Vision FM Kano

Vision FM Kano VISION FM KANO 92.5
SAMAR MUKU DA SAHIHAN LABARAI A KODA YAUSHE SHINE MURADIN MU. MIKIYA MAI HANGEN NESA
(5)

Zaku kasance tare da Hafsah Saminu Ahmad Walwala a zango na farko na yada shirye-shiryen Vision FM Kano 92.5 Lambar da z...
16/10/2025

Zaku kasance tare da Hafsah Saminu Ahmad Walwala a zango na farko na yada shirye-shiryen Vision FM Kano 92.5

Lambar da zaku turo mana da sako a manhajar WhatsApp itace 09067680000

゚viralシfypシ゚viralシalシ

Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta taya Malam Abubakar Balarabe Kofar Naisa murna bisa...
15/10/2025

Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta taya Malam Abubakar Balarabe Kofar Naisa murna bisa naɗin sa a matsayin Babban Manaja na tashar Guarantee Radio 94.7 FM Kano. Wannan naɗi dai ya nuna girmamawa da yabo ga jajircewa da ƙwarewa da kuma muhimmiyar gudunmawar da Kofar Naisa ya bayar wajen ci gaban kafafen yada labarai a jihar Kano da ƙasar baki ɗaya.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa Malam Kofar Naisa ya dade yana taka muhimmiyar rawa a fagen yada labarai, tare da nuna gaskiya, kishin al’umma da jajircewa wajen samar da ingantaccen bayani ga jama’a. Ta ce tana da cikakken tabbacin cewa sabon babban manajan zai kawo sabbin dabaru da jagoranci mai inganci wajen tafiyar da harkokin tashar, bisa manufa ta ingantaccen yada labarai da gaskiya a Kano.

A madadin gwamnatin jihar, Ma’aikatar Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida ta bukaci Kofar Naisa da ya ci gaba da rike ka’idar sana’a da ingantaccen aiki, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa ci gaban harkar yada labarai domin karfafa gaskiya, nagartaccen mulki da kuma hadin kan al’umma.

Gwamnan Bayelsa Douye Diri ya bayyana haka ne ranar Laraba a gidan gwamnatin jihar da ke birnin Yenagoa lokacin taron ma...
15/10/2025

Gwamnan Bayelsa Douye Diri ya bayyana haka ne ranar Laraba a gidan gwamnatin jihar da ke birnin Yenagoa lokacin taron majalisar zartarwar jihar.

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan ficewar Gwamnan Jihar Enugu Peter Mbah daga PDP zuwa APC.

Me kuke ganin yana saka gwamnonin adawa sauya sheka zuwa Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya? ⤵️⤵️⤵️

Hukumar Kula da gidan ajiya da gyaran hali na Jihar Kano, ta bayyana cewa, dalilan tsaro ne yasa ta  komar da Malam Abdu...
15/10/2025

Hukumar Kula da gidan ajiya da gyaran hali na Jihar Kano, ta bayyana cewa, dalilan tsaro ne yasa ta komar da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa gidan gyaran hali dake kuje Abuja .

Hukumar Kula da gidan ajiya da Gyaran Hali ta Najeriya reshen Jihar Kano, ta bayyana cewa komar da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa gidan gyaran hali dake kuje Abuja dokar hukumar ta 2019 ta tanadi hakan

Hukumar ta ce wannan mataki an dauke shi ne bisa dalilai na tsaro

Hukumar ta kuma tabbatar wa jama’a cewa walwala da hakkokin Malam Abduljabbar na tnan daram, kuma wannan sauyi bai shafi shari’arsa ko damar tuntuɓar lauyoyinsa ba.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Kano, CSC Musbahu Lawan Kofar Nassarawa ne yabayyana haka a zantawarsa da Nazifi Bala Dukawa hukumar tana cigaba da aiwatar da aikinta na tsarewa da kula da tarbiyar a gidan gyara Hali.

Ƴan uwa da magoya bayan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara wanda ke tsare a gidan yarin Kurmawa na Kano bisa tuhumar "ɓata...
15/10/2025

Ƴan uwa da magoya bayan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara wanda ke tsare a gidan yarin Kurmawa na Kano bisa tuhumar "ɓatanci" ga Annabi Muhammadu SAW, tuhumar da Malamin ya musanta kuma yake ƙoƙarin ɗaukaka ƙara, sun shiga ruɗani saboda rashin sanin halin da malamin ke ciki a yanzu haka.

Mabiya da iyalan Malamin dai sun shiga ruɗun a ranar Talata bayan da s**a kai masa ziyara a gidan yarin amma sai s**a tarar ba ya nan kuma ba su samu wata gamsasshiyar amsa ba daga jami'an gidan kason.

゚viralシfypシ゚viralシalシ

Zaku kasance tare da Hafiz Khalid Sharada a zango na farko na yada shirye-shiryen Vision FM Kano 92.5 Lambar da zaku tur...
15/10/2025

Zaku kasance tare da Hafiz Khalid Sharada a zango na farko na yada shirye-shiryen Vision FM Kano 92.5

Lambar da zaku turo mana da sako a manhajar WhatsApp itace 09067680000

゚viralシfypシ゚viralシalシ

Zargin alkalanci mara kyau a gasar kwararru ta Najeriya NPFL:Kwamitin Alkalan wasa na hukumar kwallon kafa ta kasa NFF y...
15/10/2025

Zargin alkalanci mara kyau a gasar kwararru ta Najeriya NPFL:

Kwamitin Alkalan wasa na hukumar kwallon kafa ta kasa NFF ya dakatar da Alkalan wasa Guda Uku da s**a yi Alkalancin wasa na a mako na 8 na gasar firimiyar NPFL ta Najeriya sakamakon busa ta son rai wato fasha da ta sabawa ka'idojin kwallon kafa.

