Kano Online News

Kano Online News GASKIYA DA GASKIYA
(3)

“Na rantse da Allah ko ana ha maza ha mata sai mun kayar da Gwamna Abba a 2027. Mu muke da 'yan dangwale masu albarka.”H...
08/06/2026

“Na rantse da Allah ko ana ha maza ha mata sai mun kayar da Gwamna Abba a 2027. Mu muke da 'yan dangwale masu albarka.”

Hon Kamal Mai Unguwa Farawa
(Tsohon mai neman takarar kansila a mazabar Mariri)

NDC: Ba Mu Kafa Jam’iyya Domin A Yi Amfani Da Ita A Watsar Ba — Duk Gudummawar Kuɗi Sai Ta Hannun Jam’iyyaJam’iyyar Nige...
08/06/2026

NDC: Ba Mu Kafa Jam’iyya Domin A Yi Amfani Da Ita A Watsar Ba — Duk Gudummawar Kuɗi Sai Ta Hannun Jam’iyya

Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ta bayyana cewa ba wata jam’iyyar mutum ɗaya ba ce ko kuma wata tafiya ta siyasa da za a yi amfani da ita sannan a watsar.

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Osa Director, ya fitar bayan taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) a Abuja, ya ce jam’iyyar ta sake jaddada cewa ita ce mafi girman iko, kuma duk shirye-shirye, manufofi da naɗe-naɗen gwamnatocin da aka zaɓa a ƙarƙashinta dole ne su kasance cikin tuntuba da jam’iyyar.

Ya ce an kuma kafa kwamitin sulhu na ƙasa domin sasanta membobin da s**a samu sabani, yayin da ake shirin samar da ƙa’idojin da’a ga jami’an jam’iyya da masu neman muƙamai.

Jam’iyyar ta kuma jaddada cewa dole ne a tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da kuɗaɗenta, tare da wajabta wa ‘yan takara bayyana duk wasu kuɗaɗen da s**a samu domin yaƙin neman zaɓe.

NDC ta ƙara da cewa duk gudummawar kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe, ciki har da na takarar shugaban ƙasa da gwamna, dole ne su rika shiga ta asusun da jam’iyyar ta amince da su.

08/06/2026

Ba Ƙofar Mata ba, ko Ƙofar Hanci ne, ka je ka tambayi Mai gidan Mila Road, waye ya bashi takardar Assignment ɗin a gidan Milla ɗin - Ogan Ɓoye, Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa.

'Yan tsohuwar NDC a Jihar Kano sun yi sammacin Kwankwaso a gaban uwar Jam'iyyar ta Ƙasa, don neman a basu kaso 40 cikin ...
08/06/2026

'Yan tsohuwar NDC a Jihar Kano sun yi sammacin Kwankwaso a gaban uwar Jam'iyyar ta Ƙasa, don neman a basu kaso 40 cikin 100 na hakkinsu a Jam'iyyar.

Tarihi: A rana irin ta yau 8 ga June, 2014, Masarautar Kano ta shiga wani sabon babi na tarihinta lokacin da aka sanar d...
08/06/2026

Tarihi:

A rana irin ta yau 8 ga June, 2014, Masarautar Kano ta shiga wani sabon babi na tarihinta lokacin da aka sanar da naɗin Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Dr. Muhammadu Sanusi II, PhD, CON, a matsayin Sarkin Kano na 57 kuma Sarki na 14 cikin Sarakunan Fulani da s**a yi mulki a Masarautar Kano.

Naɗin Mai Martaba ya zo ne bayan rasuwar Marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, CFR, wanda ya shafe shekaru 51 yana jagorantar Masarautar Kano cikin hikima, dattako da haɗa kan al’umma. Bayan zaman tantancewa da shawara daga masu ruwa da tsaki na Masarautar, an amince da naɗin Dr. Muhammadu Sanusi II domin ci gaba da riƙon amanar sarautar da kakanninsa s**a gada.

Kafin hawansa karagar mulki, Mai Martaba ya kasance fitaccen masanin tattalin arziki kuma jagora mai hangen nesa. Ya yi aiki a manyan cibiyoyin kuɗi na ƙasa da ƙasa, sannan ya zama Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), inda ya yi fice wajen aiwatar da gyare-gyare masu muhimmanci a tsarin kuɗi da bankuna.

