Idon Duniya Reports

Idon Duniya Reports Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Idon Duniya Reports, Broadcasting & media production company, KANO, Kano.

wannan shafi namu mai albarka.Ansamar dashi ne domin fadakarwa,ilimantarwa,nishadantarwa,hade da wayar dakan al-umma tare da dauko muku ingantattun labarai na nan gida da waje,sannan muna da bangaren tallace tallace, wasanni,dss

Idon Duniya ReportsIdd Reports
25/07/2026

Idon Duniya ReportsIdd Reports

Tsohon Ɗan takarar shugabancin Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Hon. Malam Nura Hassan Ungoggo ya fice daga Jam’iyyar APC, y...
01/07/2026

Tsohon Ɗan takarar shugabancin Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Hon. Malam Nura Hassan Ungoggo ya fice daga Jam’iyyar APC, ya koma Jam’iyyar NDC.

Tsohon ɗan takarar shugabancin Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Hon. Malam Nura Hassan Ungoggo, ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar APC tare da komawa Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC). Matakin ya zo ne a wani sabon salo na sauye-sauyen siyasa da ke gudana a jihar Kano.

Aƙalla mutane 10 ne s**a rasa rayukansu, yayin da wasu 12 s**a shiga hannun masu garkuwa da mutane a wasu hare-hare daba...
29/06/2026

Aƙalla mutane 10 ne s**a rasa rayukansu, yayin da wasu 12 s**a shiga hannun masu garkuwa da mutane a wasu hare-hare daban-daban da ake zargin ’yan bindiga ne s**a kai a jihohin Sokoto da Katsina.

Hare-haren sun faru ne duk da ci gaba da farmakin sojoji da jami’an tsaro ke yi, wanda a watannin baya ya yi sanadin kashe ’yan bindiga da dama.

A Jihar Sokoto, ana zargin ’yan bindiga sun kashe limamin wani ƙauye da wasu mazauna biyu tare da yin garkuwa da mutane 12 a harin da s**a kai ƙauyen Illela Dawagare da ke Ƙaramar Hukumar Goronyo.

Mazauna yankin sun ce kimanin ‘yan bindiga 30 ne ɗauke da makamai, suna kan babura tara, s**a kutsa cikin ƙauyen da misalin ƙarfe 12:20 na dare ranar Lahadi, inda s**a shafe kusan mintuna 30 suna harbe-harbe ba tare da ƙa’ida ba.

Wani mazaunin ƙauyen da ya nemi a sakaya sunansa ya ce mutanen ƙauyen sun yi ƙoƙarin kare kansu, amma ƙarfin ’yan bindigar ya fi nasu.

Ya ce: “Sun kashe limaminmu, maƙwabcinsa da wani mazaunin ƙauyen kafin su yi garkuwa da mutane 12, ciki har da mata takwas da maza huɗu.”

An bayyana sunayen waɗanda aka kashe da: Mallam Liman Lawwali Na Ande, Lawwali Na Lami, da Abdullahi Haruna.

Majiyar ta ƙara da cewa bayan sun kashe ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, ’yan bindigar sun kuma yi garkuwa da matarsa da kuma ‘yan’uwansa maza biyu.

Kwana arba’in da bakwai (47) bayan da ‘yan ta’adda s**a sace ɗalibai 42 daga Makarantar Firamare da Ƙaramar Sakandare ta...
29/06/2026

Kwana arba’in da bakwai (47) bayan da ‘yan ta’adda s**a sace ɗalibai 42 daga Makarantar Firamare da Ƙaramar Sakandare ta M***a da ke Ƙaramar Hukumar Askira/Uba a Jihar Borno, iyayensu sun ce suna cikin matsanancin damuwa yayin da suke jiran samun wani labari game da inda ‘ya’yansu suke.

An sace ɗaliban, ciki har da ƙananan yara masu shekara biyu kacal, daga cikin azuzuwansu a ranar 15 ga Mayu, 2026, lokacin da aka kai hari kan al’ummar M***a.

Har zuwa yanzu, babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin satar, kuma babu wanda ya tuntubi iyalan domin neman kuɗin fansa tun bayan aukuwar lamarin.

‘Yan ta’addan Boko Haram sun shafe fiye da shekara goma suna addabar yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, inda s**a kashe mutane, s**a yi garkuwa da su, tare da lalata kadarorin gwamnati da na masu zaman kansu.

