Rayuwar aure

Rayuwar aure Muna aiki domin kawo canji tareda bayar da shawarwari ga zamantakewa tsakinin al'umma musammanma ma aurata
Da kuma fannin magunguna

WAI YANA GUDUN RENIWani me kudine yakeson wata yarinya zai Aura, sai ya Kira saurayinta yace masa zan baka jarin 1.5M Ku...
27/06/2025

WAI YANA GUDUN RENI

Wani me kudine yakeson wata yarinya zai Aura, sai ya Kira saurayinta yace masa zan baka jarin 1.5M Kuma zai maka kayan Aure ka nemi wata ka Aura Amma ka bar mini ita na Aura!

Anyi hakane a gaban yarinyar, budan bakin saurayin sai yace ai kudi bazai rabani da ita ba, saboda ba don kudi takeso na ba, Kuma Nima ba don kudi nakeson ta ba..

Sai me kudin yayi murmushi, ya tafi, bayan kwana uku sai yaje gidan su yarinyar ya samu mamanta ya bata 50K, ya sayi manyar bunjuma guda biyu na 300K ya Ajjiyewa mahaifinta da 50K yace masa zan dawo muyi magana, Akwai Nima bukata da nake dashi daga gareka.

Haka bayan kwana biyu sai babanta yayita kiransa, finally dai yazo ya samu babanta yace masa Tabbas wance nakeso, Amma da Aure, inason ka taimaka min ka bani ita, atake babanta ya Aminci, yarinya tayita kuka, sai Alhajin yayi mata text cewa zataje Hajji kafin idan s**a dawo sai a daura Auren, ai washe gari da saurayin ta yazo juya masa baya tayi.

Yanzu haka Anyi Aure har sun haihu, shi Kuma saurayin Yana Nan Yana Neman aiki da FCE, Abinda zaici ma wahala take bashi, wannan shine illar makahon soyayya, kokuma rashin hangen nesa, Ya Ubangiji ka rabamu da aikin Danasani, Kayi mana mafita na Alkhairi.
Bilal Omar Baba Gombe ✍️

Amfanin Namijin Goro 16 Ga Lafiyar Dan’adam : 🔻Kamar yadda masana s**a bayyana, namijin goro na da matukar amfani ta fus...
27/06/2025

Amfanin Namijin Goro 16 Ga Lafiyar Dan’adam : 🔻

Kamar yadda masana s**a bayyana, namijin goro na da matukar amfani ta fuskoki da dama, musamman a bangaren da ya shafi magunguna, karin kuzari da sauran mak**antansu

🔴 Ga amfanin da namijin goron ke da shi 16 k**ar haka:

1⃣– Namijin goro na maganin tari; idan aka hada shi da alawar tomtom aka ci a tare.

2⃣– Kazalika, namijin goro na maganin matsalar ciwon sanyi; idan aka hada shi da kanumfari a tafasa a ruwa aka rika sha.

3⃣– Namijin goro yana maganin matsalar tsutsar ciki; idan aka jajjaga shi aka matse ruwan, sai a zuba zuma a rika sha.

4⃣– Haka nan, namijin goro na maganin olsa, idan aka hada shi da dabino aka daka, sai a zuba zuma cokali biyu a sha.

5⃣– Wakazalika, namijin goro na maganin kara kuzari da nisan tafiya ga masu iyali, idan aka hada shi da dabino sai a rika tauna su tare.

6⃣– Namijin goro na gyara maniyyi, idan aka jajjaga shi aka samu garin hulba aka tafasa, sai a samu madarar ruwa a zuba a shanye baki-daya.

7⃣– Sannan, namijin goro na kawar da majinar kirji, idan ana cin sa lokaci zuwa lokaci.

– Namijin goro na hana shan taba, idan aka hada shi da furen tumfafiya, aka dake aka samu karan sigari da madarar shanu mai kyau, a hada guri guda a bar su su kwana da safe kafin a ci komai, sai mai shan tabar ya shanye duka. Bayan wasu mintuna ko awanni zai yi aman dattin tabar baki-daya, sannan ba zai kara sha’awar sake ba da yardar Allah.

