ULT MEDIA

ULT MEDIA Media News Company
Breaking News// Sports// Political Program and Entertainment 📲

Wannan wajen da kuke Gani Shi ake Kira da Suna Tofa ( L,E,A.).Ma'ana Wato Ma'aikatar Ilimi ta Karamar Hukumar Tofa.A Dai...
01/01/2026

Wannan wajen da kuke Gani Shi ake Kira da Suna Tofa ( L,E,A.).

Ma'ana Wato Ma'aikatar Ilimi ta Karamar Hukumar Tofa.

A Dai-Dai lokacin Mike fama da fafutukan Neman samawa Yara kyakykyawan Mahali da Ajujuwa tare da kayan koyo da ko yarwa irin Nazamani wadanda zasu taimakawa Yara su fahimci karatuttukan su.

Saigashi abin ya fice kansu bama Malaman Nasuba Hatta su kansu Masu Ruwa da tsaki wajen Ganin Ilimi ya tafi yanda ya kamata Basu samu Nutsuwa irin wacce Ma'aikaci ya kamata yasamu domin godanar da aikinsa ba.

To natakaice muku magana Wannan Wake Babu da abin da yayi K**a in bada wajen ....domin kuwa ko tagogi Babu ballantana Azo batun kofofi Babu baton sauran kayayyakin da yakamata domin Adana duk wani Abu Mai Mashimmanci.

Ult Media.

Kwankwaso bai taɓa siyar da kadara don takarar siyasa ba, sai akan Abba. Ban taɓa ganin tsananin ɓacin ran Kwankwaso ba ...
29/12/2025

Kwankwaso bai taɓa siyar da kadara don takarar siyasa ba, sai akan Abba. Ban taɓa ganin tsananin ɓacin ran Kwankwaso ba sai ranar da Court of Appeal ta rushe zaben Abba. Kwankwaso bai taɓa neman alfarma a wajena ba sai akan Abba. - Inji Ja'afar - Ja'afar

Ult Media

DA DUMI-DUMI: Gwamna Abba Yusuf na Jihar Kano zai sauya sheka daga NNPP zuwa APC a makon farko na watan Janairu, kamar y...
29/12/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamna Abba Yusuf na Jihar Kano zai sauya sheka daga NNPP zuwa APC a makon farko na watan Janairu, kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.

Gwamna Yusuf, wanda ya rasa 'yan majalisar NNPP 25 daga cikin 27 na majalisar, zai koma APC ba tare da tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban NNPP, Rabiu Kwankwaso ba, wanda ya ki amincewa da wannan mataki.

Bugu da kari, Gwamna Yusuf ya kuma yanke shawarar sadaukar da mataimakinsa, Aminu Abdulsalam, wanda za a tsige don share fagen takarar mataimakin gwamnan APC a zaben gwamna na 2023, Murtala Sule-Garo a matsayin sabon mataimakin gwamna.

Ult Media

23/12/2025

Kadan daga cikin yadda take gudana kenan filing wasa na Sani Abacha fake JIHAR Kano
Yayin da Mai Girma Gwamna yake kaddamar jami'an tsaron jiha..

Shugaban Kasa Ahmad Bola Tinibu yace za'adinga yin kwajin gwaya kafin daukar duk wani Dan Kasa aiki.Meye Ra'ayinkuULT ME...
23/12/2025

Shugaban Kasa Ahmad Bola Tinibu yace za'adinga yin kwajin gwaya kafin daukar duk wani Dan Kasa aiki.

Meye Ra'ayinku

ULT MEDIA

TSOFAFFUN SHUGABANNIN AL'UMMA A JAMHURIYA TA FARKO,RESHEN TSOHUWAR DAWAKIN TOFA SUNYABAWA GWAMNAN JIHAR KANO ALHAJI ABB ...
23/12/2025

TSOFAFFUN SHUGABANNIN AL'UMMA A JAMHURIYA TA FARKO,RESHEN TSOHUWAR DAWAKIN TOFA SUNYABAWA GWAMNAN JIHAR KANO ALHAJI ABB KABIR YUSUF BISA BIYAN KANSILOLI DA CIYAMOMI HAKKINSU DA SUKE BIN JIHAR KANO.

Kwamared Balarabe Yusuf Tofa yace a Madadin Gungiyar su,suke Kara jinjinawa Mai girma Gwamna bisa Namijin kokarin da yayi wajen biyan wadannan Mutane Hakinsu duba da irin Dawainiyar da s**ayi da Al'umma.

