08/06/2026
Miji ne ya haɗa solar a gidansa domin ya dinga jin daɗin rayuwa tare da iyalinsa. Kawai sai matar tace tana so ta dinga siyar da pure water, tunda a unguwar ba a samun NEPA sosai. Yace kuma za tayi ciniki sosai.
Sai ya je ya siyo mata leda biyar. Aka gayawa ’yan unguwa ana saida ruwa, cikin ikon Allah aka dinga zuwa ana siya. Baiwar Allah nan ta na ta samun ciniki, har ya kai ana siyar da leda goma sama da haka a rana, kuma fa solar ɗinsa ake kunnawa.
Yanzu da aka fara zafi sai ake samun ciniki sosai, sai mijin yace:
“Yanzu abin da ya kamata muyi, solar nan mu daina kunnawa cikin dare. Karfe 9 na safe idan kika kunna zuwa 4, ruwan yayi sanyi har dare za ki ta ciniki. Tunda ana zafi sai mu ringa kwana a tsakar gida, mu kashe solar kar aiki yayi wa solar yawa ya lalace da wuri.”
Hmm, ba da yini yake a gida ba, iya dare yake dawowa. Kuma yace a kashe solar saboda tayi business da solar da safe. Amma ya sadaukar da jin daɗinsa saboda farin cikinta. Yace:
“Wallahi ban taɓa tambayar ta yadda take da riba ba, ko sau ɗaya ban taɓa cewa ta bani aron biyar ba.”
’Yan uwansa s**a zo yawon Sallah, baya nan zasu tafi sai s**a bugo masa waya. Yace matar ta basu 2k, idan ya dawo zai bata. Tace babu. Yace to ta basu 500 su hau adaidaita su tafi gida. Tace ita fa bayarwa ne ba za tayi ba.
“Ba a wasa da kuɗin business.”
Shi kuma yace an daina anfani da solar sa. Wallahi ba za a ƙara kunna masa solar a saida ruwa ba, sai dai ta sai nata solar.
Shine ta tafi gidan su, yaji jiya. Shi kuma yace ya rantse ba zai je ba, ko sun kirashi, sai tayi wata biyu a gidan su sannan zai je.
Shin hukuncin yayi?