– Har ila yau, namijin goro yana maganin hawan jini, idan aka hada shi da ganyan cediya; sai a tafasa a sa zuma a sha.

– Namijin goro na maganin ciwon kai, idan aka dake shi ya zama gari, sai a rika yin hayaki (turare) da shi, musamman ma mata masu yawan ciwon kai.

– Namijin goro yana gyara murya, idan aka hada shi da danyar citta da zuma, ana dafawa da lifpton a sha kafin a ci komai da safe.

– Namijin goro na maganin kuraje, idan aka samu garin namijin goron; aka kwaba da man zaitun. Idan kuma karzuwa ce ko bakon dauro, sai a kwaba da manja a rika shafawa.

Saboda yana son ki ya aure ki,amma ki sani cewa ke ce zaki kara karfafa soyayyar ki a wajan sa.Kiyi masa abinda yake so ...
27/06/2025

Saboda yana son ki ya aure ki,amma ki sani cewa ke ce zaki kara karfafa soyayyar ki a wajan sa.

Kiyi masa abinda yake so kuma kina gudun abinda baya so,idan kina masa haka zaki kara samun soyayyar sa a gare ki kuma zaki ga dukkan abinda k**e so zai miki.

Amma idan bakya masa abinda yake so ba,wato kin rainasa kina masa wulakanci,a sannu wannan son dayake miki zai daina,kuma bazaki samu yadda k**e so daga gare sa ba.

©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

ƘALUBALEN MATA: 😔1. An saketa: ai ba zata iya zaman aure ba🤔2.  Anyi mata fy*ɗe: laifinta ne wace irin shiga tayi lokaci...
27/06/2025

ƘALUBALEN MATA: 😔

1. An saketa: ai ba zata iya zaman aure ba🤔

2. Anyi mata fy*ɗe: laifinta ne wace irin shiga tayi lokacin??🥴

3. Tayi aure bata haihu ba: ai juya ce🥺🤰🏿

4. Tayi aure bata haifi ɗa namiji ba: laifin ta ne babu ɗa namiji a cikin ta 🙃

5. Ta samu arziki tana zama tana riƙe da kanta: hegiya karuwa ce..🤭💃🏿

6. An samu yaro kangararre: Laifin uwar shi ce, ita ta sangarta shi 😢

7. Tana son tayi wasannin motsa jiki: ke yarinya ce?, wannan ba shine dalilin zuwan ki duniya ba 🙎

8. Ba tayi aure ba, amma tana tuƙa mota 🚙: hummm zata kori masu zuwa neman auren ta... 🚗🙍

9. Ta faɗi ra'ayin ta: chaf, wannan boss ce juya mijinta zatayi 🙄🙎🏿

10. Ta shekara 30 ba tayi aure ba: tsohuwa ce bata da amfani 😐🤦🏿

11. Tayi aure: kash ta zama mallakin mijinta

12. Mijinta na bin mata a layi: laifin ta ne, itace silar hakan, tayi haƙuri tayi ta addu'a kawai 💔😞

13. Mijinta ya mutu: hummm ita ta kashe shi domin ta ci gado... 😥

14. Ta sake aure bayan mutuwar mijinta: hegiya ko damuwa ba tayi ba da mutuwar tsohon mijinta ba... 😔

15. Mijinta yayi mata duka: zaka samu tayi mishi wani babban laifi ne ku bincika?.. 😩

wannan sune wasu daga cikin maganganu da ake tsinkaya a yawancin majalisin wasu marasa ganin kimar mata!

Babu mai daraja mata sai mai daraja..

Ubangiji muke roƙo Ya ƙara shiga lamuran mu tare da hanamu yi da wani....🙏🙏🙏

Masu fama da karancin ruwan maniyyi ko rashin sha'awa da rashin haihuwa ga magani da yardar Allah.1- Ayaba 2- Tafarnuwa ...
25/06/2025

Masu fama da karancin ruwan maniyyi ko rashin sha'awa da rashin haihuwa ga magani da yardar Allah.

1- Ayaba
2- Tafarnuwa
3- Dabino
4- Madara

Za'a hada asa madara (ta ruwa) a marakade yawansa yakai kofi ɗaya. Za'a sha kullum sau 1 na kwana 10.