Balarabe Yusuf ya Kuma nemi Mai Girma Gwamna da yatuna dasu saboda suna daga cikin wadanda s**abawa dimokuradiya gudun mawa tundaga JAMHURIYA TA FARKO lokacin IBB .

Yusuf Tofa yace yawancinsu Sun Mutu Amma Har yanzu da akwai wadanda Suke Araye.

ULT MEDIA

MAZAN JIYAAlhaji Tanko yakasai (ya cika shekaru 100)Mutumin daya shekara 100 a duniya kuma yana gabatar da rayuwarsa kam...
06/12/2025

MAZAN JIYA
Alhaji Tanko yakasai (ya cika shekaru 100)

Mutumin daya shekara 100 a duniya kuma yana gabatar da rayuwarsa kamar kowa Alhaji Tanko yana Amfani da kafafen sada zumunta har yanzu K**ar yanda yayiwa bbc bayani

Waye Alhaji Tanko yakasai

Alhaji Salihu Abukakar Tanko Yakasai, OFR, Bahaushen Kano ne sannan kuma Bacambe a asali. Musulmi ne shi kuma mabiyin Ɗariƙar Ƙadiriyya. Gogagge ɗan siyasa, jajirtacce kuma cikakken ɗan kishin ƙasa,

wanda a lokacin da ake yin wannan rubutu, yana da shekaru 75 yana siyasa (1949 – 2025). Yana tsoma bakinsa Alhaji Tanko Yakasai, kamar yadda aka fi saninsa, makarancin Al-Ƙur’ani ne, sannan kuma masanin sauran fannonin addini bakin gwargwado, kuma ɗan jarida. Haka nan ma kuma a fannin karatun zamani ba a bar shi a baya ba, ya kwashi rabonsa kamar yadda wannan rubutu zai tantance.

Alhaji Tanko Yakasai, mutum ne ɗan fafutikar ƙwatar ‘yanci. Da su aka kafa jama’iyyar talakawa ta NEPU, kuma s**a zauna a cikinta daram, tun daga lokacin ƙyanƙyasarta, har zuwa ƙarshen rugujewar jamhuriyya ta farko a Najeriya, wanda hakan ne ya sabauta rugujewar dukkanin wasu jama’iyyun siyasa na wacan lokacin.

Da shi aka yi jamhuriyya ta farko, ta biyu, ta uku da kuma ta huɗu wacce yanzu (2025) ake cikinta. Ya ga juyin mulkin soja na farko, sannan kuma ya ga na ƙarshe a wannan ƙasa ta Najeriya. Yana da gogayayyar fafutikar ƙwatar ‘yanci tun daga gida Najeriya har zuwa ƙasashen ƙetare. Da shi aka samawa Najeriya ‘yanci daga hannun Turawa. Duk wanda ya san wannan suna ‘Tanko Yakasai’, a Najeriya da ƙasashen ƙetare, to a fagen fafutikar ƙwatar ‘yanci ya san shi. Haƙiƙa, akwai darrusan ɗiba a cikin rayuwar wannan bawan Allah.

Wannan tarihi na wannan bawan Allah, an ciro ne daga littafin da shi ya rubuta da hannunsa, wanda aka yiwa take da ‘Tanko Yakasai The Story of Humble Life An Auto Biography’, wanda ya ke juzu’i biyu ne; juzu’in farko yana da shafuka 527, juzu’i na biyu kuma yana da shafuka 487.

Tsawon lokacin da ya ɗauka a yana fafutikar siyasa da ƙwato ‘yancin ɗan’adam, Alhaji Tanko Yakasai ya haɗu da abubuwan da lissafo su ke da matuƙar wahala. Wahalhalu da s**a haɗa da muzantawa, musgunawa, rashin abinci da sha musamman lokacin NEPU, tafiyar ƙasa a cikin mawuyacin hali, da kuma uwa-uba ɗauri, suna daga cikin abubuwan da ya fuskanta kuma ya jure, tare kuma da jajircewa a kan abin ya saka a gaba.

Bincike ya tabbatar da cewa, kusan daga shekarar 1953 zuwa 1986, shi ne ɗan siyasar da aka fi ɗaure wa a duk faɗin Najeriya. Ya sha ɗaure-ɗaure ciki kuma har da zaman ƙiriƙiri. An ɗaure sau uku a zamanin Turawa kafin samun ‘yancin ƙasa, sau uku kuma a cikin jamhuriyya ta farko, sai kuma ɗauri biyu da ya sha a hannun gwamnatin sojoji biyu; shugaba Muhammadu Buhari da kuma shugaba Ibrahim Badamasi Babangida, abin da ya kai adadin ɗaure-ɗauren da ya sha zuwa ɗauruka takwas.

