25/05/2026
Rahotanni daga wasu kafafen yaɗa labarai na Asiya sun ce Amurka da Iran na tattaunawa kan wata yarjejeniya da za ta sa Tehran ta sake buɗe mashigar ruwan Hormuz na tsawon kwanaki 30 bayan cimma yarjejeniyar kawo ƙarshen rikici.
Rahoton ya ce shirin yarjejeniyar zai haɗa da dawo da zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar, wadda ke daga cikin muhimman hanyoyin safarar man fetur a duniya.
Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga Amurka ko Iran da ta tabbatar da cikakken cimma yarjejeniyar.