19/02/2026
Rikici ya barke yayin naɗa sabon dagacin Madobi a Kano
An samu barkewar rikici a Madobi bayan da aka fara shirye-shiryen naɗa sabon Dagacin Madobi sakamakon rasuwar tsohon dagacin, Alhaji Umaru Mahmud.
Rikicin ya samo asali ne bayan wasu daga cikin masu neman kujerar dagacin sun kalubalanci tsarin da s**a ce Hakimin Madobi, Alhaji Saleh Musa Saleh, ya bi wajen zaben sabon dagacin.
Daya daga cikin masu neman kujerar, Tafidan Madobi, Alhaji Hussain Sarki Aliyu Rabakaya, ya bayyana rashin gamsuwarsa da yadda aka gudanar da tsarin zaben. Ya ce ba a bi ka’idojin al’ada da tsarin da aka saba amfani da su ba wajen zabar wanda zai gaji marigayi dagacin.
Alhaji Hussain, wanda Dakta Usman Sarki Sulaiman ya wakilta, ya jaddada cewa ba za su amince da tsarin da aka bi ba, yana mai zargin cewa an cire sunayen wasu daga cikin masu neman kujerar tare da sanya wasu da ba su dace da tsarin ba.
Sai dai zuwa lokacin hada wannan rahoto, Hakimin Madobi, Alhaji Saleh Musa Saleh, bai fitar da wata sanarwa ko karin bayani ba dangane da zarge-zargen da ake yi masa.