Indai kana so ka samu dama ta rayuwa sannan ka ɗaukaka a kowacce irin hanya da ka sa gaba (Politics, Business ko kuma wa...
25/06/2025

Indai kana so ka samu dama ta rayuwa sannan ka ɗaukaka a kowacce irin hanya da ka sa gaba (Politics, Business ko kuma wani bangare na cigaban rayuwa), ya zama dole sai ka cire mutanen da ka sani ko ka taso a cikin su akan wannan hanyar kafin ka je inda kake son zuwa. Ma'ana: a yadda tarihi ya nuna, ba wani mutum a duniya da ya taɓa shahara da taimakon mutanen da ya taso a cikin su. Idan ma akwai, ɗaiɗaiku ne saboda basu da yawa cikin mutane. Meaning; the chance for you to make it is harshly difficult in reality.

Last week na shiga shafin Apostle Joshua sai na ci karo da wani video wanda ya kara shaping mind ɗina a rayuwa. Cikin abinda na saurara daga gare shi, ya bada misalin tarihin Annabi Isah (AS) cewa: da ace Annabi Isah ya taso a Nazareth ne, ko sauraren sa mutanen Nazareth ba zasu yi ba saboda zasu fara cewa "to wannan yaron da yake wasa da Taya a cikin rairai shine yanzu zai ce shine Annabi?😀, tukunna ma yaushe ya girma da ya isa ya fara karantar damu ko nuna mana gaskiya?" Ya bada misalai masu tarin yawa ciki harda irin misalan da s**a faru da Annabi Muhammad SAW da yadda yan uwa da mutanen da ya taso a cikin su s**a masa - Not because basu yadda da kasancewar sa mutumin kirki bane ko kuma yana da wata illa gare su. Idan ka bibiyi tarihin za ka ga cewa duk wani ƙalubalen da ya fuskanta yana da alaƙa da sanin da s**a yi masa ne sak**akon sun san ƙabilarsa, ahalinsa da kuma rayuwar sa tun yana ƙarami kafin ya samu ɗaukaka ta annabta.

Ka bibiyi tarihin Annabi Muhammad SAW, zaka fahimci duk wani misali da nake so na baka a wannan rubutun. Makkah itace garin da aka haifeshi sannan anan ya girma yayi wayo har annabta ta same shi. Amma daga karshe mutanen da s**a sanshi tun yarinta sune s**a hana shi duk wani jindadi da walwala saboda a cikin su ya taso. Tarihi ya tabbatar da saida ya koma Madina cikin mutanen da Basu san shi ba sannan ya samu nutsuwa kuma ya samu ɗaukaka kan abinda ya zo dashi.

Wannan fa bawai fiction story bane. It's natural call of nature

Idan namiji yaga mace.............................1.kyawunki yana jan ra'ayin sa a lokacin domin maza da yawa sun fi kal...
25/06/2025

Idan namiji yaga mace.............................

1.kyawunki yana jan ra'ayin sa a lokacin domin maza da yawa sun fi kallon kyawun mace sosai.

2.zai fahimci yanayin halayyan ki anan ma,domin namiji mai wayo zaiyi kokarin ganin shin yanayin ki zai yi daidai da tsarin rayuwar sa ne, saboda yana son macen da tsarin rayuwar sa zaiyi daidai da nashi.

3.fahimtar zurfin karatun ki duka guda biyu,wani yana son mace mai dogon karatu wani kuma yana son daidai,wani kuma ba ruwan sa,amma a yanzu ilimi ya wadata, yana son wanda zata gina masa gida da ilimin yadda har 'ya'yan sa ma zata taimaka masu.

4.Yanayin yadda take mu'amala da iyayen ta tana girmama su,tana masu biyayya idan mace tana da wannan to kaima naka iyayen zata girmama su matuka domin ta samu tarbiyya.

5.Fahimtar kawayen ta domin akwai matan da kowacce irin qawa ce nasu ne tana da son tarin qawaye,anan zai gane idan yaga abin yayi yawa zaiyi kokarin ganin ta rage.

