
04/09/2025
Sabon shugaban jamiar ilimi ta zaria farfesa yahya Isa Bunkure ya karbi takarda k**a aiki.
Yayin mika takardar nadinsa akwai karamar ministan ilimi ta tarayya farfesa Suwaiba Ahmad da karamar ministan Abuja Dr Mariya Mahmud Bunkure da kuma Dan majalisar Kanannan hukumoni Rano,Bunkure da Kibiya Rtr Hon kabiru alhassan rurum sun masa fatan alkhairi.
A nasa bangare tsohon gwamna jahar kano kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC ta Kasa Dr Abdullah Umar ganduje ya bayyana cewa an sanya kwarya a gurbinta, kasancewar prof bunkure mutum ne mai ilimi da iya gudinmawar da mulki a karshen ya yi masa fatan samun nasara da jagorancin Allah a cikin lamuran sa.
Farfesa yahya Isa Bunkure ya taba rike shugaban kwalejin ilimi ta saadatu rimi tun daga shekara ta 2017 har zuwa shekara ta 2024 ya kuma zama shugaban jamiar ilimi ta saadatu rimi da a wancan lokacin aka daga likafarta zuwa jamia kafin daga bisa a maida ita kwaleji