28/03/2025
Dakarun Sojoji Na Musamman Sun K**a 'Yan Ta'adda Yayin Da Suke Kokarin Dasa Bam A Zamfara..
Dakarun musamman na Operation FANSAN YANMA sun k**a wasu ‘yan ta’adda da suke yunkurin tayar da bama-bamai a wata hanya mai mahimmanci a dajin Gando da ke karamar hukumar Anka a jihar Zamfara.
Wata majiya ta shaida cewa dakarun da ke aiki a karkashin Operation TSAFTA DAJI III Phase 3, sun kai harin kwantan bauna a lokacin da s**a ci karo da wasu gungun ‘yan ta’adda da suke ajiye bama-bamai.
Da ganin dakarun da ke tahowa, ‘yan ta’addan sun gudu zuwa cikin dajin karkashin duhu, inda s**a yi watsi da ababen fashewa da kayan aikinsu.
Kayayyakin da aka kwato sun hada da: Babur daya, jerikan lita 25 guda uku cike da kayan aikin IED, igiyar sapper mai tsawon mita 300, abun fashewar wutar lantarki DET 33 daya da farat daya da ake amfani da su wajen dasa abubuwan fashewa.
Rundunar sojin Najeriya na ci gaba da kai farmaki kan ‘yan ta’adda da masu aikata miyagun laifuka a jihar Zamfara, inda rundunar Operation FANSAN YANMA da Operation TSAFTA DAJI III s**a kai hari a maboyar ‘yan ta’adda a fadin Anka, Bagega, da Bukkuyum.
DefenceInfo NG
HQ Nigerian army