6.Idan kuka samu sabani a tsakanin ku,tana iya saukar da kanta ta baka hakuri ko kyale ka take yi?
Akwai wasu matan da duk sabanin da zasu samu bazasu bada hakuri ba,suna kallon tamkar sun kaskantar da kan su ne,sai dai in shi ya gaji ya sauko da kansa,irin hakan ko kunyi aure bazata canja ba domin Ka saba mata da hakan.

A haka wani yake iya fahimtar mace wanda zai ga idan tayi daidai da tsarin rayuwar sa.

©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

📑 YANDA ZAKA GANE ZUMA MAI KYAU DA MAI HAƊI👇1- Kasata a freezer gidan ƙanƙara, idan mai kyauce yanda kasata ko kwana naw...
16/06/2025

📑 YANDA ZAKA GANE ZUMA MAI KYAU DA MAI HAƊI👇

1- Kasata a freezer gidan ƙanƙara, idan mai kyauce yanda kasata ko kwana nawa zatayi bazata canzaba idan kuma akwai haɗi zai iya daskarewa.

2- Kasanya zuma awani mazubi kaɗora kan wuta (wuta ƙasa-ƙasa) idan akwai haɗi zakaga tana tafasa tana kumfa ko ta ƙone duka, idan mai kyauce zata iya tafasa amma bazatayi kumfaba.

3- Kazuba ruwa a kofi saika ɗebi zuma kasa a ruwan ka gauraya kajira kaɗan, idan mai kyauce zakaga ta kwanta aƙasan kofin ko tayi haske, idan batada kyau zata iya narkewa ko tayi fatsi fatsi.

4- Kasamu paper kaɗan zuba zuma akai kabarshi zuwa ƴan mintuna, idan tanada kyau zakaga tariƙe paper tayi ƙarfi, idan batada kyau zakaga tayi saurin shiga paper kuma bazatayi ƙarfiba.

5- Idan zuma tanada kyauce idan ka shinshinata zakagaji tana ƙamshi sosai irinna furanni amma batada kyau zakagaji ƙamshin bayida ƙarfi ko kaji wani ƙamshi

MAGANIN BASIR KYAUTAFarko ma menene Basir ?Da farko dai a cikin duburar 'dan Adam akwai jijiyoyin jini wadanda wani loka...
16/06/2025

MAGANIN BASIR KYAUTA

Farko ma menene Basir ?

Da farko dai a cikin duburar 'dan Adam akwai jijiyoyin jini wadanda wani lokacin suna samun matsatsi da talala mai takurasu.
A lokacinda s**a samu takurawa da yawa, sai su kumbura.

Kumburin wadannan jijiyoyin jini da kara matsi da takura a garesu cikin dubura shi ya ke sa wa kaga wani tsiro ya fito maka a bakin dubura, wanda jijiyar jini ce.😡😳

Za ka ji ciwo, ko kai-kayi koma zubar jini.

Wannan shi ake cewa.... BASIR-MAI-TSIRO.
Da akwai kuma nau'in Basur mai sanya yawan fitar hutu wato tusa da kuma mai sa cushewar ciki ko yin kashi mai tauri. Wani basir din kuma har yana sa tsatstsagewar dubura yayin fitar bayan gida😭

ALAMUN DA MUTUM ZAI GANE YANA DAUKE DA BASUR😭👇🏼

Mutum zai rika fama da wadannan matsaloli

👉🏼Kaikayi a dubura da bacin rai.

👉🏼Fitar jini idan ana bayan gida amma ba tare da anji zafi ba.

👉🏼Ciwon jiki da rashin sakewa.

👉🏼Kumburar dubura.

👉🏼Fitar kashi curi-curi ko dunkule-dunkule tare da wahala.

HANYAR DA ZA'A BI DOMIN GUDUN KAMUWA DA CUTAR BASIR...

Wanda yake gudun kamuwa da cutar Basur sai ya yawaita shan dauri da daci, k**ar gauta da sassaqen mangwaro ko sassaqen 6aure ko madaci, ko mur da mak**antansu. Saidai a kula, kada a matsawa shan daci saboda matsalolin hanta.



MAGANIN BASUR KOWANNE IRI

Idan an riga an kamu da ciwon basur kuma sai a gwada daya daga cikin wadannan hanyoyi:-
👉🏼A samu lemon-tsami guda uku, tsohuwar-tsamiya guda uku, jan-gauta guda uku, barkono guda biyar, sabulun sha k**ar girman lemon tsami.

