HASKE TV

HASKE TV Inda ake samun labarai masu zafi 🔥
Labaran Arewa | Najeriya | Duniya
Nishadi | Siyasa | Trending videos
📌 Ku danna follow domin sabbin updates kullum.

A tuntubemu ta WhatsApp 08122103543

https://whatsapp.com/channel/0029VbCIGT61t90XKCRWeV0y

Shugaban JIBWIS na ƙasa, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su mutunta addinan juna.Shugaban Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqa...
14/08/2026

Shugaban JIBWIS na ƙasa, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su mutunta addinan juna.

Shugaban Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS)na ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su mutunta addinan juna tare da yin aiki tare domin kare ƙasar.

Ya ce Musulmi da Kiristoci duk suna da haƙƙi da ruwa da tsaki iri ɗaya a Najeriya, kuma ya k**ata su zauna lafiya duk da bambance-bambancen addinansu.

Bala Lau ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa na Abuja, bayan tashin Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League), Sheikh Dr Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa, bayan kammala taron ƙasa da ƙasa na kwanaki biyu kan bambancin al’adu da zaman lafiya a cikin al’umma.

JIBWIS ce ta shirya taron tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya, mai taken: “Bambance-bambance da Zaman Lafiyar Al’umma: Haɗin Gwiwa Domin Makoma Mai Kyau.”

HASKE TV

Da Dumi-Duminsa: Kasar Iran Ta Kai Hari Kan Jiragen Kasar Daukar larabawa a Mashigar Hormus UAE Ta Zargi Iran da Kai Har...
14/08/2026

Da Dumi-Duminsa: Kasar Iran Ta Kai Hari Kan Jiragen Kasar Daukar larabawa a Mashigar Hormus

UAE Ta Zargi Iran da Kai Hari kan Jiragen ADNOC a Mashigar Hormuz
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) ta yi kakkausar s**a ga Iran, tana zargin cewa Iran ta kai hari kan jiragen ruwa biyu masu alaƙa da kamfanin mai na ƙasar, ADNOC, yayin da suke wucewa ta Mashigar Hormuz a ranar Alhamis.
UAE ta ce ba a samu rahoton jikkata ko mutuwa ba, amma ta bayyana harin a matsayin babban barazana ga tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa da kuma samar da mak**ashi a duniya.

Mashigar Hormuz na daga cikin muhimman hanyoyin safarar man fetur da iskar gas a duniya, kuma wannan sabon lamari na ƙara tsananta rikicin da ke tsakanin Iran da ƙasashen yankin.

Rahotanni sun ce Iran ba ta bayar da martani kan wannan zargin na UAE ba tukun

HASKE TV

ICPC Ta Bankado Ma’aikatan Bogi 900Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa Ta ICPC ta bankado wasu ma’aikatan bogi da aka s...
13/08/2026

ICPC Ta Bankado Ma’aikatan Bogi 900

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa Ta ICPC ta bankado wasu ma’aikatan bogi da aka saka cikin tsarin biyan albashin gwamnati, ciki har da wani jami’i da ya shigar da ’yan uwansa 14, yayin da wani kuma ake zargin yana karɓar albashi 13.

Shugaban ICPC, Musa Aliyu, ya ce binciken da hukumar ta gudanar ya gano yadda wasu ke amfani da dabaru wajen saka sunayen bogi cikin albashin gwamnati.

Ya ce hukumar ta gano kusan ma’aikatan bogi 900 tare da wallafa sunayensu.

Ya bayyana cewa ICPC ta kwato sama da Naira biliyan 24 daga kudaden fansho na ma’aikatan bogi a shekarar 2024.

Ya ce hukumar na ƙara mayar da hankali wajen hana cin hanci da rashawa da kuma kare dukiyar gwamnati ta hanyar amfani da bayanai da fasaha.

HASKE TV

Kungiyar Ma’aikatan Sufurin Jiragen Sama Ta Ce Naira Biliyan 25 Na TSC Na Hana Ci GabaKungiyar Ma’aikatan Sufurin Jirage...
13/08/2026

Kungiyar Ma’aikatan Sufurin Jiragen Sama Ta Ce Naira Biliyan 25 Na TSC Na Hana Ci Gaba

Kungiyar Ma’aikatan Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasa (NUATE) ta ce rashin mika Naira biliyan 25 na kudin TSC da kamfanonin jiragen sama s**a tara na kawo cikas ga ayyukan harkar jiragen sama.

Shugaban kungiyar na Abuja, Ahmed Yusuf, ya ce kudaden kashi biyar cikin dari ne daga tikitin fasinjoji da ya k**ata a bai wa hukumomin jiragen sama domin gudanar da ayyukansu da kula da jin dadin ma’aikata.

