Halacci Online TV -HTV

Halacci Online TV -HTV Hallaci is an online TV which aims is to promote cultural values, commerce, politics and tackle insec

31/01/2026

Jawabin godiya da bangajiya na Ɗan takarar shugabancin jam'iyyar APC ta jihar kano Hon. Dr. Mukhtar Ishaq Yakasai, bisa Ɗaurin Auren 'yar sa da akayi a ranar 30th January

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya isa Abu Dhabi don halartar taron mak**ashiƘarin bayani - https://bbc.in/3YzLYcg
12/01/2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya isa Abu Dhabi don halartar taron mak**ashi

Ƙarin bayani - https://bbc.in/3YzLYcg

Sojoji sun kai hare-hare kan ’yan ta’adda a sassa daban-daban na Jihar Borno, inda s**a kashe wasu, wasu kuma s**a miƙa ...
12/01/2026

Sojoji sun kai hare-hare kan ’yan ta’adda a sassa daban-daban na Jihar Borno, inda s**a kashe wasu, wasu kuma s**a miƙa wuya tare da kwato mak**ai da kayan aiki.

Wannan na cikin sanarwar da Rundunar Operation Hadin Kai ta fitar a ranar Lahadi 11 ga Janairu, 2026.

Sanarwar ta ce matsin lamba da sojoji s**a yi a yankin Azir zuwa Wajiroko ya tilasta wa ’yan ta’adda 11 miƙa wuya tare da bindigogin AK-47 da harsasai, yayin da a wasu samame aka kashe ’yan ta’adda takwas.

Sanarwar ta ƙara da cewa an lalata sansanonin ’yan ta’adda a wasu yankunan jihar, tare da k**a mutane biyu da ake zargi da taimaka musu da kayan aiki a Karamar Hukumar Gubio.

Ƙasar Ethiopia ta fara gina filin jirgin sama mafi girma a Afirka Firaministan Ethiopia, Abiy Ahmed, ya ce ƙasar ta fara...
12/01/2026

Ƙasar Ethiopia ta fara gina filin jirgin sama mafi girma a Afirka

Firaministan Ethiopia, Abiy Ahmed, ya ce ƙasar ta fara gina abin da zai zama filin jirgin sama mafi girma a Afirka.

A wani sakon da ya fitar a kafafen sada zumunta ranar Asabar, firaministan ya ce filin jirgin saman, mai suna Bishoftu International Airport (BIA), za a gina shi a garin Bishoftu a Ethiopia kuma za a kammala aikin a shekarar 2030.

“Domin ci gaba da haɓakar sufurin jiragen sama a Habasha da kuma faɗaɗa cibiyar sadarwar duniya ta Ethiopian Airlines, ana gina wani babban tashar jiragen sama (mega hub) tare da Filin Jirgin Sama na Addis Ababa Bole International Airport, wanda ke kusa da iyakar damar saukar fasinjoji miliyan 25 a kowace shekara,” in ji sanarwar.

“Bishoftu International Airport (BIA) zai zama babban aikin gina filin jirgin sama mafi girma a tarihin Afirka,” in ji shi.

Firaministan ya ce wannan shiri ya yi daidai da sauye-sauyen tattalin arziki na ƙasa, shirin masana’antu, da kuma tsarin dogon lokaci na harkar sufurin jiragen sama a Habasha.

Fubara: Ba na surutu ko korafi, domin Allah yana tare da niGwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya ce ba ya ihu ko k...
12/01/2026

Fubara: Ba na surutu ko korafi, domin Allah yana tare da ni

Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya ce ba ya ihu ko korafi kan halin da ake ciki a jihar, domin ya dogara ga Allah.

Fubara ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi yayin wani taron ibada na haɗin gwiwar coci-coci da aka gudanar a Cocin Anglican na St. Cyprian da ke Port Harcourt domin tunawa da Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026.