In aka tashi sai a hade su wajedaya, a jika, su kwana. Kullum sai a tsiyayi rabin kofi a sha da safe kafin a ci abinci. Ana diba ana kara ruwa, har sai ya salamce sannan a zubar.

Wannan magani ne na Basur sosai. Indai ka hada shi zai warke, ka rabu da shi da iznin Allah.

👉🏼 A samu madacin qasa daidai misali, a wanke shi, a zuba a cikin tukunya. A zuba ruwa da jar kanwa kadan, a dora akan wuta.

Idan ya huce, sai a dinga shan rabin kofi kullum sau uku. Da safe rabin kofi, da rana rabin kofi da daddare ma rabin kofi.
A dinga sha kullum ana kara ruwa har ya salamce. A cigaba da hadawa har sai an warke sarai.

👉🏼A samu sassaqen itacen mangwaro, da sassaqen kadanya, da sassaqen dorawa, da sassaqen madaci amma madacin kadan ake bukata.

Sai a hade su wajedaya a wanke a zuba jar kanwa kadan.

A tafasa, kullum a sha rabin kofi sau uku kafin a ci abinci.

Idan kuma basur din mai tsiro ne ko wanda ake fitar baya, to idan an tashi sai a tafasa magungunan a zuba ruwan a cikin babban mazubi. Sai ka tsuguna, tururin ya dinga shiga karkashinka, idan ya dan huce kuma sai a shiga ciki a zauna tsawon yan mintuna ko kuma a dinga k**a ruwa da shi.

Insha Allahu indai an hada wannan ana sha ana shiga ciki, to lokaci kadan za a rabu da basur kowane iri ne.

👉🏼A samu 6awon dorawa, a hada da jar kanwa a tafasa. Sai a dinga tsugunawa yadda tururin zai dinga shiga cikinka sosai, idan ya dan huce sai a shiga ciki a zauna ko a dinga k**a ruwa da shi. Sannan a dinga tsiyaya ana sha. Shi ma hanya ce ingantacciya ta maganin basur.

👉🏼 A samu man habbatussaudaa da man tafarnuwa da man zaitun. Sai a hada su waje daya. Sai ka samu auduga mai kyau ka dangwali wannan man kay matsi da shi a karkashinka, musamman in za ka kwanta da daddare. Kullum ka dinga yin haka sau daya. Wannan yana saurin kashe basur mai tsiro da maganin tsatstsagewar dubura.

👉🏼A samu garin sanamakiy da zuma. Sai a tafasa garin rabin cokali, a sa zuma daidai gwargwado. Sai a sha kullum sau daya.

Yana maganin kashin jini, da taurin bayan gida, yana fitar da dattin cikin cikin kankanin lokaci. Saidai wannan banda mace mai ciki, banda yara kanana.

👉🏼A samu `ya`yan raidore da kumfar maliya da garin bagaruwa, sai a hada su waje daya a tafasa. Sai ya tsuguna tururin ya dinga shiga jikinsa, idan ya dan huce sai ya zauna a ciki ko kuma ya dinga k**a ruwa da shi. Wannan yana kone tsuron basur yana maganin tsatstsagewar dubura.
Allah yabamu Lafia.

IDAN ana buqatar hadadden maganin Basir sai a tuntubeni Muna Nan a kasuwar rimi bayan Asibitin murtala kano
In ma baka kano zamu aika maka duk Inda kake in shaa ALLAH.

BAYANIN YADDA AKE YIN ISTIKHARA IRIN WACCE ANNABI ﷺ YA KOYAR:Istikhara wata sallah ce da akeyi domin neman za'bin Allah ...
16/06/2025

BAYANIN YADDA AKE YIN ISTIKHARA IRIN WACCE ANNABI ﷺ YA KOYAR

:
Istikhara wata sallah ce da akeyi domin neman za'bin Allah madaukakin sarki game da wasu al'amura da bawa yake neman zabin Allah a cikin ɗaya daga cikinsu, misali k**ar a harkar neman aure dadai sauran wasu al'amuran.