Ya ce rashin mika kudaden na barazana ga dorewar hukumomin jiragen sama, tare da jaddada cewa ma’aikata na da hakkin kafa kungiyoyin kwadago.

Kungiyar ta ce yajin aikin da ta yi tare da kungiyar manyan ma’aikatan ayyukan sufurin jiragen sama ta Najeriya (ATSSSAN) ya samo asali ne daga matsalolin ma’aikata, yayin da NCAA da FAAN s**a bukaci bangarorin da abin ya shafa su rungumi tattaunawa.

HASKE TV

Rundunar Tsaron Amurka CENTCOM Ta Ƙaddamar da Sabuwar Rundunar Jiragen Yaƙi Masu Sarrafa Kansu a Cikin TekunRundunar Soj...
13/08/2026

Rundunar Tsaron Amurka CENTCOM Ta Ƙaddamar da Sabuwar Rundunar Jiragen Yaƙi Masu Sarrafa Kansu a Cikin Tekun

Rundunar Sojin Amurka ta CENTCOM ta sanar a ranar 13 ga Agusta cewa tana ƙoƙarin kafa rundunar farko ta ƙasashe da dama, wadda za ta mayar da hankali kan amfani da jiragen yaƙi marasa matuƙi (drones) daga sama, teku da ƙarƙashin teku.

An sanya wa rundunar suna Task Force Falcon Strike. Za ta ƙunshi sojojin Amurka da abokan hulɗarta na yankin Gabas ta Tsakiya, domin haɓaka da kuma haɗa amfani da mak**an drones masu kai hari.

Wannan mataki ya zo ne watanni tara bayan kafa Task Force Scorpion Strike, wadda ita ce rundunar farko ta musamman da Amurka ta kafa a Gabas ta Tsakiya domin amfani da drones masu kai hari.

A cewar CENTCOM, Scorpion Strike ta samu nasarori da dama, ciki har da harba drone mai kai hari daga wani jirgin ruwan yaƙin Navy na Amurka a watan Disamba.

Kwamandan CENTCOM, Adm. Brad Cooper, ya ce Falcon Strike za ta faɗaɗa nasarorin da Scorpion Strike ta samu, tare da haɗa sabbin fasahohin soji na Amurka da na ƙawayenta.
CENTCOM ta fara tattaunawa da ƙasashen abokan hulɗarta domin gayyatar su shiga sabuwar rundunar. Idan ƙasashen s**a shiga, ana sa ran Falcon Strike za ta taimaka wajen samar da tsarin haɗin gwiwar drones masu kai hari a faɗin Gabas ta Tsakiya.

Rundunar sojojin U.S. Special Operations Command Central (SOCCENT) ce za ta jagoranci ma'aikatan Falcon Strike daga Amurka da ƙasashen abokan hulɗa.

HASKE TV

Sabbin Hotuna Sun Nuna Hare-haren Iran Sunyi wa Amurka Mummunan BarnaSabbin hotunan tauraron ɗan Adam sun nuna wuraren d...
13/08/2026

Sabbin Hotuna Sun Nuna Hare-haren Iran Sunyi wa Amurka Mummunan Barna

Sabbin hotunan tauraron ɗan Adam sun nuna wuraren da ake cewa hare-haren mak**ai masu linzami na Iran s**a lalata ko s**a yi wa illa a wasu muhimman wurare a yankin Gulf. Rahotanni sun tabbatar da cewa hare-haren sun shafi wasu na’urorin radar da cibiyoyin fasaha da ake dangantawa da ayyukan sojin Amurka.
Abubuwan da aka bayyana a cikin rahoton:
🇦🇪 Hadraf Air Base, UAE: Na’urar radar ta TPS-57.

🇦🇪 Habshan: Na’urar matsa iskar gas a yankin masana’antar mak**ashi.

🇧🇭 Bahrain: Cibiyar bayanai ta Amazon da Iran ta ce tana tallafa wa ayyukan leƙen asirin sojin Amurka; hotunan tauraron ɗan Adam sun nuna alamun lalacewa a wuraren cibiyar.

🇦🇪 Masana’antar aluminium: An kuma bayyana lalacewa ga wani ɓangare na masana’antar.
Rahotannin sun nuna cewa Iran na ƙoƙarin kai hari kan radar, sadarwa da sauran muhimman ababen more rayuwa da take ganin suna taimaka wa sojojin Amurka da kawayenta a yankin.
Domin samun ingantattun labarai kuyi following HASKE TV

Yahudawan Isaraila Sunkai Hari Wani Gida a Yankin Qozah Tare Da Tozarta Al'qur'ani Mai GirmaRahotanni sun ce wasu mazaun...
13/08/2026

Yahudawan Isaraila Sunkai Hari Wani Gida a Yankin Qozah Tare Da Tozarta Al'qur'ani Mai Girma

Rahotanni sun ce wasu mazauna Isra’ila sun kai hari tare da lalata wani gida a yankin Bir Qozah, kusa da matsugunin Beita, da ke kudancin Nablus a Yammacin Kogin Jordan.