Ƙungiyoyin agaji da dama sun yi kiyasin cewa dubban mutane, ciki har da jami’an tsaro, sun rasa rayukansu sakamakon ta’addancin Boko Haram. Haka kuma, daruruwan ‘yan ta’addan sun mutu a hare-haren da jami’an tsaro s**a kai.

Duk da ci gaba da farmakin sojoji a yankin, ‘yan ta’addan na ci gaba da kai hare-hare kan fararen hula da kuma jami’an tsaro.

Makarantun gwamnati na Jihar Kano na fuskantar matsanancin ƙarancin malamai da ɗakunan karatu, inda malami guda ke kula ...
29/06/2026

Makarantun gwamnati na Jihar Kano na fuskantar matsanancin ƙarancin malamai da ɗakunan karatu, inda malami guda ke kula da ɗalibai har 150 a matakin firamare da ƙananan yara (pre-primary), kamar yadda rahoton Ƙididdigar Makarantu ta Shekarar 2024/2025 (Annual School Census – ASC) ya bayyana.

Rahoton ya nuna cewa adadin ɗalibai ga malami a makarantun gwamnati na pre-primary da firamare ya kai 150:1, yayin da a makarantun sakandaren ƙasa (Junior Secondary Schools) ya kasance 50:1, sannan a manyan makarantun sakandare (Senior Secondary Schools) ya kasance 37:1.

A cewar Hukumar UNESCO, ƙa’idar da ta dace ita ce malami guda ya kula da ɗalibai 25 kacal a matakin firamare.

Sai dai Manufofin Ilimi na Ƙasa (National Policy on Education) na Najeriya sun tanadi cewa adadin ya kasance 1:25 a matakin pre-primary, 1:35 a firamare, sannan 1:40 a makarantun sakandare.

Duk da haka, yawancin makarantun firamaren gwamnati, musamman waɗanda ke cikin manyan birane masu cunkoso, suna aiki ne da adadin ɗalibai da ya zarce waɗannan ƙa’idoji saboda yawan ɗalibai da ƙarancin malamai.

Ko da yake an fitar da rahoton ƙididdigar makarantun Kano ne a watan Disambar 2025, Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa shi ne har yanzu sabon rahoton hukuma da ke bayyana halin da fannin ilimi ke ciki a jihar.
Idd ReportsIdon Duniya Reports

Wata malamar makaranta mai shekara 22, Maryam Usman, wadda ke koyarwa a Makarantar Brains Minds Nursery and Primary Scho...
29/06/2026

Wata malamar makaranta mai shekara 22, Maryam Usman, wadda ke koyarwa a Makarantar Brains Minds Nursery and Primary School da ke Ugbamaka-Igah a Ƙaramar Hukumar Olamaboro ta Jihar Kogi, ta rasu bayan da ake zargin mahaifin ɗaya daga cikin ɗalibanta ya jagoranci dukan ta saboda ta hukunta ɗansa.

Lamarin ya fara ne a ranar 17 ga Yuni, lokacin da Maryam ta hukunta ɗalibin bisa laifin rashin ɗa’a a makaranta. A yayin hakan, ana zargin yaron ya faɗi ƙasa kuma ya ji rauni a hannunsa.

Bayan faruwar lamarin, mahaifin yaron, mai suna Ishaq Abdullahi, tare da wasu mutum biyu, ana zargin sun je gidan Maryam inda s**a kai mata hari a ranar. An kuma ce daga baya an sake kai mata hari yayin da take kan hanyarta ta zuwa masallaci.

A cewar ɗan’uwan marigayiyar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, an sake kai wa Maryam hari a ranar 18 ga Yuni tare da wasu ƙarin mutane, lamarin da ya jikkata ta sosai har ta suma.

Ya ce: “Da farko an kai ta wani ƙaramin asibiti, daga bisani aka mayar da ita wani asibiti a garin Okpo. Sai dai duk da ƙoƙarin ceto rayuwarta, lafiyarta ta ci gaba da tabarbarewa har ta rasu da misalin ƙarfe 5:00 na safiyar ranar 25 ga Yuni, 2026.”

Ya yi kira ga Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike tare da tabbatar da cewa an hukunta duk waɗanda ke da hannu a lamarin.

Wani dattijon al’ummar yankin mai suna Drisu ya shaida cewa marigayiyar da iyalan ɗalibin dangin juna ne. Ya ƙara da cewa iyalan biyu sun gudanar da tarurruka da dama domin sasanta lamarin.

Address

KANO
Kano
900001

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Idon Duniya Reports posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share