Vision FM Kano

Vision FM Kano VISION FM KANO 92.5
SAMAR MUKU DA SAHIHAN LABARAI A KODA YAUSHE SHINE MURADIN MU. MIKIYA MAI HANGEN NESA
(4)

Tsohuwar Ministar Harkokin Jin-ƙai da Ci Gaban Jama'a, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta roƙi Babbar Kotun Abuja da ta soke ...
08/06/2026

Tsohuwar Ministar Harkokin Jin-ƙai da Ci Gaban Jama'a, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta roƙi Babbar Kotun Abuja da ta soke sammacin k**a ta da aka bayar a kanta.

A zaman kotun da aka gudanar yau Litinin, Sadiya Farouq ba ta halarta ba, yayin da sauran waɗanda ake tuhuma tare da ita s**a bayyana a gaban kotun. Lauyan ta ya bayyana cewa rashin lafiyarta ne ya hana ta zuwa kotun.

Sai dai lauyan hukumar EFCC ya yi adawa da sauraron buƙatar, yana mai cewa ba za a iya sauraron ta ba kafin a gurfanar da wadda ake tuhuma. Duk da haka, kotun ta amince a saurari ƙorafin nata.

Lauyan Sadiya Farouq ya roƙi kotun da ta soke sammacin k**a ta, yayin da lauyan EFCC ya buƙaci kotun ta yi watsi da buƙatar tare da ƙin amincewa da takardun shaidar rashin lafiyar da aka gabatar.

Bayan sauraron ɓangarorin biyu, Mai Shari’a Jude Onwuegbuzie ya ɗage shari’ar zuwa ranar 10 ga watan Yuni domin yanke hukunci kan buƙatar da aka gabatar.

Wani sabon rikici ya kunno kai tsakanin bangaren Kwankwasiyya ƙarƙashin jagorancin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Jam'iy...
08/06/2026

Wani sabon rikici ya kunno kai tsakanin bangaren Kwankwasiyya ƙarƙashin jagorancin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Jam'iyyar NDC kan batun rabon tikitin takara a Jihar Kano.

‎Rahotanni sun nuna cewa jam'iyyar NDC ta sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar da bangaren Kwankwasiyya ya gabatar domin tsayawa takara a zaɓukan shekarar 2027.

‎A cewar wata takarda da shugaban jam'iyyar NDC na Kano, Honarabul Hussaini Isah Mairiga, ya sanya wa hannu, an bayyana cewa matakin ya biyo bayan yarjejeniyar rabon tikitin takara da aka cimma tsakanin bangaren Kwankwasiyya da shugabancin jam'iyyar.

‎Yarjejeniyar dai ta tanadi cewa bangaren Kwankwasiyya zai samu kaso 60 cikin 100 na tikitin takara, yayin da bangaren jam'iyyar da aka tarar zai samu kaso 40 cikin 100.

‎Sai dai bayanan da ke fitowa sun nuna cewa bangaren jam'iyyar na zargin cewa ba a ba shi kujerun da s**a dace da kason da aka amince da shi ba, lamarin da ya haifar da rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu.

‎A sak**akon haka, shugabancin NDC a Kano ya amince da sauya wasu daga cikin sunayen 'yan takarar Majalisar Tarayya da ta Jiha domin tabbatar da abin da ta kira adalci wajen aiwatar da yarjejeniyar.

‎A gefe guda kuma, wasu majiyoyi sun bayyana cewa bangaren Kwankwasiyya bai gamsu da matakin da jam'iyyar ta ɗauka ba. Rahotanni sun ce ana ci gaba da tattaunawa kan makomar haɗin gwiwar, yayin da ake hasashen yiwuwar ɗaukar wasu matakai na siyasa idan ba a samu maslaha tsakanin ɓangarorin ba.

‎Masana harkokin siyasa na ganin cewa wannan rikici na iya yin tasiri ga yanayin siyasar Kano da kuma shirye-shiryen zaɓen 2027, musamman idan aka kasa warware saɓanin da ke tsakanin ɓangarorin cikin lokaci.

‎Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da ke tabbatar da rahotannin da ke yawo kan yiwuwar sauya jam'iyya.

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa na kawo ƙarshen matsalar tsaro tare da tabbatar da ...
08/06/2026

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa na kawo ƙarshen matsalar tsaro tare da tabbatar da ceto duk mutanen da ke hannun masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka a faɗin Najeriya.

‎Shugaban ƙasar ya kuma bai wa 'yan Najeriya tabbacin cewa gwamnatin tarayya za ta ƙara ƙaimi wajen rage matsin tattalin arziki da tsadar rayuwar da jama'a ke fuskanta.

