Express Radio Nigeria

Express Radio Nigeria Express Radio 90.3 FM - Gaskiya Dokin Karfe
Tashar Gaskiya, Tashar Jama'a.
(3)

29/07/2026

Sponsored
"Da alama wata Sabuwa ta taso a Jam'iyyar NDC ta jihar Kano, domin Hajiya Hauwa Marke, tazo da wani kurman Baƙin Siyasa"

29/07/2026

Sponsored:

" Wallahi, a yanzu ko Kwankwaso ba zai ce yaya na ne shi a siyasa ba.

Duk wanda ya taɓa Mai Girma Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf, to mu zai gani, kuma za mu tare masa.

— Hon. Ahmad S. Aruwa, Mai Bawa Gwamna Shawara kan Yaɗa Labarai.

Sponsored Don yin koyi ga Gwamnan jihar Kano Excellency Abba Kabir Yusif kan yadda yake bawa Ilmi fifiko, ta sanya Hon. ...
29/07/2026

Sponsored

Don yin koyi ga Gwamnan jihar Kano Excellency Abba Kabir Yusif kan yadda yake bawa Ilmi fifiko, ta sanya Hon. Sabi’u Sulaiman Gwammaja ya bada Tallafin littattafai da kayan karatu ga Daliban Firamare dake Mazabar Gwammaja.

Makarantun da Daliban s**a amfani da wannan Tallafi, sun hadar da Makarantar Firamare ta Dala, Gwammaja Model Primary School da Gwammaja Pilot Primary School.

29/07/2026

Sponsored.

“Babu wani cikakken ɗan Kano da yake jin daɗin abin da Ɗanbilki Kwamanda yake yi a siyasar Kano.”

— Comr. Adamu Abdullahi Karkasara, Babban Mataimaki na Musamman ga DSP Sanata Barau I. Jibrin.

29/07/2026

Sponsored

Muddin Rarara ne zai yi tallan APC a arewa tabbas ba za tayi nasara ba.

Yusuf Dan Mama

29/07/2026

LABARAN EXPRESS 29=7=2026

29/07/2026

EXPRESS NEWS 29=7=2026

Masu unguwannin sun bayyana cewa gidajensu sun zama tamkar ofisoshin 'yan sanda, saboda yawan mutanen da ke zuwa neman s...
29/07/2026

Masu unguwannin sun bayyana cewa gidajensu sun zama tamkar ofisoshin 'yan sanda, saboda yawan mutanen da ke zuwa neman sasanci da warware rikice-rikice. Sai dai sun koka da cewa wasu daga cikin al'umma ba sa girmama aikinsu, lamarin da ke jefa su cikin ƙalubale.

Sun ce a Ƙaramar Hukumar Kumbotso suna da kyakkyawar alaƙa da Shugaban Ƙaramar Hukuma da kuma Jami'in 'Yan Sanda mai kula da yankin (DPO).

Haka kuma, sun bayyana cewa sun kafa ƙungiya domin ƙarfafa haɗin kai da gudanar da ayyukansu tare, duk da cewa suna aiki ne a ƙarƙashin tsarin masarauta da kuma na gwamnati.

Masu unguwannin sun bayyana hakan ne yayin da suke zantawa da wakilin Express Radio 90.3 FM a Jihar Kano, Najeriya Abubakar Sale Yakub.

Sun kuma yi kira ga al'umma da su ba su cikakken haɗin kai wajen magance matsalolin da s**a addabi al'umma, k**ar cin iyaka, rikice-rikicen filaye, da kuma faɗace-faɗacen da ke faruwa tsakanin maƙwabta.

Wani jami’in soja mai muƙamin Kanal, Abdussalam Ude, ya rasa ransa bayan wasu 'yan bindiga sun kai hari gidansa da ke un...
29/07/2026

Wani jami’in soja mai muƙamin Kanal, Abdussalam Ude, ya rasa ransa bayan wasu 'yan bindiga sun kai hari gidansa da ke unguwar Kurudu a Abuja.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, jim kaɗan bayan ya dawo daga wurin aiki.

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa maharan sun yi ƙoƙarin sace Kanal ɗin ko kuma wani daga cikin iyalansa.

A yayin harin ne s**a harbe shi har lahira, yayin da matarsa, direbansa da jami’in tsaronsa s**a samu raunukan harbin bindiga, kuma aka garzaya da su asibiti domin samun kulawa.

Kanal Ude, wanda ya fito daga Jihar Enugu, ya kasance jami’i a Nigerian Army Intelligence Corps, inda ya riƙe muƙamai masu muhimmanci a fannin tattara bayanan sirri da yaƙi da ta’ addanci.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta k**a wata budurwa mai shekaru 25 da ake zargi da yanke al'aurar saurayinta a wani ota...
29/07/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta k**a wata budurwa mai shekaru 25 da ake zargi da yanke al'aurar saurayinta a wani otal da ke unguwar Badawa a Jihar Kano.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:00 na ranar Litinin, bayan samun rahoton aukuwar al’amarin.

Ya bayyana cewa mutumin da abin ya shafa da kuma wadda ake zargin duk ’yan asalin Jihar Jigawa ne, sai dai lamarin ya faru ne a Kano.

A cewarsa, binciken farko ya nuna cewa wadda ake zargin ta zo daga Maigatari da wata wuka, wadda ake zargin ta yi amfani da ita wajen aikata laifin.

Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce bayanan farko sun nuna cewa matar ta shaida wa jami’an tsaro cewa ta aikata hakan ne lokacin da saurayin nata ke barci bayan ya sha maganin ciwon kai.

Ya ƙara da cewa bayan faruwar lamarin, matar ta yi ƙoƙarin kai saurayin zuwa banɗaki domin tsaftace jinin da ya zuba, kafin mutanen da ke kusa s**a gano abin da ya faru tare da sanar da jami’an tsaro.

Dangane da jita-jitar cewa an yi amfani da wani sinadari ko kayan maye kafin aukuwar lamarin, kakakin rundunar ya ce har yanzu babu wata hujja da ke tabbatar da hakan.

Ya ce jami’an ’yan sanda sun samu kwalbar abin sha da ruwa a cikin ɗakin otal ɗin, kuma ana ci gaba da bincike domin gano ko suna da alaƙa da abin da ya faru.

Rundunar ta tabbatar da cewa mutumin da abin ya shafa yana raye kuma yana ci gaba da samun kulawar likitoci a wani asibiti.
A halin yanzu, wadda ake zargin tana tsare a hannun ’yan sanda, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kafin gurfanar da ita a gaban kotu.

Address

No:114 Lamido Crescent Nasarawa G.R.A Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Express Radio Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share