11/04/2026
GWAMNATIN NIGERIA TA FITAR DA JERIN SUNAYEN MUTANE DA KUNGIYOYI DA AKE ZARGIN SUNA DA HANNU A TA'ADDANCIN DA AKEYI A KASAR.
Abuja, Najeriya – Gwamnatin Najeriya ta fitar da jerin sunayen mutane da kungiyoyi 48 da ake zargin suna da hannu wajen tallafawa ayyukan ta’addanci a fadin kasar. Wannan jerin ya fito ne daga Kwamitin Takunkumi na Najeriya (NIGSAC) a ranar Asabar.
Kwamitin ya bayyana cewa, jerin ya kunshi mutane daga sassa daban-daban na kasar da kungiyoyi da ake zargin suna hada-hadar kudi da samar da goyon baya ga ayyukan ta’addanci, ciki har da kungiyoyin Jama’atu Wal-Jihad, Ansarul Sudan (Ansaru), Islamic Province (ISWAP), da Indigenous Biafra (IPOB).
Daga cikin sunayen mutane akwai:
Abdulsamat Ohida, Mohammed Sani, Abdurrahaman Abdurrahaman, Fatima Ishaq, Tukur Mamu, Yusuf Ghazali, Muhammad Sani, Abubakar Muhammad, Sallamudeen Hassan, Adamu Ishak, Hassana Isah, Abdulkareem Musa, Umar Abdullahi, Abdurrahaman Ado, Bashir Yusuf, Ibrahim Alhassan, Muhammad Isah, Salihu Adamu, Surajo Mohammad, Fannami Bukar, Muhammed Musa, Sahabi Ismail, Mohammed Buba, Jama’atu Wal-Jihad, Ansarul Sudan (Ansaru), Islamic Province (ISWAP), Indigenous Biafra (IPOB), Yan Group, Yan Group NLBDG, Adamu Hassan, Hassan Mohammed, Usman Abubakar, Kubara Salawu, Rabiu Suleiman, Simon Njoku, Godstime Iyare, Francis Mmaduabuchi, John Onwumere, Chikwuka Eze, Edwin Chukwuedo, Chiwendu Owoh, Ginika Orji, Awo Uchechukwu, Mercy Ali, Ohagwu Juliana, Eze Okpoto, Nwaobi Chimezie, da Ogumu Kewe.
Kwamitin NIGSAC ya jaddada cewa duk wani mutum ko kungiya da aka fitar a wannan jerin zai fuskanci takunkumi na kudi da sauran matakai na doka, domin hana su yin wani abu da zai taimaka ga ayyukan ta’addanci a Najeriya.
Gwamnatin Najeriya ta kuma yi kira ga jama’a da su kasance masu lura da ayyukan da ake gudanarwa a unguwanni, tare da bayar da rahoto ga hukumomi idan sun sami bayani kan irin waɗannan ayyuka.
NIGSAC ta kuma bayyana cewa wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnati na tabbatar da tsaron kasa da hana samun kudi ga ayyukan ta’addanci a Najeriya.
PLAN B TV.