‎Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, wanda ya wakilce shi a taron addu'ar haɗin gwiwa na majami'u da aka gudanar a Babban Cocin Ƙasa da ke Abuja domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2026.

‎A cikin saƙon da aka karanta a madadinsa, shugaban ƙasar ya taya 'yan Najeriya murnar cika shekaru 27 na mulkin dimokuraɗiyya ba tare da katsewa ba tun daga shekarar 1999.

‎Ya bayyana wannan nasara a matsayin wata shaida ta juriya, sadaukarwa da kuma ƙoƙarin al'ummar Najeriya wajen tabbatar da dorewar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.

‎Shugaban ya kuma yi kira ga 'yan ƙasa da su ci gaba da bai wa gwamnati haɗin kai domin cimma manufofin ci gaba, tsaro da bunƙasa tattalin arziki.

Rahotanni daga Abuja sun bayyana cewa an hana tsohon mataimakin gwamnan Jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, da Aminu Abduss...
08/06/2026

Rahotanni daga Abuja sun bayyana cewa an hana tsohon mataimakin gwamnan Jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, da Aminu Abdussalam shiga gidan jagoran jam'iyyar NDC na ƙasa, Sanata Seriake Dickson.

A cewar rahoton da Premier Radio ta wallafa, lamarin ya faru ne a daren Lahadi lokacin da wakilan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso s**a isa gidan Seriake Dickson domin tattaunawa kan rikicin da ya kunno kai dangane da rabon tikitin takara a Jihar Kano.

Wata majiya daga gidan shugaban jam'iyyar ta ce an sanar da tawagar cewa Sanata Seriake Dickson ya bayar da umarnin kada a bari su shiga gidan a lokacin, saboda ba ya son gudanar da ganawar.

Rahotannin sun ce wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama tsakanin bangaren Kwankwasiyya da kuma bangaren tsohuwar NDC kan yadda za a raba tikitin takara a Kano.

Tun da farko dai an ce an cimma yarjejeniya ta rabon kujeru da tikitin takara a tsarin kashi 60 cikin 100 ga bangaren Kwankwasiyya da kuma kashi 40 cikin 100 ga bangaren NDC. Sai dai sabbin bayanai na nuna cewa rikici ya kunno kai kan yadda aka aiwatar da wannan yarjejeniya.

‎Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ko kuma shugabancin jam'iyyar NDC ta ƙasa da ke tabbatarwa ko musanta rahoton.

BUƊAƊƊIYAR WASIƘA ZUWA GA SANATA BARAU JIBRIN (MALIYA)Daga: Comrade Murtala Mohammed KanoAssalamu Alaikum,Da farko, ina ...
08/06/2026

BUƊAƊƊIYAR WASIƘA ZUWA GA SANATA BARAU JIBRIN (MALIYA)

Daga: Comrade Murtala Mohammed Kano

Assalamu Alaikum,

Da farko, ina fatan kana cikin koshin lafiya tare da alkhairi, kai da dukkan masoyanka na gaskiya, ba na gani-ka-so ba.

A tafiyata ta siyasa, a baya na kasance mai bin jam’iyya ne ba mutum ba. Amma a yanzu, ina goyon bayan nagartattun mutane a duk jam’iyyar da suke. Wannan ne ya sa ban amince da karɓar wasu muƙamai da aka taɓa yi min tayin su a jam’iyyun ADC, SDP da APC ba. A ganina, muddin mutum cikakken ɗan jam’iyya ne, wajibi ne ya mara baya ga duk wanda jam’iyyarsa ta tsayar ko ta ba shugabanci.

Ina daga cikin magoya bayan Alhaji Atiku Abubakar, Wazirin Adamawa, kuma an san ni a kafafen sada zumunta da kafafen yaɗa labarai kan wannan matsayi na. Ba na ɓoye ra’ayina a rayuwa.

Saƙon da nake son isarwa ga Sanata Barau a nan shi ne:

Kana da masaniya cewa akwai mutanen da ka samar wa ayyuka da kuma waɗanda ka ba muƙamai na siyasa, k**ar masu ba da shawara (SA, SSA, SLA da sauransu), waɗanda mafi yawansu ba sa taimaka maka ta kowace hanya.

Shin an samar musu aikin ne kawai domin su zauna suna karɓar albashi ko alawus a ƙarshen kowane wata?