A yayin harin da aka kai jiya da rana, an zargi mazauna Isra’ilan da tsagewa da kuma tozarta Alƙur’ani mai girma da ke cikin gidan.

Lamarin ya jawo Allah-wadai, musamman saboda yadda ake kallon Alƙur’ani a matsayin littafi mai tsarki ga Musulmi a duniya.

HASKE TV

An K**a Mutane 4 Da Ake Zargi Da Shirin Kashe Wani Dan Kasuwa A AnambraRundunar ’yan sandan jihar Anambra ta k**a mutane...
13/08/2026

An K**a Mutane 4 Da Ake Zargi Da Shirin Kashe Wani Dan Kasuwa A Anambra

Rundunar ’yan sandan jihar Anambra ta k**a mutane hudu da ake zargi da kulla makircin kashe wani dan kasuwa tare da kwace filayensa a Ukwulu, karamar hukumar Dunukofia.

Wadanda aka k**a sun hada da Obiora Nwankwo mai shekaru 38, Chiadikobi Okoye mai shekaru 36, Emmanuel Mboko mai shekaru 42 da Ifeanyi Obi mai shekaru 37.

An k**a su ne a wurare daban-daban a Ukwulu da Amichi.

Kakakin rundunar, Tochukwu Ikenga, ya ce jami’an Rapid Response Squad da hadin gwiwar jami’an tsaron Agunechemba ne s**a gudanar da kamen bisa sahihan bayanan sirri. An kuma kwato bindigogi biyu da alburusai daga hannun wadanda ake zargin.

Ya ce bincike na ci gaba da gudana domin gano sauran mutanen da ke da hannu da kuma tantance rawar da kowanne daga cikin wadanda ake zargin ya taka.

HASKE TV

Da Dumi-Duminsa:Jirgin Saman Yaƙin Amurka Ya Tarwatse Birnin a Texas, Mutane Biyu Sun Sheka LahiraWani jirgin saman yaƙi...
13/08/2026

Da Dumi-Duminsa:Jirgin Saman Yaƙin Amurka Ya Tarwatse Birnin a Texas, Mutane Biyu Sun Sheka Lahira

Wani jirgin saman yaƙi mai saukar ungulu kirar AH-64 Apache na sojojin Amurka ya yi hatsari a yankin Salado, jihar Texas, inda matukan jirgin biyu da ke cikinsa s**a rasa rayukansu.

Rahotanni sun ce jirgin, wanda ke da alaƙa da sansanin sojojin Fort Hood, ya faɗi cikin wani fili a ranar Laraba, 12 ga Agusta 2026, sannan ya haddasa babbar gobara a yankin.

Gobara ta bazu zuwa kusan acres 100, lamarin da ya sa hukumomi s**a kwashe wasu mazauna yankin tare da rufe wasu hanyoyi domin jami’an agaji su samu damar gudanar da aikin ceto da kashe gobarar.

Hukumomi sun tabbatar da cewa jirgin bai bugi wani gida ko mutum a ƙasa ba. Har yanzu ana ci gaba da bincike domin gano abin da ya haddasa hatsarin, yayin da ba a bayyana sunayen sojojin biyu ba saboda ana jiran sanar da iyalansu.

CNN ta ruwaito cewa: hatsarin ya faru ne yayin da jirgin ke gudanar

HASKE TV

Gwamnan Ondo Ya Sa Hannu Kan Sabuwar Dokar Wutar LantarkiGwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya amince da sabuwar doka...
13/08/2026

Gwamnan Ondo Ya Sa Hannu Kan Sabuwar Dokar Wutar Lantarki

Gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya amince da sabuwar dokar gyaran harkar wutar lantarki ta jihar ta shekarar 2026, wadda za ta ƙarfafa tsarin samarwa, rarrabawa da kula da wutar lantarki.

Dokar ta kafa Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Ondo, wadda za ta kula da lasisi, farashin wuta, saka hannun jari,da mak**ashi mai sabuntawa.

Haka kuma za a kafa masu kula da tsarin wuta da kasuwar lantarki ta jihar.

Sabuwar dokar ta tanadi tilasta sanya mitoci, kare kayayyakin wutar lantarki da kuma hukunta masu lalata ko yi wa kayan wuta zagon ƙasa.

Gwamnatin jihar ta ce dokar za ta jawo masu saka jari masu zaman kansu, ƙara samun ingantacciyar wutar lantarki, bunƙasa mak**ashi mai sabuntawa da kuma amfani da wutar lantarki wajen haɓaka masana’antu da tattalin arzikin jihar.

HASKE TV

Address

Nigeria
Kano
713281

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HASKE TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share