28/05/2026
Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Tudun Wada/Doguwa, Alhassan Ado Doguwa, ya buƙaci ’yan Najeriya su yafewa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, kura-kuran gwamnatinsa tare da ci gaba da ba shi goyon baya.
Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a birnin Mina na ƙasar Saudiyya, inda ya ce duk da matsin tattalin arzikin da ake fama da shi, akwai buƙatar a duba ƙoƙarin da shugaban ƙasar ke yi wajen tafiyar da mulki.
Doguwa ya ce lokaci ya yi da ya kamata ’yan Arewa su saka wa Tinubu bisa irin goyon bayan da ya bai wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, a zaɓukan baya.
Haka kuma ya yi addu’ar Allah Ya kawo sauƙin rayuwa da zaman lafiya ga al’ummar Najeriya.