Anan zamu fahimci cewa ashe ita istikhara ibadace kuma Annabi muhammadu ﷺ shine ya koyar da yadda ake yin ta, sabida haka babu inda akace kaje ayi MAKA ita inkuma kaje daya daga cikin wannan zaayi MAKA . bugun kasa ko duban taurari ko akira aljani a tmby shi shikuma ya gaya musu karya da gaskiya sukuma su gayama Allah yabamu Samar bin abinda Manson Allah ﷺ yazo mana dashi .duk wanda yayi wata istikhara ba irin wacce manzon Allah ﷺ ya koyar ba, to ya sani ba istikhara tabbatacciya yayi ba koda ma yayi babu wani tasiri da zatayi domin Allah madaukakin sarki baya karbar duk wata ibada har sai anyita a bisa koyarwar Annabi muhammadu ﷺ .

Sahabi jabir (ra) yana cewa: *MANZON ALLAH ﷺ YA KASANCE YANA KOYA MASU ISTIKHARA A CIKIN DUKKAN AL'AMURANSU KAMAR YADDA YAKE KOYA MUSU SURA DAGA CIKIN AL'KURANI.*
hadisin yana cikin *Sahihul Bukhari*

kunga wannan yake nuna mana ashe ita itikhara annabi ne ya koyar da ita bawai kowa gaban kansa zeyi kawai yaje ya aikata abinda yaga dama a matsayin istkhara ba.

Hal ila yau dai sahabi jabir yana cewa: Annabi yace: *IDAN 'DAYANKU YAYI NUFIN YIN WANI AL'AMARI TO YAYI SALLAH RAKA'A BIYU BA SALLAR FARILLAH BA SANNAN YACE*
اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْتَخِيرُكَ بِعِلْمِكَ، وَأسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْألُكَ مِنْ فَضْلِكَ الْعَظِيم، فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلا أَقْدِر، وَتَعْلَمُ وَلا أَعْلَم، وَأَنْتَ عَلاّمُ الغُيوبِ، اللّهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ-(((( وَيُسَمِّي حَاجَتَهُ ))))))– خَيْرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، عَاجِلِهِ وَأَجِلِهِ فَاقْدُرْهُ لِي وَيَسِّرْهُ لِي ثُمَّ بَارِكْ لِي فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ شَرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاصْرِفْهُ وَاصْرِفْنِي عَنْهُ وَاقْدُرْ لِي الْخَيْرَ حَيْثُ كَانَ ثُمَّ أَرْضِنِي بِهِ.

Allahumma innee astakheeruka bi’ilmik, wa-astaqdiruka biqudratik, wa-as-aluka min fadlikal-‘azeem, fa-innaka taqdiru wala aqdir, wata’lamu wala a’lam ,wa-anta ‘allamul ghuyoob, allahumma in kunta ta’lamu anna hazal-amr ((((say your need)))) khayrun lee fee deenee wama’ashee wa’akibati amree fakqurhu lee, wayassirhu lee, thumma barik lee feeh, wa-in kunta ta’lamu anna hazal-amr sharrun lee fee deenee wama’ashee wa’aqibati amree fasrifhu ‘annee wasrifnee ‘anh, waqdur liyal-khayra haythu kan, thumma ardinee bihi.

*Ma'ana:*
Ya Allah! Ina neman zabinka domin iliminka, kuma ina neman Ka ba ni iko domin Ikonka, kuma ina rokonka daga falalarka Mai girma; domin Kai ne mai iko ni kuwa ba ni iko, kuma Kai ne Masani, ni kuwa ban sani ba, kuma Kai ne masanin abubuwan fake. Ya Allah! Idan ka san cewa wannan al’amari((((( sai ya ambaci bukata tasa ))))))alheri ne gare ni a cikin addinina, da rayuwata, da kuma karshen al’amarina a wata rayuwar; da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa Ka kaddara mini shi, kuma Ka saukake mini shi, sannan Ka albarkance ni a cikin sa. Kuma idan Ka san wannan al’amari sharri ne gare ni a cikin addinina, da rayuwata da karshen al’amarina a wata ruwayar; da magaggaucin al’amarina da majinkircinsa – Ka kawar da shi daga gare ni, kuma Ka kawar da ni daga gare shi, kuma Ka kaddara mini alherin a duk inda yake, kuma Ka sanya ni in yarda da shi”.

