02/04/2026
📰 RIGIMA TA ƘUNNO KAI TSAKANIN . DA F.C. RØMØ UNITED
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.
Rigima ta ɓarke tsakanin . da ƙungiyar F.C. RØMØ United bayan da ƙungiyar ta nemi taimakonsa sakamakon wata bukata da ta taso a gare su.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan ƙungiyar sun roƙi a rage musu wasu kuɗaɗe domin samun sauƙi, musamman duba da cewa suna da magoya baya da za su je domin ƙarfafa musu gwiwa wajen neman nasara.
Sai dai Hon. ya shawarce su da su tsaya da ƙafafunsu, lamarin da ya jawo rashin jituwa tare da ɓullar da cece-kuce a tsakanin ɓangarorin biyu. Wannan mataki ya haddasa fusata a cikin matasan ƙungiyar, inda wasu s**a fara zanga-zanga, yayin da wasu kuma s**a fara wallafa hotuna da saƙonni a shafukan sada zumunta domin nuna rashin jin daɗinsu.
A wani ɓangare kuma, wasu magoya bayan Hon. #*Magaji Sule sun yi zargin cewa ya taba sayawa matasa kayan wasa, ciki har da ƙwallo kan kuɗi kimanin ₦35,000 da kuma rigunan wasa da ake kiyasin darajarsu ta kai ₦94,500. Sai dai ƙungiyar F.C. RØMØ United ta fito fili ta karyata wannan zargi, tana mai cewa ba su da wata masaniya a kan hakan.
Ƙungiyar ta bayyana cewa duk wani tallafi ko gudummawa da aka bayar gare su ana bayyana shi a fili, tare da sunan wanda ya bayar, ko a jikin kayan wasa ko kuma a sanarwa. Saboda haka, sun jaddada cewa babu wani ɗan wasa ko ƙungiya da aka bai wa ƙwallo ko wani tallafi na kuɗin da aka ambata.
Duk da haka, ‘yan ƙungiyar ba su hakura ba. Sun ƙara kira ga . da ya ƙara kula da amanar da aka ɗora masa, musamman dangane da aikin gadar da aka fara amma yake tafiya a hankali.
Sun nuna damuwa cewa aikin ya tsaya cak har tsawon makonni biyu, lamarin da ka iya janyo tsaiko, musamman da yake damina na gabatowa. A cewarsu, matasa ne s**a nemo wannan aiki domin ci gaban al’umma, amma rashin kulawa na iya lalata komai.
Ƙungiyar ta kuma bayyana cewa idan har ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, za su cire tsoro su kai ƙorafinsu har zuwa sakatariya, tare da fara fallasa lamarin a bainar jama’a kan zargin cin amanar jama’a.
A ƙarshe, sun jaddada cewa:
“Sauyi dole ne, In sha Allah.”