da ta nuna Trump ya yi irin wannan furuci.

Duk bayanansa na baya-bayan nan sun fi karkata kan batun shige da fice a Amurka, muhawarar tattalin arziki, da kuma shari’o’in da yake fuskanta a cikin gida.

Haka kuma, an gano cewa wannan ba shi ne karo na farko da aka danganta Trump da siyasar Najeriya ba.

Babu ruwan ubangiji da halin da Nigeria take ciki. Bai zama lallai sai ka yarda ba, saboda haka zaka iya fassara wannan ...
17/09/2025

Babu ruwan ubangiji da halin da Nigeria take ciki. Bai zama lallai sai ka yarda ba, saboda haka zaka iya fassara wannan rubutun duk yadda kake so. Ina da tabbacin sai na samu matsala da mutane da yawa a wannan rubutun. Amma koda zaka dena min magana sai na faɗa maka gaskiya 🫵. Duk abinda kake tunani saida nayi nazari mai faɗi ta kowacce irin fuska sannan nayi bincike daidai fahimta ta ga rayuwa sannan nayi wannan rubutun. Abinda yasa nayi rantsuwa cewa "Babu ruwan ubangiji da halin da Nigeria take ciki" shine:

Na farko duk wani abu daka sani a duniya tun daga kan Natural resources, intensive population, highly recommended naturally talented individuals, very productive fertile agricultural lands da sauran duk wani abu da ake buƙatar ɗan adam ya rayu da shi har yau ɗin nan Nigeria ce a gaba a duk faɗin ƙasashen Afrika 54 tunda aka shata duniya. Babu wani abu a duniya da wani mutum zai nuna a Europe, Asia, American ko Australian continent wanda Allah bai ajiye shi ba a Nigeria. Akwai wani great philosopher Adam Smith wanda ya taɓa cewa, "da ace za'a tambaye shi a ina ubangiji yake zaune a duniya zai ce wallahi a Nigeria yake". Duk wata ƙasa daka san ta cigaba a duniya sai da ta nemi haɗin gwiwa da tattalin arzikin Nigeria directly or indirectly. Google it idan baka yarda dani ba.

Dubai daka ke ji cewa ita ce ƙasa mafi more abubuwan jin daɗin rayuwar da ɗan adam yake buƙata yau a duniya, to a 1960 ko jihar Jigawa ma tafi ta cigaba ta kowacce irin fuska duniya da lahira idan baka sani ba. Titunan da suke ƙasar Saudi Arabia yau a duniya, a 1960 ko rabin titunan da suke ƙwaryar garin Kaduna ma basu da shi. Manyan gine-ginen da kake jin labarin su a kasar Singapore wanda yanzu itace ƙasa ta 4 a tattalin arziki a duniya, to a 1960 ko Jihar Lagos ta fita cigaba a duniya. Kar ka yarda da abinda na faɗa maka. Google it.

Amma kullum kana zaune kana ɗorawa ubangiji laifi tare da yin addu'o'i marasa fa'ida da sunan Tauhidi wai "Allah ya gyara mana Nigeria". Ko Ni nan ka isa na daga darajar ka ta kowacce irin fuska a duniya kuma ka dawo ka ɗora min alhakin abinda ba Ni bane da haƙƙin sa - na saurare ka?🙄. Am I playing with you?. Allah da kansa sai da yace "wallahi bazan taɓa gyara muku rayuwa ba har sai ku da kanku kun gyara kawunan ku tukunna". Kana zaune ne fa zaka ga wani mutum ko wani abokin ka wanda kake tunanin yayi karatu daidai gwargwado kuma ya samu tarbiyya daga nagartattun iyaye, amma haka kawai zaka hango shi yana tallata wasu d@bbobin 'yan siy@sa marasa tunani da alƙiblar rayuwar duniya da ta lahira a matsayin waɗanda ya riƙe alƙiblar sa.

Ƙarara fa Ni da kai ko kuma shi ɗin duk munsan mutanen b@nza ne j@hilai marasa tunani kuma f@jirai ta kowacce irin fuska ko a mizanin Allah, amma haka kawai saboda tsabar w@uta da j@hilci tare da zunzurutun talaucin zuciya dana alƙiblar rayuwa sai kaga mutum har rikici ana yi da shi wajen wai dole sai ya nuna maka cewa wane mutumin kirki ne kawai saboda abinda zai samu. Zuciyar sa bata taɓa nuna masa abinda zai biyo baya ga rayuwar 'ya'yan sa, iyayen sa ko al'ummar da zasu biyo baya koda shi ɗin ya tsallake. Don Allah wacce irin rayuwa kake tunanin zamu yi nan gaba idan bamu chanza ba. Kai dai ka sani cewa da ace addu'a ce zata gyara Nigeria ba tare da mun chanza hali ba, ba yadda za'a yi a adalcin ubangiji ya bari mu riski wannan tsawon lokacin ace kullum muna cikin masifa. It's impossible kowanne irin Tauhidi ne da kai kasan ƙarya ne wallahi bazai yiwu ba.

Ni na fahimci inda rayuwa ta ta dosa in sha Allahu. Saboda haka ka fassara wannan rubutun da kowanne irin yare for your earliest convenience.

© Ameer Salihu Koko (RPHP, EMT)

16/09/2025

YAHUDAWA Part 17

16/09/2025

YAHUDAWA Part 16

16/09/2025

YAHUDAWA Part 15

16/09/2025

YAHUDAWA Part 14

16/09/2025

YAHUDAWA Part 13

Address

Arewa Media 24/7
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share