Ya rike mukaman gwamnati da dama kamar haka

1967 – 1971 ya zama kamishinan yaɗa labarai na jahar Kano.

1971 – 1972 ya zama kamishinan ma’aikatar gandun daji, raya karkara da kuma kwafarati (Forestry, Community Dev. and Cooperatives) na jahar Kano.

1972 – 1975 ya zama kamishinan ma’aikatar kuɗi ta jahar Kano.
1973 – 1975 ya zama mamba na hukumar gudanarwar babbar makarantar harkokin ƙasa-da-ƙasa (Nigerian Institute of International Affairs) ta Najeriya.
1979 – 1983 ya riƙe muƙamin mai baiwa shugaban ƙasa shawara da shiga tsakanin majalisar Najeriya.

Allah ya kara masa lafiya da tsawon rai

Mun tattaro bayanan a rumbun ilmi✍️

ULT MEDIA

SIYEN JIRGI MARA MATUKI DAI-DAINE A KANOYa kuke kallon matakin Gwamnatin Kano na sayo Jirgi domin yakar Yan Bindiga Gwam...
04/12/2025

SIYEN JIRGI MARA MATUKI DAI-DAINE A KANO

Ya kuke kallon matakin Gwamnatin Kano na sayo Jirgi domin yakar Yan Bindiga

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana shirin gwamnati na samar da jirage marasa matuki da sauran kayan aiki don sa ido da kuma hanzarta mayar da martani domin kare mazauna yankunan kan iyaka tsakanin Jihohin Kano da Katsina.

Wannan ya na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba.

ULT MEDIA

Da Dumi-Dumi:Tsohon Ministan Tsaron Nijeriya Badaru Abubakar ya karyata jita-jitar da ake yadawa kan murabus dinsaMohamm...
03/12/2025

Da Dumi-Dumi:

Tsohon Ministan Tsaron Nijeriya Badaru Abubakar ya karyata jita-jitar da ake yadawa kan murabus dinsa

Mohammed Badaru Abubakar, ya karyata wani rubutu na boge da ke yawo a kafafen sada zumunta, da ke cewa ya yi murabus ne saboda “ba zai tsaya ya kalli gwamnatin Amurka da ta Shugaba Tinubu suna luguden wuta kan ’yan’uwansu a daji ba.”

A cikin wani sakon martini da ya wallafa a shafinsa na Facebook a Larabar nan 3 ga Disamba, 2025, Badaru ya ce ba shi ne ya fitar da wannan kalaman ba, kuma babu wani wakili ko mai magana da yawunsa da ya taba fadin hakan.

Ya jaddada cewa ainihin dalilan da s**a kai ga murabus dinsa an gabatar da su kai tsaye ga Shugaban kasa, kuma daga baya aka bayyana su ga jama’a ta kafafen yada labarai da shafukan sadarwa na zamani.

Don haka duk wani yunkuri na danganta murabus dinsa da wata magana mai tayar da hankali, ya ce sharri ne tsantsa.

ULT MEDIA /DLC

30/11/2025

ZANGA ZANGA A KARAMAR HUKUMAR TOFA

Yanda Al'ummar kananan hukumomin Tofa da Bakwai s**a fito domin nonawa Duniya Arin Hali da suke ciki na Wahalar Rayuwa.

Mutanen sunce dukkannin alkaryun Garorowan da suke a wannan Nahiya Manoma me sannan da 'yankasuwa.

Sun Kuma Kara da cewa a fannin lafiya basusan Iya adadin Rayukan da aka Rasaba sakamakon Rashin kyawun Hanyar.

Don haka suke Kira ga Gwamnati da ta duba halin da suke ciki.

ULT MEDIA

SHUGABAN KASA YA JANYE YANSANDA DAGA BAWA WASU MUTANE TSARO.Umarnin na shugaban ƙasa ya fito ne daga zama na musamman  d...
23/11/2025

SHUGABAN KASA YA JANYE YANSANDA DAGA BAWA WASU MUTANE TSARO.

Umarnin na shugaban ƙasa ya fito ne daga zama na musamman da ya gudanar da yammacin lahdin nan a Abuja tare da Shugabannin Rundunonin tsaron kasar nan.

A cewar umarnin shugaban ƙasa, daga yanzu dukkan manyan mutane da ke buƙatar kariya za su riƙa neman jami’an tsaro daga rundinar tsaro ta Civil Defence.

Ult Media /Freedom Radio

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ULT MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share