07/08/2026
Abba Gida Gida ya jagoranci ɗaurin auren ma’aurata 1,500 a Kano
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci ɗaurin auren zawarawa da ’yan mata 1,500 a ƙarƙashin shirin auren gata na Gwamnatin Jihar Kano wanda Hukumar Hisbah ta jihar ke gudanarwa.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a.
Gwamna Abba Gida Gida ya bayyana cewa shirin wani muhimmin mataki ne na tallafa wa marasa ƙarfi, ƙarfafa zaman lafiyar iyali da bunƙasa kyawawan ɗabi’u a cikin al’umma.
Ya ce gwamnatin sa ta ɗauki nauyin dukkanin abubuwan da s**a shafi auren domin rage wa al’umma nauyin kuɗaɗen aure tare da ba wa waɗanda s**a amfana damar fara rayuwar aure cikin mutunci da kwanciyar hankali.
A yayin ɗaurin auren, Gwamnan ya wakilci angon farko inda ya nemi auren amaryar daga hannun waliyyinta, Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II, wanda ya amince da auren bisa koyarwar addinin Musulunci.
Tun da farko, Sarkin Kano ya gabatar da huɗubar Juma’a inda ya yi kira ga sabbin ma’auratan da su gina gidajensu bisa imani, haƙuri, mutunta juna da tausayi.
Babban Kwamandan na Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya ce an tantance dukkan waɗanda s**a ci gajiyar shirin tare da ba su shawarwari kafin gudanar da auren.
Babban Limamin Kano, Farfesa Sani Zahraddeen, ya jagoranci addu’o’in neman albarka da zaman lafiya ga sabbin ma’auratan.
Wasu daga cikin waɗanda s**a amfana sun gode wa Gwamna Abba Kabir Yusuf, suna mai bayyana shirin a matsayin wata dama ta sake fara rayuwa cikin mutunci da fata.