Ya yi kira ga al’ummar jihar da su kasance cikin natsuwa, yana mai tabbatar da cewa zaman lafiya zai dawo Rivers.

A cewarsa, dalilin da ya sa ba ya ihu ko korafi shi ne saboda ya san Allah yana tare da shi.

A halin da ake ciki, ‘yan majalisar dokokin Jihar Rivers 26 sun fara dauka matakan tsige gwamnan da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, bisa zargi aikata laifi, inda shugaban majalisar, Martins Amaewhule, ya ce suna barazana ga dimokuraɗiyya.

Halacci online Tv

Ikon Allah: An sanar da rasuwar dattijo mafi tsufa da aka sani a Saudiyya, Nasser bin Radan Al Rashid Al Wadaei, wanda y...
11/01/2026

Ikon Allah: An sanar da rasuwar dattijo mafi tsufa da aka sani a Saudiyya, Nasser bin Radan Al Rashid Al Wadaei, wanda ya kai shekaru 142 a duniya, k**ar yadda jaridar Prime Trust ta ruwaito.

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf, Ya Yaye Ɗalibai 2,260 Tare da Raba Jarin Fara Sana’a da Kayan AikiMai Girma Gw...
11/01/2026

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf, Ya Yaye Ɗalibai 2,260 Tare da Raba Jarin Fara Sana’a da Kayan Aiki

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci bikin yaye ɗalibai dubu biyu da ɗari biyu da sittin (2,260) tare da raba jarin fara sana’a da kayan aiki ga waɗanda s**a kammala karatu daga makarantun koyon sana’o’i mallakin gwamnatin Jihar Kano, a wani muhimmin shiri da ke nuni da ƙudirin gwamnatinsa na ƙarfafa tattalin arziki da bunƙasa rayuwar matasa da mata a faɗin jihar.

Bikin, wanda ya gudana cikin tsari da armashi, ya haɗa da ɗalibai daga sassa daban-daban na Jihar Kano da s**a samu horo a fannoni masu amfani kai tsaye ga kasuwar aiki, k**ar su dinki da ƙera tufafi, aikin wutar lantarki, gyaran mota, walda da ƙera ƙarafa, aikin katako, gyaran sanyi (AC/Refrigeration), gyaran wayoyi da kwamfuta, girke-girke, kwalliya, da sauran sana’o’in zamani da ke taimakawa dogaro da kai.

A jawabinsa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ɗauki ilimin sana’a a matsayin ginshiƙin ci gaban tattalin arziki, inda ya jaddada cewa ba horo kaɗai ake bukata ba, sai an haɗa shi da tallafin jari da kayan aiki, domin bai wa matasa damar fara sana’a kai tsaye ba tare da tangarda ba.

Gwamnan ya ce:

“Manufarmu ita ce mu ba matasa da mata damar dogaro da kai, su zama masu samar da aiki maimakon masu nema. Wannan tallafi da kuke samu yau amanace, ku yi amfani da shi ta hanya mai kyau domin gina makomarku da ta al’umma baki ɗaya.”

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ingantawa da faɗaɗa makarantun koyon sana’o’i, tare da samar da kayan aiki na zamani, ƙwararrun malamai, da ƙarin shirye-shiryen tallafi, domin ƙara yawan masu cin gajiyar wannan muhimmin shiri.

Gwamnan ya shawarci waɗanda aka yaye da su rungumi aiki tukuru, gaskiya, haƙuri da ƙwarewa, tare da gujewa duk wani abu da zai lalata damar da aka ba su, yana mai jaddada cewa su ne ginshiƙan gina Kano mai ƙarfi, wadatuwa da cigaba.

A nasu jawaban, jami’an gwamnati da shugabannin hukumomin da ke kula da makarantun koyon sana’o’i sun yaba da hangen nesa da jajircewar Gwamnan wajen zuba jari a bunƙasar ɗan Adam, inda s**a bayyana cewa shirin zai taimaka matuƙa wajen rage zaman banza, talauci da rashin aikin yi a Jihar Kano.

