Kano Online News

Kano Online News GASKIYA DA GASKIYA
(1)

“Sanata Barau Jibrin bai da gogewa wajen iya magana da har zai soki tsarin Kwankwasiyya, ya bari ya gama gogewa a siyasa...
03/11/2025

“Sanata Barau Jibrin bai da gogewa wajen iya magana da har zai soki tsarin Kwankwasiyya, ya bari ya gama gogewa a siyasa da iya magana tukunna. Kuma Kwankwasiyyar ce tayi masa Riga da Wando da Zanin daurawa.”

"Kuma duk wannan sambatun da yakeyi, takarar Gwamna dai a Jihar Kano daga nan har Mahadi ya bayyana tafi karfinsa, sai ya jira."

- Shuaibu Muhd Kwankwason Kabo
(Toshon mai neman takarar Kansila na Mazabar Kabo dake Kabo LG, Kano)

Tsohon mataimakin Gwamnan Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna tare da shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Nentawe Yilwatda a hany...
03/11/2025

Tsohon mataimakin Gwamnan Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna tare da shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Nentawe Yilwatda a hanyarsu ta zuwa Bayelsa domin karɓar Gwamnan jihar zuwa APC.

“Sanyi ya busa, dole Abdullahi Abbas ya fara irin kalaman da ya saba na rashin kan Gado, Abba zai maimaita kujerarsa da ...
03/11/2025

“Sanyi ya busa, dole Abdullahi Abbas ya fara irin kalaman da ya saba na rashin kan Gado, Abba zai maimaita kujerarsa da yardar Allah, kana ji kana gani, ba yadda za kayi.”

- Hon Abdullahi Zubair Abiya
(Mataimakin shugaban Jam'iyyar NNPP na Jihar Kano shiyyar Kano ta tsakiya)

Daga 1999 zuwa 2015, shugabannin Nigeria sun ziyarci fadar White House ta Ƙasar America.
03/11/2025

Daga 1999 zuwa 2015, shugabannin Nigeria sun ziyarci fadar White House ta Ƙasar America.

Fadar Shugaban Ƙasa ta yaba da Kwankwaso kan s**a ga Trump bisa barazanar da ya yi wa NajeriyaGwamnatin Shugaban Ƙasa Bo...
03/11/2025

Fadar Shugaban Ƙasa ta yaba da Kwankwaso kan s**a ga Trump bisa barazanar da ya yi wa Najeriya

Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta yaba wa tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, bisa irin tsayuwarsa wajen s**ar maganganun Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, wanda ya yi barazanar yi wa Najeriya katsalandan ta hanyar soji.

Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Mista Bayo Onanuga, ya bayyana cewa abin da Kwankwaso ya yi alama ce ta kishin ƙasa, inda ya bukaci sauran ’yan adawa su bar siyasa a gefe su haɗa kai wajen kare martabar ƙasar.

A cewarsa: “Mun gode wa Sanata Kwankwaso saboda kishin ƙasarsa. Wannan lokaci ne da ya dace shugabannin siyasa su haɗa kai su kare martabar Najeriya.”

Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya fitar da wata sanarwa inda ya gargadi Trump cewa irin waɗannan maganganu na iya tayar da ƙarin rikice-rikice da tashin hankali a cikin ƙasar.

A cikin rubutunsa a shafin X (Twitter), Kwankwaso ya ce: “Na lura da yadda Shugaba Trump ke ta yin maganganu masu tsanani kan Najeriya, musamman bayan ya sake sanya ƙasarmu cikin jerin ‘ƙasashen da ke da matsala ta addini’. Najeriya ƙasa ce mai cikakken ‘yanci, kuma matsalolin tsaro da muke fuskanta ba su bambanta tsakanin addini, kabila, ko siyasa ba.”

Ya kuma shawarci Amurka da ta taimaka wa Najeriya da fasahar zamani da bayanan sirri wajen yaki da ‘yan ta’adda maimakon yin barazana.

A ƙarshe, ya bukaci gwamnatin tarayya ta ƙara ƙarfafa hulɗa ta diflomasiyya ta hanyar naɗa jakadu da wakilai na musamman a ƙasashen duniya.

