New media 24

New media 24 New media 24
Tasha ce da take kawo muku sahihan labarai, tare da tsage gaskiya ba tare da son rai ba. Idan kuna da labari ku turo mana a 07038603678
(1)

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Tudun Wada/Doguwa, Alhassan Ado Doguwa, ya buƙaci ’yan Najeriya su yafewa Shugaban Ƙa...
28/05/2026

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Tudun Wada/Doguwa, Alhassan Ado Doguwa, ya buƙaci ’yan Najeriya su yafewa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, kura-kuran gwamnatinsa tare da ci gaba da ba shi goyon baya.

Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a birnin Mina na ƙasar Saudiyya, inda ya ce duk da matsin tattalin arzikin da ake fama da shi, akwai buƙatar a duba ƙoƙarin da shugaban ƙasar ke yi wajen tafiyar da mulki.

Doguwa ya ce lokaci ya yi da ya kamata ’yan Arewa su saka wa Tinubu bisa irin goyon bayan da ya bai wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, a zaɓukan baya.
Haka kuma ya yi addu’ar Allah Ya kawo sauƙin rayuwa da zaman lafiya ga al’ummar Najeriya.

“Lokaci ya yi da mutane za su gane tsakanin Kwankwaso da Abba, wanene maci amana daga irin sakamakon da ake shirin aikat...
28/05/2026

“Lokaci ya yi da mutane za su gane tsakanin Kwankwaso da Abba, wanene maci amana daga irin sakamakon da ake shirin aikata wa Gawuna.”

“Daga Muslinta, sai ka ja mana sallah ai muna da limaminmu.”
28/05/2026

“Daga Muslinta, sai ka ja mana sallah ai muna da limaminmu.”

Al-Ameen G Fresh Ya Bayyana Hakan Cikin Bidiyon Da Ya Wallafa A Shafinsa.
28/05/2026

Al-Ameen G Fresh Ya Bayyana Hakan Cikin Bidiyon Da Ya Wallafa A Shafinsa.

Rahotanni daga Daily Nigerian sun bayyana cewa tsohon ɗan takarar gwamna a Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, ya ƙi amincewa da ...
28/05/2026

Rahotanni daga Daily Nigerian sun bayyana cewa tsohon ɗan takarar gwamna a Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, ya ƙi amincewa da tayin kujerar mataimakin gwamna da kuma takarar Sanatan Kano ta Tsakiya da ake cewa an yi masa.

Majiyoyin sun ce tayin ya fito ne daga jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, a wani yunƙuri na shawo kan lamuran siyasa kafin zaɓen 2027.

Sai dai rahotanni sun ce Gawuna ya yi watsi da tayin, yana mai cewa ya shiga tafiyar ne ba tare da wani sharadi ba, kuma zai ci gaba da kasancewa a cikinta.

Bayanan sun kuma nuna cewa wannan mataki na iya shafar shirye-shiryen siyasa a cikin jam’iyyar NDC Kwankwasiyya a jihar Kano.

Daga shafin Mubarak Adam Saleh Mubarak adam saleh “Wallahi Jagora, karya amana ba ka da ita.”
28/05/2026

Daga shafin Mubarak Adam Saleh Mubarak adam saleh “Wallahi Jagora, karya amana ba ka da ita.”

NDC Kwankwasiyya Ta Dage Zaɓen Fidda Gwanin Ɗan Takarar Gwamna Zuwa Ranar Juma’a 29/05/2026.
28/05/2026

NDC Kwankwasiyya Ta Dage Zaɓen Fidda Gwanin Ɗan Takarar Gwamna Zuwa Ranar Juma’a 29/05/2026.

Wane ne, ba wane ne ba?
28/05/2026

Wane ne, ba wane ne ba?

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Abdulaziz Abdulaziz  Abdulaziz na taya Al'umma...
28/05/2026

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Abdulaziz Abdulaziz Abdulaziz na taya Al'ummar Musulmi Barka da Bikin Babbar Sallah.

“Mai girma Kwankwaso ya shiga duhu, ya kasa fidda ɗan takarar gwamna.”
28/05/2026

“Mai girma Kwankwaso ya shiga duhu, ya kasa fidda ɗan takarar gwamna.”

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kura, Madobi da Garun Mallam, Datti Umar Yusuf, ya bayyana cewa ya ...
28/05/2026

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kura, Madobi da Garun Mallam, Datti Umar Yusuf, ya bayyana cewa ya rasa tikitin takarar kujerarsa a ƙarƙashin jam’iyyar NDC Kwankwasiyya domin zaɓen 2027.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ɗan majalisar ya ce ya karɓi lamarin a matsayin ƙaddara, yana mai gode wa Allah da kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, bisa damar da aka ba shi.

Ya kuma gode wa al’ummar Kura, Madobi da Garun Mallam bisa goyon bayan da s**a ba shi tun daga farkon tafiyarsa ta siyasa.

Datti Umar Yusuf ya tabbatar da cewa shi da magoya bayansa za su ci gaba da kasancewa cikin tafiyar Kwankwasiyya tare da mara wa duk wanda ya samu tikitin takara baya daga sama har ƙasa.

“Mun sha faɗin cewa ko da mulki ko babu, muna tare da Engr. Dr. Rabiu Musa Kwankwaso,” in ji shi.

Dan majalisar ya kuma bayyana cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukan tallafa wa al’umma da shirye-shiryen ƙarfafa rayuwa a ragowar wa’adin mulkinsa na kusan shekara guda.

A ƙarshe, ya gode wa magoya bayansa bisa addu’o’i da fatan alheri, yana mai cewa zai ci gaba da gwagwarmaya a tafarkin Kwankwasiyya kamar yadda s**a saba.

Address

Zoo Road
Kano
1122

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when New media 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share