Yaku bayin Allah Wannan itace fa addu'ar istikhara wacce Annabi ﷺ ya koyar yanzu kuma za muyi bayaninta daki daki insha Allahu.
*BAYANIN YADDA AKE YIN ISTIKHARA*
Da farko dai Ita sallar istikhara bata da wani ke'bantaccen lokaci da akace dole sai a lokacin mutum zeyi a'a duk lokacin da wani al'mari ya bijirowa mutum da safe ne ko da rana da yamma ne ko da daddare dukkan waɗannan lokutan ya halatta mutum yayi sallar neman zabin Allah a cikinsu, dai sai kuma wani al'amari ya bijirowa muttm kuna yana bukatar ya nemi zabin Allah a cikin lamarin to ya halatta yayi sallar istikharar domin neman zabin Allah

:- *NIYYA* k**ar yadda muka sani a cikin shahararren hadisin Amirul muminin Sayyadin umar ɗan khad'd'ab cewa manzon Allah yace dukkan ayyuka basa yiwuwa/tabbatuwa sai da niyyoyinsu. To k**ar hakane itama sallah istikhara bata tabbatuwa sai da niyya. Bayan mutum yayi niyyar sallar istikhara sai yaje yayi alwala k**ar yadda yake sallah bata ingantuwa sai da alwala, Amma idan mutum yana da alwala a lokacin da yake son yin istikharar kawai zeyi sallar ne babu bukatar sai ya sake sabuwar al'wala.

:- *SALLAH* Mutum zeyi Sallah Raka'a biyu.

:- *LOKACIN DA AKE YIN ADDU'AR:*
Ana karanta addu'ar istikharan Bayan an idar da sallah, sannan kuma mutum ze iya karanta addu'ar istikharar bayan ya gama karatun tahiya lokacin daya kammala salatul ibrahim kafin ya yiya sallama.

:- *KAFIN MUTUM YA FARA ADDU'A* Zai fara da yabo da kirari ga Allah madaukakin sarki, Sannan sai yayi salatul ibrahim daga nan sai yayi addu'ar istikharar bayan ya kammala addu'ar sai ya rufe addu'ar da Salati ga Manzon Allah ﷺ Salatul ibrahim mutum zeyi.

:- *IDAN MUTUM YANA HALIN TSARKI* to ya jira har sai ya samu tsarki k**ar me haila, jinin haihuwa dasauransu. baya halatta ayi sallar sai ana da cikakken tsarki. Amma idan ana tsoron Abinda za'ayi istikharar akan sa zai ku'bucewa kuma ana halin rashin tsarki to adaidai lokacin sai a nemi zabin Allah ta hanyar yin Addu'ar kawai ba tare da anyi sallar ba.

:- *IDAN MUTUM BE HADDACE ADDU'AR BA* Babu laifi ya rubuta a wani abin yana Kallon addu'ar yana karantawa Amma a haddace addu'ar shine yafi.

:- *IDAN MUTUM BE IYA KARANTA RUBUTUN LARABCIN BA* Babu laifi ya karanta addu'ar da hausa Amma a karanta da larabcin shine yafi.

:- *KASKANTAR DA KAI WAJEN NEMAN ZABIN ALLAH* ana so mutum ya dukufar da kansa wajen neman zabin ubangijinsa ya ajiye zabin zuciyarsa kada ya rinjayar da abinda yafi so yayin istikharar.

:- *SANYA YAQINI* ana so mutum ya sanya yaqini cewa lallai ubangiji zai datar dashi akan abinda shine mafi alkhairi a gare shi.

:- *TATTARA ZUCIYARSA YAYIN ADDU'AR* ana so mutum ya tattara zuciyarsa a lokacin fara addu'ar tare da tadabburin (hakaito ma'anonin) abin da addu'ar ta kumsa.