Ta cikin sanarwar da sakataren kwamitin Aminu Muhammad, ya sakawa hannu aka rabawa manema labarai , NFF ta dakatar da Mohammed B Tuta Dan asalin jihar Adamawa da Mataimakin sa Ben Japhet na jihar Benue, sakamakon yadda s**a gudanar da wasan Kano Pillars da Shooting Stars.

Ya yinda a bangare daya hukumar ta ladabtar da Ikechukwu Taiwo dan asalin jihar Rivers da ya Jagoranci wasan Nassarawa United da Enugu Rangers , sakamakon bada bugun daga kai sai mai tsaron gida na bogi da bai cancanta ba.

Sanarwar ta kara dacewa dukkanin Alkalan wasan an dakatar da su har sai abinda Hali ya yi.

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya halarci zaman majalisar wakilan tarayya a ranar Talata domin shaida yadda wasu ‘yan m...
14/10/2025

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya halarci zaman majalisar wakilan tarayya a ranar Talata domin shaida yadda wasu ‘yan majalisar jam’iyyar PDP uku s**a koma jam’iyyar APC. Wadanda s**a sauya sheka su ne Abdulkarim Hussain Mohammed, Aliyu Mustapha Abdullahi da Sadiq Ango Abdullahi. Kakakin majalisar, Abbas Tajudeen, ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar.

Majalisar ta dakatar da wasu ayyuka nata domin ba gwamnan damar halartar zaman, inda daga bisani ya jagoranci sabbin ‘yan jam’iyyar APC wajen gaisawa da kakakin majalisar tare da daukar hoto. Wannan lamari ya ja hankalin ‘yan majalisar da dama da ke cikin zauren.

Sai dai jagoran ‘yan adawa a majalisar, Kingsley Chinda, ya soki wannan sauya sheka, yana mai bukatar kakakin majalisar ya bayyana kujerun mutanen a matsayin babu mai rike da su bisa tanadin sashe na 68 na kundin tsarin mulkin kasa.

"Muna kira ga shugaban jam'iyyar APC na Karamar Hukumar Tarauni daya fito ya janye kalaman da yayi, domin yin hakan ya s...
14/10/2025

"Muna kira ga shugaban jam'iyyar APC na Karamar Hukumar Tarauni daya fito ya janye kalaman da yayi, domin yin hakan ya sabawa tsarin dimukuradiyya.

Hon. Hamisu Sunusi Babannan
Dan Jam'iyyar APCn Tarauni

゚viralシfypシ゚viralシalシ

Majalisar Dokoki ta ƙasa ta gabatar da sabon shirin sauya lokacin gudanar da zaɓen da za'ayi nan gaba na ƙasa zuwa watan...
14/10/2025

Majalisar Dokoki ta ƙasa ta gabatar da sabon shirin sauya lokacin gudanar da zaɓen da za'ayi nan gaba na ƙasa zuwa watan Nuwamba 2026, watanni shida kafin lokacin da aka saba gudanar da zaɓe a watan Fabrairu. Wannan na cikin sabon kudirin dokar zaɓe ta 2025 da aka gabatar a zaman sauraron ra’ayoyin jama’a a Abuja.

Sabon kudirin na neman tabbatar da cewa an kammala dukkan shari’o’in zaɓe kafin ranar rantsar da sabbin shugabanni a ranar 29 ga Mayu, 2027. Ya kuma tanadi wasu muhimman sauye-sauye kamar yin amfani da NIN wajen rajistar masu zaɓe, bai wa ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje damar yin zaɓe da wuri, da kuma tabbatar da amfani da fasahar BVAS wajen tantance masu kaɗa ƙuri’a.

Idan aka amince da kudirin, zaɓukan shugaban ƙasa da na gwamnoni za su fara gudana a watan Nuwamba 2026. Majalisar ta kuma ba da shawarar a cire tilasta amfani da katin zabe PVC, domin tsarin na'urar BVAS bata amfani da microchip ɗinta. Haka kuma, jam’iyyun siyasa za su rika mika sunayen ‘yan takararsu watanni bakwai kafin zaɓe domin ƙara ingancin tsarin.

13/10/2025

"San zuciyar da akeyi a siyasar karamar hukumar Tarauni yayi yawa shiyasa dole mu fito mu goyawa gaskiya baya, babu dan takarar daya kai Hon. M. Nasir Ja'oji cancanta a Tarauni.....

Nasiru Dan Malam
Dan Jam'iyyar APCn Kano

゚viralシfypシ゚viralシalシ

13/10/2025

An kammala zaman Tattaunaa da Malam Lawal Abubakar Triumph da kwamitin Shura.

An dauki lokaci ana tattaunawa inda 'yan kwamitin na Shura s**a yiwa Malamin tambayoyi bayan kunna karatuttukansa da ake zargin akwai sabo a ciki.

A karshe Malam ya kare kansa kuma ya karbi nasihohin kyautata harshe yayin wa'azi tare da cewar kofar sa a bude take dan karbar shawarwari.

Address

Guda Abdullahi
Kano
700101

Website

http://stream.zeno.fm/5510fz5kkzzuv

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Vision FM Kano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share