25/08/2025
Da Dumi-dumi:
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da kwamitin shirya bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai
Gwamnatin Jihar Kano, ta hannun Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, ta kaddamar da kwamitin shirya bikin zagayowar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai.
An gudanar da bikin kaddamarwar ne a dakin taro na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, inda manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban s**a halarta.
A yayin jawabin sa, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bukaci mambobin kwamitin da su gudanar da aikinsu cikin gaskiya, jajircewa da kishin ƙasa. Ya jaddada cewa bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai ba kawai biki ba ne na murna, har ma dama ce ta tunawa da tarihin ƙasa, haɗin kai da ci gaba.
Kwamishinan ya kara da cewa dole ne a tsara bukukuwan cikin salon da zai haɗa kowa da kowa, tare da nuna bambancin al’adu, nasarori da burukan Najeriya. Ya kuma tabbatar wa da kwamitin cewa ma’aikatarsa za ta bayar da cikakken goyon baya domin ganin an samu nasara.
A nasa jawabin, shugaban kwamitin kuma mukaddashin sakatare ɗin dindindin na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Alhaji Inuwa Idris Yakasai, ya gode wa Gwamnatin Jihar Kano da ma’aikatar bisa amincewa da su. Ya yi alkawarin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru domin tabbatar da shiryayyen biki mai ɗaukar hankali, wanda zai fito da ruhin haɗin kai da ƙaunar ƙasa.
Bikin kaddamarwar ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, daraktoci daga ma’aikatun gwamnati, da kuma wakilan rundunonin tsaro irin su Sojoji, ’Yan sanda, Civil Defence, Hukumar Shige da Fice, da ƙungiyoyin fararen hula.