Ya ƙara da cewa: “Ya ku ‘yan ƙasa, wannan lokaci ne da ya dace mu haɗa kai a matsayin Ɗaya Ƙasa. Allah Ya taimaki Najeriya.”

Cikin Hotuna:A yau Litinin, 3 ga Nuwamba, 2025, Majalisar Dokokin Jihar Kano ta gudanar da zaman ta na yau da kullum kar...
03/11/2025

Cikin Hotuna:

A yau Litinin, 3 ga Nuwamba, 2025, Majalisar Dokokin Jihar Kano ta gudanar da zaman ta na yau da kullum karkashin jagorancin Rt. Hon. Jibril Isma’il Falgore, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano.

📸 Facebook/Ibrahim Gudaji

Ya ku ka kalli wannan kalamai na shugaban Jam'iyyar APC?
03/11/2025

Ya ku ka kalli wannan kalamai na shugaban Jam'iyyar APC?

Allah Ya yi wa fitaccen jarumin Kannywood, Mato Na Mato, wanda aka fi sani da Malam Nata'ala a cikin shirin Dadin Kowa r...
02/11/2025

Allah Ya yi wa fitaccen jarumin Kannywood, Mato Na Mato, wanda aka fi sani da Malam Nata'ala a cikin shirin Dadin Kowa rasuwa.

02/11/2025

Jawabin Sanata Barau yayin karɓar sama da mutane 1,000 da s**a sauya sheƙa daga jam'iyyar NNPP/Kwankwasiyya zuwa jam'iyyar APC

Kwankwaso ya mayar da martani kan furucin Donald Trump game da NajeriyaTsohon Gwamnan Jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kw...
02/11/2025

Kwankwaso ya mayar da martani kan furucin Donald Trump game da Najeriya

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso (RMK), ya nuna damuwarsa kan yadda Shugaban Amurka, Donald Trump, ke ta yin kalamai masu tsanani kan Najeriya, musamman bayan da ya ayyana kasar a matsayin “ƙasa mai matuƙar damuwa” (country of particular concern).

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sanata Kwankwaso ya jaddada cewa Najeriya ƙasa ce mai cikakken ‘yanci da ikon kanta, wacce ke fuskantar barazanar tsaro daga miyagu a sassa daban-daban na ƙasar. Ya ce wadannan matsalolin tsaro ba su bambanta tsakanin addini, kabila ko jam’iyya, don haka bai kamata a yi musu kallon siyasa ko bambancin ra’ayi ba.

Kwankwaso ya bukaci gwamnatin Amurka da ta mayar da hankali wajen tallafawa Najeriya da sabbin hanyoyi da na’urorin zamani wajen yaƙi da ta’addanci da sauran laifukan tsaro, maimakon yin furuci ko matakai da za su iya ƙara rarraba al’umma.

Haka kuma, ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta duba yiwuwar naɗa jakadu na musamman daga cikin kwararrun diplomasiyyarta domin tattaunawa kai tsaye da gwamnatin Amurka. Ya ce lokaci ya yi da Najeriya za ta kafa jakadu na dindindin a ƙasashen duniya domin kare muradunta da inganta hulɗa ta diflomasiyya.

A ƙarshe, Sanata Kwankwaso ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su tsaya kai da fata wajen kare martabar ƙasa, tare da jaddada cewa lokaci ne da ya dace a rungumi haɗin kai maimakon rarrabuwa.

“Wannan lokaci ne da ya dace mu mayar da hankali kan haɗin kai da ƙasarmu, mu guji duk wani abu da zai raba mu. Allah ya taimaki Najeriya,” in ji RMK.

RESPECT FOR NIGERIA’S SOVEREIGNTY: A Response to Donald Trump’s WarningBy,Comrade Abdullahi Ghali Basaf2nd November, 202...
02/11/2025

RESPECT FOR NIGERIA’S SOVEREIGNTY: A Response to Donald Trump’s Warning

By,
Comrade Abdullahi Ghali Basaf
2nd November, 2025

Recent remarks by former U.S. President Donald Trump warning Nigeria about the alleged persecution of Christians have sparked renewed debate about international respect for national sovereignty. While concern for human rights anywhere in the world is commendable, Mr. Trump’s statement risks violating a foundational principle of global order: the sovereign equality of nations.