Shin soyayya da goyon bayan mutum yana nufin kada a nuna hakan a zahiri? Idan aka taɓo mutuncin mutum a kafafen sada zumunta ko na yaɗa labarai, ya dace mabiyansa su tsaya su kare shi da ayyukansa.

A taƙaice, menene amfanin mutanen da aka ɗauka aiki ko aka ba muƙamai idan ba sa taka wata muhimmiyar rawa wajen kare martabar wanda ya ba su wannan dama?

Bincike ya nuna cewa ba a taɓa samun Sanata ko ɗan majalisar da ya taimaki al’ummarsa da yawa k**ar Sanata Barau Jibrin ba. Wanda ke biye masa a wannan fanni shi ne Hon. Aminu Sulaiman Goro.

Abin takaici shi ne, duk da irin taimakon da waɗannan mutane s**a yi wa jama’a, sau da yawa ba sa samun goyon baya daga yawancin waɗanda s**a amfana da su.

A duk lokacin da aka taɓo lamarin Sanata Barau, mutane kaɗan ne ake gani suna tsayawa domin kare shi ko bayyana ayyukan alkhairinsa. Daga cikin waɗanda ake yawan gani akwai:

Comrade Kabiru Ado Laƙwaya

Hon. Hafizu Alfindiƙi

Hon. Malami Abubakar Dala

Malam Jamilu Ɗan Kuda

Ina ba ka shawarar ka gudanar da bincike domin za ka tabbatar da cewa waɗannan mutane na daga cikin waɗanda suke tsayawa tsayin daka wajen kare martabarka da bayyana ayyukanka.

Shawarata gare ka ita ce ka sake duba mutanen da ke kewaye da kai. Duk wanda ba ya kawo wata gudummawa ta zahiri wajen kare mutuncinka ko tallata ayyukanka, ya k**ata a sake nazarin matsayinsa. Wani lokaci rashin anfani daga wasu na iya zama k**ar babu su kwata-kwata.

A siyasa, sakayya da biyayya suna da muhimmanci. Idan mutum ba zai iya tsayawa tare da kai a lokacin da ake buƙatarsa ba, to ya k**ata a tambayi kanka irin amfanin da yake da shi a gare ka.

Na gode.

Comrade Murtala Mohammed Kano

‎Jam'iyyar NDC a Jihar Kano ta sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar da bangaren Kwankwasiyya ya gabatar mata, a wa...
08/06/2026

‎Jam'iyyar NDC a Jihar Kano ta sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar da bangaren Kwankwasiyya ya gabatar mata, a wani mataki da ta ce ya biyo bayan yarjejeniyar rabon tikitin takara da aka cimma tsakanin bangarorin biyu.

‎A wata takarda da shugaban jam'iyyar na Kano, Honarabul Hussaini Isah Mairiga, ya sanya wa hannu, an bayyana sababbin sunayen 'yan takarar da za su wakilci jam'iyyar a wasu mazabu na Majalisar Tarayya da ta Jiha.

‎Daga cikin wadanda aka amince da su akwai Barrista Isma'il Idris Sani a Kumbotso, Nasiru Ali Ahmed a Nassarawa, Kabiru Ishaq Sa'id a Kano Municipal, Barrista Ɗayyabu Jamilu Ibrahim a Doguwa da Tudunwada, Muhammad Hamisu Abubakar a Dawakin Tofa da Rimin Gado da Tofa, Ibrahim Bashir Bango a Sumaila da Takai, sai kuma Abdulmajid Isa Umar Mairigar Fata a Gwale.

‎Haka kuma rahotanni sun nuna cewa an yi sauye-sauye a wasu tikitin takarar Majalisar Jiha da s**a haɗa da mazabun Dala, Tarauni, Kumbotso, Ungogo da Dawakin Kudu.

‎Jam'iyyar ta ce tun farko an cimma yarjejeniya da jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, cewa bangaren Kwankwasiyya zai samu kaso 60 cikin ɗari na muk**ai da tikitin takara, yayin da jam'iyyar za ta samu kaso 40 cikin ɗari.

‎Sai dai bayanan da ke fitowa sun nuna cewa wannan yarjejeniya ce ta jawo sabani, bayan da ake zargin bangaren jam'iyyar bai samu kujerun da aka yi masa alƙawari ba, lamarin da ya sa ta ɗauki matakin tabbatar da nata kason.



Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Allah ya yi wa Usman Sani Jibo rasuwa jiya Asabar.Inda aka gudanar da jana’izarsa y...
07/06/2026

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Allah ya yi wa Usman Sani Jibo rasuwa jiya Asabar.