Tun bayan hawansa karagar mulki, Mai Martaba ya ci gaba da bayar da gudunmawa a fannonin ilimi, tattalin arziki, zaman lafiya, kare haƙƙin mata da yara, da kuma bunƙasa al’umma. Haka kuma ya kasance ɗaya daga cikin fitattun muryoyin gargajiya da ke bayar da shawarwari kan ci gaban Arewa da Najeriya baki ɗaya.

A yau, yayin da ake tunawa da wannan rana mai muhimmanci a tarihin Masarautar Kano, al’umma da dama suna ci gaba da yaba wa gudunmawar Mai Martaba wajen kare martabar Masarautar da kuma jajircewarsa wajen hidimtawa jama’a.

Allah Ya ƙara wa Mai Martaba lafiya, basira, hikima da tsawon rai cikin ɗaukaka da nasara. Allah Ya ci gaba da kare Masarautar Kano da al’ummarta. Amin.

Jami’ar Bayero Kano Ta Karrama Dr. Nasiru Yusuf GawunaJami’ar Bayero Kano (BUK) ta karrama tsohon Mataimakin Gwamnan Jih...
07/06/2026

Jami’ar Bayero Kano Ta Karrama Dr. Nasiru Yusuf Gawuna

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta karrama tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, ta hanyar sanya sunansa ga wata muhimmiyar hanya da ke Sabuwar Harabar Jami’ar (New Campus).

Wannan mataki ya biyo bayan amincewar Majalisar Gudanarwar Jami’ar ta 15 a zamanta na 7 da aka gudanar ranar 15 ga Afrilu, 2026. Jami’ar ta bayyana cewa an dauki wannan mataki ne domin girmama gudunmawar da Dr. Gawuna ya bayar wajen ci gaban ilimi da al’umma.

“Duk wani wanda yace ba zai zabi shugaban ƙasa, ko ni Kawu, ko Kofa ba, to ya sani gwamna Abba Gida Gida yake yiwa tanad...
07/06/2026

“Duk wani wanda yace ba zai zabi shugaban ƙasa, ko ni Kawu, ko Kofa ba, to ya sani gwamna Abba Gida Gida yake yiwa tanadin faɗuwa, saboda duk sakamakon zaɓen da aka samu a zaɓen shugaban ƙasa shi za'a samu a zaɓen gwamna.”

- Sanata Sulaiman Abdurrahman Kawu Sumaila.
(Sanata mai wakiltar yankin Kano ta Kudu)

ADC na zawarcin Gawuna da tikitin takarar gwamnan Kano tare da tallafin kuɗin yaƙin neman zaɓeJam’iyyar African Democrat...
06/06/2026

ADC na zawarcin Gawuna da tikitin takarar gwamnan Kano tare da tallafin kuɗin yaƙin neman zaɓe

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta ƙara kaimi wajen shawo kan tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, domin ya tsaya takarar gwamna a zaɓen shekarar 2027 a ƙarƙashin inuwarta, yayin da jam’iyyar ke ci gaba da ƙoƙarin ƙarfafa tasirinta a muhimman jihohin ƙasar nan.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa, majiyoyi masu karfi kan lamarin sun shaida wa cewa wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar suna gudanar da tattaunawa da fitattun abokan siyasar Gawuna domin rinjayar sa ya amince da karɓar tikitin takarar gwamnan Kano na ADC.

A cewar majiyoyin, jam’iyyar ta yi wa Gawuna tayin wasu manyan tagomashin siyasa, ciki har da ba wa wasu daga cikin mabiyansa damar samun tikitin takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar Kano da kuma Majalisar Wakilai ta Tarayya.

Majiyoyin sun kuma bayyana cewa shugabannin ADC sun bai wa tsohon mataimakin gwamnan tabbacin samar da isasshen tallafin kuɗi domin gudanar da yaƙin neman zaɓensa idan har ya amince ya shiga takarar a ƙarƙashin jam’iyyar.

Rahotanni sun nuna cewa tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, da tsohon jakadan Najeriya, Faruk Yabo, na daga cikin fitattun ’yan siyasar da ke jagorantar yunƙurin jawo Gawuna zuwa jam’iyyar.