Masu cin gajiyar shirin sun nuna matuƙar farin ciki da godiya ga gwamnatin Jihar Kano, suna masu cewa horo, kayan aiki da jarin da aka ba su zai zama tushen sauya rayuwarsu, tare da yin alƙawarin amfani da damar wajen bunƙasa sana’o’insu da taimaka wa wasu a cikin al’umma.

Bikin ya ƙare ne da raba takardun shaidar kammala karatu, kayan aiki, da jarin fara sana’a, tare da baje kolin ayyuka da ƙwarewar da ɗaliban s**a samu a tsawon lokacin horo, abin da ya ƙara tabbatar da nasarar wannan gagarumin shiri na gwamnatin Jihar Kano.

NNPP: Ba za mu bari Kwankwaso ya tsaya takara a jam'iyyar mu a 2027 baJam’iyyar NNPP ta ce ba za ta bari Sanata Rabiu Kw...
11/01/2026

NNPP: Ba za mu bari Kwankwaso ya tsaya takara a jam'iyyar mu a 2027 ba

Jam’iyyar NNPP ta ce ba za ta bari Sanata Rabiu Kwankwaso ya nemi tikitin shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027 ba.

Sakataren Ƙ jam’iyyar na ƙasa, Ogini Olaposi, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Legas, inda ya ce tikitin 2027 a buɗe yake ga dukkan sahihan mambobin jam’iyyar.

Olaposi ya ce an hana Kwankwaso sake tsayawa takara ne sak**akon sabanin da ya shiga da NNPP da kuma ƙungiyar Kwankwasiya , tare da bayyana cewa yarjejeniyar da aka kulla tsakanin jam’iyyar da ƙungiyar ta ƙare bayan zaɓen 2023.

Ya ƙara da cewa an kori Kwankwaso da wasu jagororin Kwankwasiya saboda ayyukan cin amanar jam’iyya, kuma har yanzu ba a janye hukuncin ba.

Ya ce NNPP tana maraba da masu niyyar tsayawa takara da haɗin gwiwa da sauran jam’iyyun siyasa masu irin akida ɗaya, inda ya jaddada cewa shugabancin NNPP ne kaɗai ke da ikon yanke duk wani hukunci kan haɗin gwiwa a 2027.

22/12/2025

Jawabin mai tsawatar wa marasa runjaye a zauren majalisar dokokin jihar kano, RT. Hon. Ayuba Labaran Durum, wakilin ƙaramar hukumar Kabo a zauren majalisar dokokin jihar kano, a wajan taron kwamatin yakin neman zaben shugabancin jam'iyyar APC ta jihar kano, na Mukhtar Ishaq Yakasai.

Dakarun sojojin Najeriya sun kashe kasurgumin shugaban ƴanbindiga a Benue Dakarun Forward Operating Base (FOB) Wukari, k...
22/12/2025

Dakarun sojojin Najeriya sun kashe kasurgumin shugaban ƴanbindiga a Benue

Dakarun Forward Operating Base (FOB) Wukari, karkashin birgediya ta 6 ta rundunar sojin Najeriya/Sashe na 3 na Operation Whirl Stroke (OPWS), sun k**a wani kasurgumin shugaban ‘yan fashi a Karamar hukumar Ukum ta Jihar Benue.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, Laftanar Umar Muhammad, Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulda da Jama’a na rundunar sojin ya bayyana k**a mutumin a matsayin gagarumin nasara a ayyukan sojin.

A cewarsa, k**a wannan fitaccen shugaban ‘yan fashi da ke da alhakin sace-sacen mutane da kuma fashin makami da dama a kan hanyar Benue zuwa Taraba, babbar nasara ce a ayyukan rundunar.

Sanarwar ta ce,
“An gudanar da kamen ne a ranar 22 ga Disamba, 2025, yayin wani aiki na musamman da aka tsara bisa bayanan sirri a al’ummar Vaase, Karamar hukumar Ukum ta Jihar Benue.