:- *HANYAR DA MUTUM ZAI GANE ZABIN ALLAH* mutum zaiji ɗaya daga cikin al'amuran da yayi istikharar yafi kwanta masa a cikin ransa kuma za'a iya daukan dan lokaci kafin yaji hakan, sabida haka Ba mafarki mutum zeyi a nuna masa zabin nasa ba Kamar yadda wasu suke faɗa, a'a kawai abin da yake shine mafi alkhairi mutum zaiji yafi kwanta masa a ransa zaiji yafi nutsuwa daga cikin abubuwan daya nemi zabin, misali idan yaji abin ya fice a ransa bayan yayi addu'ar to kawai sai abar al'amarin, idan kuma yaji abin yayi matukar kwanta masa a cikin ransa shikenan sai ya rinjarayar da abin. idan kuma beji ya karkata a ɗaya daga cikin abubuwan biyu ba Sai ya sake istikharar haka zai tayi har zuwa lokcin da zabin mahaliccinsa ya bayyana agareshi.

:- *BABU LAIFI MUTUM YAYI ISTIKHARA SAMA DA SAU ƊAYA* Babu laifi a maimaita istikhara fiye da sau ɗaya idan yayi istikharar kuma be samu tabbaci a cikin zuciyar tasa ba, babu wani adadi da shari'a ta iyakance da ake yin istikhara.

Sannan yaku yan uwa kusani soyayyar manzon Allah ﷺ

Baa iya baki takeba dole said munyi koyi dashi. Munyi aiki da abnda y koyar


allah. Ya datar damu akan sunnah annabi ﷺ

Wallahu A'alam

ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ , ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.

Matar farko tana rike matsayin ta ne in har ta zama macen arziki a gidan auran ta.Idan macen kirki ce ita koda an auro w...
16/06/2025

Matar farko tana rike matsayin ta ne in har ta zama macen arziki a gidan auran ta.
Idan macen kirki ce ita koda an auro wata bazata samu fuskar da zata raina ta ba.

Amma idan har baki zama macen arziki na kirki ba.
Bakya masa biyaya
Bakya girmamasa.
Sai wulakanci baya jin dadin zama dake, kawai zaman hakuri yake yi dake.
Idan ya auri wata macen sai ya samu abinda yake so a wajan wancan,ki sani dole zaki ga banbanci saboda ko yaro ne wajan da ake kyautata masa yake zuwa.

Amma ina son ki sani ke ce sanadin daya dawo miki hakan.
Ki zama macen kirki a gidan auran ki,ki zama macen da mijinta zai kara aure bawai don kin gaza ba.

©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

Kina tak**ar idan kince wa Namiji yayi hakuri k**ar kin zubar da ajin ki ko? Akwai matan da duk abinda zai haɗa su da mi...
16/06/2025

Kina tak**ar idan kince wa Namiji yayi hakuri k**ar kin zubar da ajin ki ko? Akwai matan da duk abinda zai haɗa su da mijin su ko kuma saurayin su,sunfi karfin su Bada hakuri,kuma har alfahari sukeyi da hakan,wai a shirmen tunanin su baiwa Namiji hakuri gazawa ce kuma zubar da aji ne,Wanda wannan karatun sam shirme ne a cikin sa.

Dole a rayuwa ko kina so ko bakya so, namiji shugaba ne a gare ki,idan abu ya haɗa ku kalmar yi hakuri nan babu abinda zai rage ki dashi illa ma ya daga miki darajar ki,mata masu wayo koda sune da gaskiya s**anyi saurin cewa mijin su ko saurayin su,su bashi hakuri hakan na kara masu soyayyar mace a zuciyar sa,kuma sai yaji kunya,zaiyi tunani yaga fa cewa shine ya miki laifi amma kin saukar da kanki kince masa yayi hakuri,idan mai ganewa ne zaki ga ya kiyaye gaba,zai kiyiye abinda zaina b'ata miki rai kuma.

Namiji tamkar jariri ne duk macen da zata iya tafiyar dashi,tsab zata mallake sa bawai ta hanyar asiri ba.

Wannan girman kai da kika sakawa zuciyar ki na kinfi karfin baiwa namiji hakuri kima cire sa daga kanki tun wuri,domin hakan bazai haifar miki da komai ba,saima rage miki kimar ki a gun miji.

©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rayuwar aure posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rayuwar aure:

Share