11/01/2026
Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf, Ya Yaye Ɗalibai 2,260 Tare da Raba Jarin Fara Sana’a da Kayan Aiki
Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci bikin yaye ɗalibai dubu biyu da ɗari biyu da sittin (2,260) tare da raba jarin fara sana’a da kayan aiki ga waɗanda s**a kammala karatu daga makarantun koyon sana’o’i mallakin gwamnatin Jihar Kano, a wani muhimmin shiri da ke nuni da ƙudirin gwamnatinsa na ƙarfafa tattalin arziki da bunƙasa rayuwar matasa da mata a faɗin jihar.
Bikin, wanda ya gudana cikin tsari da armashi, ya haɗa da ɗalibai daga sassa daban-daban na Jihar Kano da s**a samu horo a fannoni masu amfani kai tsaye ga kasuwar aiki, k**ar su dinki da ƙera tufafi, aikin wutar lantarki, gyaran mota, walda da ƙera ƙarafa, aikin katako, gyaran sanyi (AC/Refrigeration), gyaran wayoyi da kwamfuta, girke-girke, kwalliya, da sauran sana’o’in zamani da ke taimakawa dogaro da kai.
A jawabinsa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ɗauki ilimin sana’a a matsayin ginshiƙin ci gaban tattalin arziki, inda ya jaddada cewa ba horo kaɗai ake bukata ba, sai an haɗa shi da tallafin jari da kayan aiki, domin bai wa matasa damar fara sana’a kai tsaye ba tare da tangarda ba.
Gwamnan ya ce:
“Manufarmu ita ce mu ba matasa da mata damar dogaro da kai, su zama masu samar da aiki maimakon masu nema. Wannan tallafi da kuke samu yau amanace, ku yi amfani da shi ta hanya mai kyau domin gina makomarku da ta al’umma baki ɗaya.”
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ingantawa da faɗaɗa makarantun koyon sana’o’i, tare da samar da kayan aiki na zamani, ƙwararrun malamai, da ƙarin shirye-shiryen tallafi, domin ƙara yawan masu cin gajiyar wannan muhimmin shiri.
Gwamnan ya shawarci waɗanda aka yaye da su rungumi aiki tukuru, gaskiya, haƙuri da ƙwarewa, tare da gujewa duk wani abu da zai lalata damar da aka ba su, yana mai jaddada cewa su ne ginshiƙan gina Kano mai ƙarfi, wadatuwa da cigaba.
A nasu jawaban, jami’an gwamnati da shugabannin hukumomin da ke kula da makarantun koyon sana’o’i sun yaba da hangen nesa da jajircewar Gwamnan wajen zuba jari a bunƙasar ɗan Adam, inda s**a bayyana cewa shirin zai taimaka matuƙa wajen rage zaman banza, talauci da rashin aikin yi a Jihar Kano.
Masu cin gajiyar shirin sun nuna matuƙar farin ciki da godiya ga gwamnatin Jihar Kano, suna masu cewa horo, kayan aiki da jarin da aka ba su zai zama tushen sauya rayuwarsu, tare da yin alƙawarin amfani da damar wajen bunƙasa sana’o’insu da taimaka wa wasu a cikin al’umma.
Bikin ya ƙare ne da raba takardun shaidar kammala karatu, kayan aiki, da jarin fara sana’a, tare da baje kolin ayyuka da ƙwarewar da ɗaliban s**a samu a tsawon lokacin horo, abin da ya ƙara tabbatar da nasarar wannan gagarumin shiri na gwamnatin Jihar Kano.