ASB Hausa

ASB Hausa ASB Hausa
Sahihan labarai, cikin daidaito. Labarai | Rahotonni | Wasanni

Rahotanni daga wasu kafafen yaɗa labarai na Asiya sun ce Amurka da Iran na tattaunawa kan wata yarjejeniya da za ta sa T...
25/05/2026

Rahotanni daga wasu kafafen yaɗa labarai na Asiya sun ce Amurka da Iran na tattaunawa kan wata yarjejeniya da za ta sa Tehran ta sake buɗe mashigar ruwan Hormuz na tsawon kwanaki 30 bayan cimma yarjejeniyar kawo ƙarshen rikici.

Rahoton ya ce shirin yarjejeniyar zai haɗa da dawo da zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar, wadda ke daga cikin muhimman hanyoyin safarar man fetur a duniya.

Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga Amurka ko Iran da ta tabbatar da cikakken cimma yarjejeniyar.

Yadda Jagoran Jam'iyyar NDC na Kano Engr. Rabi'u Musa Kwankwaso ke ganawa da ƴan takarar Jam'iyyar na shiyyar Kano ta ku...
24/05/2026

Yadda Jagoran Jam'iyyar NDC na Kano Engr. Rabi'u Musa Kwankwaso ke ganawa da ƴan takarar Jam'iyyar na shiyyar Kano ta kudu a yau Lahadi.

📸 Hon. Saifullahi Hassan

Tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Mohammed Abubakar-Adamu, ya ƙi amincewa da sak**akon zaɓen fidda gwani na j...
24/05/2026

Tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Mohammed Abubakar-Adamu, ya ƙi amincewa da sak**akon zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC a jihar Nasarawa, wanda ya bai wa Sanata Aliyu Ahmed-Wadada nasara.

Adamu ya zargi cewa an tafka maguɗi da rashin gaskiya a zaɓen, yana mai cewa akwai wuraren da ba a gudanar da zaɓe ba amma aka cika sak**ako.

Ya kuma bukaci shugabannin APC da su binciki yadda aka gudanar da zaɓen, tare da gargadin cewa zai sanar da matakin siyasar da zai ɗauka idan ba a yi masa adalci ba.

Fitaccen jarumin Kannywood, Isah Feroz Khan, wanda aka fi sani da Presdo a cikin shiri mai dogon zango na Labarina, ya a...
24/05/2026

Fitaccen jarumin Kannywood, Isah Feroz Khan, wanda aka fi sani da Presdo a cikin shiri mai dogon zango na Labarina, ya angwance a yau Lahadi.

Rahotanni sun ce an gudanar da ɗaurin auren ne cikin farin ciki tare da halartar iyalai, abokai da masoyan jarumin.

Presdo na daga cikin fitattun jaruman da s**a shahara a shirin Labarina, wanda ya samu karɓuwa sosai a tsakanin masu kallon fina-finan Hausa.

Masoya da abokan arziki sun ci gaba da taya jarumin murnar shiga sabuwar rayuwa ta aure tare da yi masa fatan alheri.

Tsohon ministan sufurin Najeriya ya bayyana hakan ne yayin da yake nuna damuwa kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan na Ka...
24/05/2026

Tsohon ministan sufurin Najeriya ya bayyana hakan ne yayin da yake nuna damuwa kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan na Kaduna Nasir El-Rufai.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan shari’ar El-Rufai da kuma rahotannin hana wasu jiga-jigan jam'iyyar ADC ganinsa.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya ya bayyana haka yayin da yake magana kan shirye-shiryen jam’iyyar ADC gabanin zaɓen ...
24/05/2026

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya ya bayyana haka yayin da yake magana kan shirye-shiryen jam’iyyar ADC gabanin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Sojojin Iran sun ce sun harbo wani jirgin leƙen asiri maras matuƙi na Isra’ila a lardin Hormozgan da ke kudancin ƙasar.K...
24/05/2026

Sojojin Iran sun ce sun harbo wani jirgin leƙen asiri maras matuƙi na Isra’ila a lardin Hormozgan da ke kudancin ƙasar.

Kamfanin dillancin labarai na Mehr ya ruwaito cewa an gano jirgin ne tare da ƙwato ɓaraguzansa da taimakon dakarun ruwa na Iran.

Rahoton ya ce jirgin na aikin sa ido ne kafin sojojin Iran su kai masa hari. Sai dai har yanzu Isra’ila ba ta fitar da wata sanarwa kan iƙirarin ba.

Lamarin na zuwa ne yayin da rikici da tashin hankali ke ci gaba da ƙaruwa tsakanin Iran da Isra’ila a yankin Gabas ta Tsakiya.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya lashe zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC, lamarin da ke nufin zai sake tsayawa ta...
24/05/2026

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya lashe zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC, lamarin da ke nufin zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen watan Janairun 2027.

Tinubu ya samu nasarar ne bayan ya doke abokin karawarsa, Stanley Ofiso, a zaɓen cikin gida da jam’iyyar ta gudanar ranar Asabar a faɗin ƙasar.

Ana sa ran jam’iyyar APC za ta gabatar da shi a hukumance a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa nan gaba a yau.

Tinubu, mai shekaru 74, na neman wa’adi na biyu ne bisa hujjar sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta aiwatar tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023.

Sai dai masu s**arsa na ganin matsalar rashin tsaro, musamman a arewacin Najeriya, na iya zama babban ƙalubale ga takararsa a zaɓen mai zuwa.

A gefe guda kuma, jam’iyyun adawa na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da nasu zaɓukan fidda gwani domin tunkarar shugaban a zaɓen 2027.

Fitaccen tauraron fina-finan Indiya, C Joseph Vijay, ya k**a aiki a matsayin babban ministan jihar Tamil Nadu bayan nasa...
10/05/2026

Fitaccen tauraron fina-finan Indiya, C Joseph Vijay, ya k**a aiki a matsayin babban ministan jihar Tamil Nadu bayan nasarar da jam’iyyarsa ta samu a zaɓen majalisar dokokin jihar.

An rantsar da Vijay ne a birnin Chennai, babban birnin jihar, a gaban dubban magoya bayansa da s**a taru domin shaida bikin.

Jam’iyyarsa ta TVK mai suna Tamilaga Vettri Kazhagam ta samu kujeru 108 a zaɓen, kafin daga bisani ta haɗa kai da wasu jam’iyyu uku domin samun rinjayen kujerun da ake buƙata wajen kafa gwamnati.

Nasarar tasa na zuwa ne bayan shigarsa siyasa daga masana’antar fina-finai, inda ya kasance cikin shahararrun jaruman Tamil da s**a yi tasiri a Indiya.

Masu nazari na ganin nasarar Vijay na nuna yadda taurarin fina-finai ke ci gaba da samun gagarumar karɓuwa a siyasar kudancin Indiya.

Me za ku ce?

03/05/2026

Yadda tsohon Gwamnan Kano Rabi'u Musa Kwankwaso da tsohon Gwamnan Anambra Peter Obi s**a shiga jam'iyyar NDC bayan sun fita daga Jam'iyyar ADC a yammacin yau Lahadi.

Me za ku ce?

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ASB Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category