Duk da cewa a baya Gawuna ya sha bayyana biyayyarsa da jajircewarsa ga tafiyar Kwankwasiyya, majiyoyin cikin gida sun ce ci gaba da matsin lamba da kuma irin tayin siyasar da ADC ke yi sun sa aka fara sake nazari kan lamarin a tsakanin na kusa da shi.

Ana tuna cewa har yanzu shugabancin ADC na ƙasa bai sanar da wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na takarar gwamnan Kano ba, wanda Ibrahim Khalil da Ibrahim Little s**a fafata a cikinsa.

Majiyoyin jam’iyyar sun ce an jinkirta sanar da sakamakon ne domin bai wa jam’iyyar damar kammala yarjejeniya da Gawuna, wanda ake ganin takararsa za ta ƙara wa ADC ƙarfin fafatawa a jihar.

Gawuna, wanda ya taba zama mataimakin gwamnan Kano kuma ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan adawa masu tasiri a jihar.

Masu nazarin siyasa sun yi nuni da cewa har yanzu yana da dimbin magoya baya a sassa daban-daban na Kano, lamarin da ke sa ya zama abin sha’awa ga jam’iyyun da ke neman fitar da ƙwararren ɗan takara da zai iya ƙalubalantar gwamna mai ci, Abba Kabir Yusuf, a zaɓen da ke tafe.

Haka kuma, an yi ta hasashen cewa Gawuna na daga cikin waɗanda za su iya zama ’yan takarar gwamna a jam’iyyar NDC, kafin jagoran jam’iyyar, Rabiu Musa Kwankwaso, ya zaɓi amininsa na kusa kuma tsohon mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, a matsayin wanda jam’iyyar ke son ya zama mai ɗaukar tutarta.

Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga Gawuna ko shugabannin ADC dangane da rahotannin tattaunawar da ake yi tsakaninsu.

"A da Rabi'u Musa kawai ake kiran Kwankwaso, Wallahi Tallahi ni ne na ba shi shawara ya ƙara sunan garinsu (Kwankwaso) a...
06/06/2026

"A da Rabi'u Musa kawai ake kiran Kwankwaso, Wallahi Tallahi ni ne na ba shi shawara ya ƙara sunan garinsu (Kwankwaso) a gaban sunansa, kuma daga nan ne Kwankwasiyya ta fito, In Ji Tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi U. Ganduje.

Babbar Nasara Ga Matasan Najeriya: Kotu Ta Soke Dakatar da NYCNBabbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Rajist...
05/06/2026

Babbar Nasara Ga Matasan Najeriya: Kotu Ta Soke Dakatar da NYCN

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Rajistar Kamfanoni ta Najeriya (CAC) da ta dawo da rajistar Majalisar Matasan Najeriya (NYCN) tare da mayar mata da dukkan hakkokinta na doka.

Kotun ta kuma ba da umarnin a mayar da Sukubo Sara-Igbe Sukubo da sauran amintattun mambobin Kwamitin Amintattu (BoT) na majalisar zuwa matsayinsu, tare da soke amincewar da aka bai wa Kwamitin Rikon Kwarya (IMC) da aka kafa domin tafiyar da harkokin Majalisar.

Mai shari’a Binta Nyako ta yanke hukuncin ne bayan karar da Sukubo da wasu s**a shigar, suna kalubalantar matakin da CAC ta dauka na soke rajistar NYCN da kuma kafa kwamitin rikon kwarya.

A hukuncinta, Mai shari’ar ta bayyana cewa CAC na da ikon sa ido kan kungiyoyi masu rijista, amma ba ta da ikon tantance wa’adin shugabanni ko maye gurbin shugabancin kungiyar yayin da rikicin ke gaban kotu.

Ta ce matakin da CAC ta dauka na soke rajistar NYCN da kafa kwamitin rikon kwarya ya wuce iyakokin ikon da doka ta ba ta, kuma hakan na iya kawo cikas ga shari’o’in da ke gaban kotu.

Saboda haka, kotun ta soke cire rajistar NYCN, ta umarci a dawo da takardar shaidar rajistarta, tare da rushe Kwamitin Rikon Kwarar da aka kafa.

Haka kuma, ta umurci bangarorin da abin ya shafa su koma matsayin da suke ciki kafin CAC da Ma’aikatar matasa su tsoma baki, har sai Kotun Daukaka Kara ta yanke hukunci kan rikicin da ke gabanta.

Address

Kano
700282

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kano Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share