Inda aka gudanar da jana’izarsa yau Lahadi a unguwar Tukuntawa, Gidan Rediyo, Layin Gidan Kallon Abdulaziz.

Allah Ya gafarta masa, Ya jiƙansa da rahama, Ya sanya Aljanna Firdausi ce makomarsa. Ameen.

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta girke fitilun hasken rana guda 12,050 a sassa daban-daban na birnin Kano cikin s...
07/06/2026

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta girke fitilun hasken rana guda 12,050 a sassa daban-daban na birnin Kano cikin shekaru uku da s**a gabata. Kwamishinan Ayyuka, Injiniya Marwan Ahmad, ya ce an aiwatar da aikin ne domin inganta tsaro, sauƙaƙa zirga-zirga da kuma bunƙasa harkokin kasuwanci musamman da daddare.

‎A cewarsa, an girke fitilun ne a manyan tituna da muhimman wurare a faɗin birnin, a wani ɓangare na shirin gwamnatin jihar na sabunta ababen more rayuwa ta hanyar amfani da mak**ashi mai ɗorewa da kare muhalli. Ya ce hakan ya taimaka wajen rage dogaro da hanyoyin samar da wutar lantarki na gargajiya tare da rage kuɗaɗen kula da kayayyakin gwamnati.

‎Kwamishinan ya ƙara da cewa aikin ya sauya yanayin birnin Kano da daddare, inda ya ƙara tsaro ga mazauna gari da masu ababen hawa tare da samar da yanayi mai kyau ga kasuwanci. Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da kula da fitilun tare da faɗaɗa irin waɗannan ayyuka zuwa sauran sassan jihar.

Tsohon Manjo Janar Abubakar Rabe da matarsa, Hajiya Amina Abubakar, sun roƙi gwamnati da shugabannin al’umma su taimaka ...
07/06/2026

Tsohon Manjo Janar Abubakar Rabe da matarsa, Hajiya Amina Abubakar, sun roƙi gwamnati da shugabannin al’umma su taimaka wajen tabbatar da an kuɓutar da su bayan sun shafe mako guda a hannun masu garkuwa da su a Jihar Katsina. Sun bayyana hakan ne a cikin wani bidiyo da masu garkuwar s**a fitar a kafafen sada zumunta.

‎A cikin bidiyon, ma’auratan sun ce masu garkuwar na neman a sako wasu mutane uku da s**a ce suna tsare, tare da mayar musu da wasu dabbobi da aka ƙwace. Hajiya Amina ta yi kira ga gwamnatin Katsina da shugabannin yankunan da abin ya shafa su shiga tsakani domin a warware matsalar, yayin da Janar Rabe ya buƙaci a fifita zaman lafiya da tattaunawa wajen magance rikicin.

‎An sace Janar Rabe, matarsa da direbansu ne a makon da ya gabata yayin tafiya zuwa Katsina, bayan wasu ‘yan bindiga sun tare motarsu a kusa da ƙauyen Zakin Baure da ke ƙaramar hukumar Matazu. Har zuwa yanzu hukumomin tsaro da gwamnatin jihar ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan bidiyon ko buƙatun da masu garkuwar s**a gabatar ba.

‎Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya bayyana cewa al’ummar Arewa maso Gabas za su mayar da martani ga ayyukan ci gaban ...
07/06/2026

‎Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya bayyana cewa al’ummar Arewa maso Gabas za su mayar da martani ga ayyukan ci gaban ababen more rayuwa da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ke yi da ƙuri’u masu yawa a zaɓen 2027.

‎Ndume ya faɗi haka ne bayan ƙaddamar da aikin sake ginawa da faɗaɗa titin Gombe zuwa Biu mai tsawon kilomita 125. Ya yaba wa Shugaba Tinubu da Ministan Ayyuka, David Umahi, bisa cika alƙawarin gyara titin da ya ce yana da matuƙar muhimmanci ga tattalin arziki, tsaro da haɗin kan yankin Arewa maso Gabas.

‎Sanatan ya ce ya dade yana kira ga gwamnatoci daban-daban su ba titin muhimmanci, kuma ya nuna farin cikinsa cewa Majalisar Zartarwa ta Tarayya ta amince da aikin wanda aka kiyasta zai lashe sama da Naira tiriliyan 1.245. Ya ƙara da cewa al’ummar yankin za su yaba da wannan aiki kuma za su nuna hakan a babban zaɓen da ke tafe.

Address

Guda Abdullahi
Kano
700101

Website

http://stream.zeno.fm/5510fz5kkzzuv

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Vision FM Kano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share