The Federal Republic of Nigeria is not a U.S. territory, protectorate, or region it is an independent state and a member of the United Nations since 1960. Under Article 2(1) of the United Nations Charter (1945), “the Organization is based on the principle of the sovereign equality of all its Members.” This means that no country, regardless of its size or power, has authority to dictate or “warn” another sovereign state as though it were under its jurisdiction.

Equally important, Article 2(7) of the Charter provides that “nothing contained in the present Charter shall authorize the United Nations to intervene in matters which are essentially within the domestic jurisdiction of any state.” If even the UN itself is bound to respect this principle, it follows that no individual nation or political figure has the right to interfere in Nigeria’s domestic affairs.

The Atlantic Charter of 1941, one of the moral foundations for the creation of the UN, declared the signatories’ commitment “to see sovereign rights and self-government restored to those who have been forcibly deprived of them.” Ironically, a statement such as Mr. Trump’s stands against this very spirit of self-determination and mutual respect.

INSECURITY in Nigeria Is a National Challenge, Not a Religious War

Nigeria’s internal security challenges banditry, kidnapping, terrorism, and armed robbery are complex and affect all faiths. It is inaccurate and unfair to portray the crisis as a targeted campaign against Christians alone. In the northern regions especially, both Muslim and Christian communities suffer frequent attacks from violent non-state actors who are motivated by criminal and political factors rather than purely religious hatred.

By simplifying the issue into a Christian-versus-Muslim narrative, external commentators risk deepening division, fuelling mistrust, and undermining the national unity that is essential for confronting insecurity. Nigeria’s federal and state governments continue to work albeit with acknowledged challenges to improve security, enhance intelligence cooperation, and rebuild trust among diverse communities.

The UN General Assembly’s Declaration on the Inadmissibility of Intervention in the Domestic Affairs of States (Resolution 2131 [XX], 1965) reaffirms that “no state has the right to intervene, directly or indirectly, for any reason whatever, in the internal or external affairs of any other state.” This principle is not a shield for impunity it is a rule designed to maintain international peace and equality.

When world leaders or former officials publicly issue threats or warnings to other countries, they risk undermining this equilibrium. Constructive engagement through diplomatic dialogue, technical cooperation, and respect for local leadership—is the proper channel for expressing concern over human-rights or security issues.

Nigeria values friendship and cooperation with the United States and all international partners. However, respect must be mutual. Support for peace, security, and human rights in Nigeria should be offered in a manner consistent with international law and with full recognition of Nigeria’s sovereign authority.

The way forward is through collaboration sharing intelligence, supporting economic development, empowering local peace initiatives not through unilateral “warnings” that disregard the equality of nations.

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar tura sojojin Amurka zuwa Najeriya da “makamai” idan gwamnatin Najeriya ta...
02/11/2025

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar tura sojojin Amurka zuwa Najeriya da “makamai” idan gwamnatin Najeriya ta ci gaba da barin kamar yadda ya bayyana kisan Kiristoci da masu kishin addinin Musulunci ke yi. Kamar yadda ya bayana a shafinsa na Truth Social ranar Asabar.

Ya ce idan har Gwamnatin Najeriya ta ci gaba da nuna halin ko in kula, Amurka za ta dakatar da duk wani taimako da tallafi zuwa Najeriya, kuma wataƙila za ta shiga cikin ƙasar da nufin “kakkabe” kungiyar ‘yan ta’adda Musulmi da ke aikata wannan mummunan laifi.

Shugaban ya bayyana cewa ya umarci Ma’aikatar Yaki ta shirya yiwuwar ɗaukar mataki, yana mai cewa idan za a kai hari zai zama cikin “sauri, mai kuma tsanani, kuma mai gamsarwa.”

Address

No. 009 Gidaje Plaza, Zoo Road By Gandun Albasa
Kano
700282

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kano Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share