Arewa Updates

Arewa Updates Kafa mai kawo muku labaran halin da ake ciki a Arewacin Najeriya, ba wariya, ba ɓangaranci WhatsApp 09075555758.
(2)

An gudnaar da taron Facebook Connect na matasan ƙaramar hukumar Birni da kewaye na jihar Kano don bunƙasa haɗin kai da s...
08/07/2025

An gudnaar da taron Facebook Connect na matasan ƙaramar hukumar Birni da kewaye na jihar Kano don bunƙasa haɗin kai da sada zumunta.

A wara sanarwa da shugaban kwamitin shirya taron Mukhtar Idrees Bature Maisalati, ya fitar ya ce taron na bana ya yi armashi matuƙa.

Ya ce kwamitin ya samu ci gaba sosai cikin shekara guda, ciki har da koyar da matasa 33 ilimin fasahar AI da samar da guraben aiki, da kuma horas da mata 44 a sana’o’in hannu k**ar haɗa takalma, jaka da dinka zanin gado.

Shugaban ya kuma miƙa godiya ga abokan haɗin gwiwa da shugabannin da s**a ba da gudunmawa, tare da tabbatar da cewa za a ci gaba da shirya irin waɗannan tarurruka domin tallafa wa matasa da ci gaban al’umma.

Ya kuma jinjinawa mahalarta taron kan haɗin kai da goyon bayan da s**a nuna.

Tsohon Dan Majalisar Tsohuwar Karamar Hukumar Minjibir a Jamhuriya ta biyu Alh. Muhammad Jibril Bobo ya rasu.An yi janaʼ...
08/07/2025

Tsohon Dan Majalisar Tsohuwar Karamar Hukumar Minjibir a Jamhuriya ta biyu Alh. Muhammad Jibril Bobo ya rasu.

An yi janaʼizarsa a gidan karatu da ke Rimin Keɓe Mazaɓar Zango da ke Karamar Hukumar Ungogo a Kano.

-Mudassir Hamisu Ahmad

Wasu da ake zargin ’yan daba ne sun lalata makarantu biyu a unguwar Sabon Gari da ke cikin birnin Kano, inda s**a shiga ...
08/07/2025

Wasu da ake zargin ’yan daba ne sun lalata makarantu biyu a unguwar Sabon Gari da ke cikin birnin Kano, inda s**a shiga cikin dare s**a rusa sassa na gine-gine tare da kwashe kayan makarantun.

Daya daga jagororin tsoffin daliban makarantun, Bashir Sharif Ibrahim, ya tabbatar da hakan ga Arewa Updates.

Ya ce matasan sun kai farmaki cikin dare, inda s**a cire kofofi da tagogi, da sauran kayan amfani a makarantar Maikwatashi da ta Commercial, sannan s**a rusa makarantar firamare ta Zawa’i da ke kusa da makarantun.

Wakilinmu ya tuntubi shugaban Hukumar kula da makarantun sakandire ta jihar Kano, Rabiu Sale Gwarzo, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce sun ɗauki matakin sanya masu gadi a wuraren da aka lalata domin hana ci gaba da barna.

Amma wasu rahotanni da Arewa Updates ta samu sun nuna cewa matasan batagarin sun ciccire bulon gine-ginen makarantar Zawa’i kuma s**a kasa a kan t**i s**a sayar a kan farashin Naira dari biyu (₦200) kowanne.

Shin me za ku ce?

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 18 ƙarƙashin Mai shari’a Fatima Adamu ta sanya ranar 11 ga Yuli, 2025 domin fara saura...
08/07/2025

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 18 ƙarƙashin Mai shari’a Fatima Adamu ta sanya ranar 11 ga Yuli, 2025 domin fara sauraron shaidu a shari’ar da Gwamnatin Jihar Kano ta shigar.

Gwamnatin na tuhumar wasu Amir Zakariyya da Aliyu Usaini da laifin haɗin baki wajen aikata fashi da makami da kuma kisan kai.

An zarge su da kisan Buhari Imam, ma’aikaci a Jamiʼar Northwest da ke Kano.

08/07/2025

Dan Gwagwarmayar nan kuma lauyan alʼumma Barr. Abba Hikima Fagge ya maka Hukumar Kiyaye Afkuwar Hadura ta ƙasa FRSC ƙara a Kotu.

Shin ko me ya yi za fi? Ga ƙarin bayanin da ya yi wa Arewa Updates.

Dan Gwagwarmayar nan kuma lauyan alʼumma Barr. Abba Hikima Fagge ya maka Hukumar Kiyaye Afkuwar Hadura ta ƙasa FRSC ƙara...
08/07/2025

Dan Gwagwarmayar nan kuma lauyan alʼumma Barr. Abba Hikima Fagge ya maka Hukumar Kiyaye Afkuwar Hadura ta ƙasa FRSC ƙara a Kotu.