“Aikin ya kai ga k**a Fidelis Gayama, wani babban wanda ake zargi da hukumomin tsaro ke nema tun da dadewa.”

Ya kara da cewa binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin yana da alaka ta kut-da-kut da Aka Dogo, wani shugaban kungiyar ‘yan bindiga da ake nema ruwa a jallo.

“Yanzu haka wanda ake zargin yana hannun rundunar soji, kuma za a mika shi ga hukuma da ta dace domin cikakken bincike da gurfanarwa bisa dokokin da ke aiki,” in ji sanarwar.

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa Shugaban K...
22/12/2025

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa

Shugaban Kwamitin fadar shugaban kasa kan Sauye-sauyen Haraji, Taiwo Oyedele, ya gargaɗi cewa jinkirta aiwatar da sabbin dokokin haraji bayan 1 ga Janairu, 2026, zai ƙara nauyin haraji ga ma’aikata da ’yan kasuwa a Najeriya.

Oyedele ya ce kashi 98 cikin 100 na ma’aikata za su ci gaba da fuskantar haraji iri-iri, yayin da ’yan kasuwa za su rasa rangwamen da sabbin dokokin s**a tanada.

Ya bayyana haka ne a shirin The Morning Brief na gidan talabijin na Channels .

Gargaɗin nasa na zuwa ne a lokacin da ake ta ce-ce-ku-ce kan zargin cewa dokokin da aka fitar a gazette ba su yi daidai da waɗanda majalisar tarayya ta amince da su ba.

Wasu ’yan siyasa da ƙungiyoyin fararen hula sun yi kira da a dakatar da aiwatar da dokokin.

Sai dai Oyedele ya ce maimakon dakatarwa, ya k**ata a aiwatar da dokokin k**ar yadda majalisar tarayya ta amince da su, tare da gyara duk wani kuskure da aka gano daga baya.

Dokokin sauye-sauyen haraji guda huɗu da shugaba Bola Tinubu ya rattaba wa hannu ana sa ran za su fara aiki daga 1 ga Janairu, 2026, domin sauƙaƙa tsarin biyan haraji, faɗaɗa tushen haraji da inganta tara kuɗaɗen shiga a ƙasar.

Dangote ya zargi Shugaban hukumar NMDPRA da cin hanciAliko Dangote, shugaban masana'antun Dangote , ya zargi Shugaban Hu...
15/12/2025

Dangote ya zargi Shugaban hukumar NMDPRA da cin hanci

Aliko Dangote, shugaban masana'antun Dangote , ya zargi Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta (NMDPRA), Farouk Ahmed, da cin hanci, yana mai cewa ya biya dala miliyan 5 a matsayin kuɗin makarantar sakandare ga ’ya’yansa huɗu a ƙasar Switzerland.

Dangote ya yi zargin ne a yayin wani taron manema labarai a Matatar Dangote a ranar Lahadi, inda ya ce irin wannan kashe kuɗi ya wuce ƙarfin albashin shugaban hukumar, tare da kira ga gwamnatin tarayya da ta binciki lamarin.

Attajirin ya ce ya dace a ba Ahmed damar wanke kansa ta hanyar bincike, ba tare da korar sa ba, amma ya yi barazanar ɗaukar matakin shari’a kan makarantun Switzerland idan s**a musanta zargin.

A wani bangaren kuma, Dangote ya bayyana cewa farashin man fetur zai ragu zuwa kusan naira 740 kowace lita a Lagos daga ranar Talata, bayan da matatar tasa ta rage farashin zuwa naira 699.

Ya ce tashoshin MRS ne za su fara nuna sabon farashin, yana mai jaddada cewa tace man fetur a cikin gida zai amfani ’yan Najeriya duk da asarar da masu shigo da mai za su fuskanta.

Address

103 Sky Complex
Kano
9333

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Halacci Online TV -HTV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category