09/06/2026
Ibrahim Harande Ya Buƙaci Shugabanni da Su Mai da Hankali Kan Matsalolin Jama'a
Shugaban kamfanin iHarande, Ibrahim Yahya Harande, ya soki abin da ya bayyana a matsayin karkatar da hankali daga manyan matsalolin da ke addabar al'umma, bayan kalaman Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, kan rawar da jihar Legas ta taka wajen bunƙasar attajirai irin su Aliko Dangote da BUA.
A wani martani da ya wallafa, Harande ya ce abin takaici ne yadda wasu shugabanni ke mayar da hankali kan batutuwan da ba su da tasiri kai tsaye ga rayuwar talakawa, a daidai lokacin da miliyoyin 'yan Najeriya ke fama da matsalolin tsaro, talauci, rashin aikin yi da tsadar rayuwa.
Ya bayyana cewa ko da akwai muhimmancin tattauna tarihin nasarar manyan 'yan kasuwa da gudummawar da wasu birane s**a bayar ga ci gaban kasuwanci, hakan bai kamata ya mamaye tattaunawar da ya kamata ta fi karkata kan hanyoyin magance matsalolin da ke damun jama'a ba.
Harande ya ce mafi yawan 'yan Najeriya a yau na buƙatar jin matakan da gwamnati ke ɗauka wajen rage raɗaɗin rayuwa, samar da tsaro da kuma buɗe ƙofofin tattalin arziki ga matasa da sauran al'umma.
Ya kuma jaddada cewa lokaci ya yi da za a fara auna shugabanni da irin tasirin ayyukansu ga rayuwar jama'a, maimakon yawan kalamai ko muhawarorin siyasa.
A cewarsa, Najeriya na buƙatar ƙarin aiki da sakamako a aikace, domin fitar da al'umma daga ƙalubalen da suke fuskanta a halin yanzu.
Kalaman Harande na zuwa ne yayin da ake ci gaba da muhawara kan fifikon da ya kamata shugabanni su bai wa matsalolin da s**a fi shafar rayuwar 'Ƴan kasa.