Shin ko me ya yi za fi? Ga ƙarin bayanin da ya yi wa Arewa Updates.
https://youtu.be/E_oGO1YYo1M

Dan Gwagwarmayar nan kuma lauyan alʼumma Barr. Abba Hikima Fagge ya maka Hukumar Kiyaye Afkuwar Hadura ta ƙasa FRSC ƙara a Kotu.Shin ko me ya yi za fi? Ga ƙa...

Ahmed Musa ya musanta raba wa yan Kano Pillars motocin alfarma.Ya nemi masu yaɗa labarin su daina.
08/07/2025

Ahmed Musa ya musanta raba wa yan Kano Pillars motocin alfarma.

Ya nemi masu yaɗa labarin su daina.

Hukumar Lura da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano KAROTA ta roƙi alʼumma su riƙa yi wa jamiʼanta uzri yayin da su ke guda...
08/07/2025

Hukumar Lura da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano KAROTA ta roƙi alʼumma su riƙa yi wa jamiʼanta uzri yayin da su ke gudanar da ayyukansu.

Mataimakin Shugaban Hukumar Auwal Lawan Aranposu ne ya bayyana hakan a Talatar nan, yayin tattaunawa da gidan rediyon Hikima da ke Kano.

Ya ce, jamiʼan KAROTA na yin iya ƙoƙarinsu ne domin taimakawa alʼumma da tabbatar da bin doka ba wai abokan fadan jamaʼa ba ne.

Kamar yadda hukumar ba ta lamunci a ci zarafin jamiʼanta ba haka ma ba za ta lamunci jamiʼanta su cusgunawa jamaʼa ba a cewarsa.

Ya nemi alʼummar Kano su ci gaba da bai wa jamiʼan haɗin kai, yayin ayyukansu tare da sanar da su duk wani bayanai da zai taimaki aikin nasu ga hukumar.

Shin me za ku ce?

Allah ya yi wa fitaccen malamin Alƙur’ani mai girma a Kano, Malam Sabo Sharifai rasuwa.Marigayin ya shafe tsawon shekaru...
08/07/2025

Allah ya yi wa fitaccen malamin Alƙur’ani mai girma a Kano, Malam Sabo Sharifai rasuwa.

Marigayin ya shafe tsawon shekaru yana koyar da Alƙur’ani a unguwanni da dama na cikin birnin Kano.

Ya zamo babban jigo wajen koyar da alƙurʼani a Unguwannin Sharifai, Darma, Zage, Zango, Kofar Wambai, Kasuwar Kurmi, ’Yan Awaki, Dukawa, Gabari, Yola da Hanga.

Ko a lokacin da ya ke kwance a asibiti rahotonni sun nuna yadda ya sanya karatun alƙurʼani a gaba duk da rashin lafiya.

Za a gudanar da jana’izarsa da ƙarfe 11:00 na safe a unguwar Sharifai, zauren Tudun Fadar Sarkin Sharifan Nijeriya, kuma daga nan za a kai shi makabartar Kara da ke Abbatuwa a Kano.

Allah ya jikansa, ya gafarta masa, ya sanya Aljannah Firdausi ce makomarsa.

Ga Makarantar GSSS Kubarachi a Karamar Hukumar Madobi da ke Kano.Hotuna daga Abba M. Hussaini
07/07/2025

Ga Makarantar GSSS Kubarachi a Karamar Hukumar Madobi da ke Kano.

Hotuna daga Abba M. Hussaini

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya umurci shugabannin kananan hukumomi 17 na jihar su haɗa kai da sarakunan gargajiya...
07/07/2025

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya umurci shugabannin kananan hukumomi 17 na jihar su haɗa kai da sarakunan gargajiya domin ɗaukar mataki kan yawaitar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a jihar.

Wannan na cikin jawabin gwamnan a ranar Litinin 7 ga Yuli, 2025, yayin ganawa da shugabannin ƙananan hukumomi da sarakuna a Damaturu.

Gwamnan ya ce dole ne a yi gaggawar dakile matsalar da ke barazana ga matasa da makomar jihar, inda ya ba da umarni a gurfanar da duk wanda aka k**a da hannu a sha ko fataucin ƙwayoyi.

Ya kuma jaddada cewa gwamnatinsa na ci gaba da inganta fannin lafiya, inda aka kafa cibiyoyin lafiya matakin farko 142 tare da ɗaukar sama da ma’aikata 2,000 a faɗin jihar a cewarsa.

Mai bai wa Gwamnan Kebbi shawara Hon. Nasiru Muhammad Dan Umma (Katukan Kabi), ya ajiye muƙaminsa tare da bin tsohon min...
07/07/2025

Mai bai wa Gwamnan Kebbi shawara Hon. Nasiru Muhammad Dan Umma (Katukan Kabi), ya ajiye muƙaminsa tare da bin tsohon ministan shariʼa Abubakar Malami SAN zuwa jamʼiyyar ADC.

A jawabin da ya gabatar yayin sauya sheƙa ya zargi Gwamnatin Kebbi da butulci da munafunci da cin amanar Malami.

Sannan ya sha alwashin cewa za su gani a ƙwaryar shansu.

Shin me za ku ce?

Address

Kano
700231

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Updates posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share