
13/07/2025
Kar ku zagi matattu…” – wannan umarni ne daga Annabi Muhammad (SAW) domin kare mutuncin mamaci. Matattu sun riga sun koma ga Allah, inda za a biya su bisa ayyukansu. Zagin su ba zai canza komai ba, illa ƙara zunubi ga mai zagi. Maimakon haka, mu rika yin addu’a a gare su, ko mu yi shiru idan ba za mu iya fadin alheri ba. Tsarkake harshe daga zagin mamaci na daga cikin ladabi da tausayi, kuma yana nuna tsoron Allah.
Copied