06/06/2026
ADC na zawarcin Gawuna da tikitin takarar gwamnan Kano tare da tallafin kuɗin yaƙin neman zaɓe
Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta ƙara kaimi wajen shawo kan tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, domin ya tsaya takarar gwamna a zaɓen shekarar 2027 a ƙarƙashin inuwarta, yayin da jam’iyyar ke ci gaba da ƙoƙarin ƙarfafa tasirinta a muhimman jihohin ƙasar nan.
Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa, majiyoyi masu karfi kan lamarin sun shaida wa cewa wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar suna gudanar da tattaunawa da fitattun abokan siyasar Gawuna domin rinjayar sa ya amince da karɓar tikitin takarar gwamnan Kano na ADC.
A cewar majiyoyin, jam’iyyar ta yi wa Gawuna tayin wasu manyan tagomashin siyasa, ciki har da ba wa wasu daga cikin mabiyansa damar samun tikitin takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar Kano da kuma Majalisar Wakilai ta Tarayya.
Majiyoyin sun kuma bayyana cewa shugabannin ADC sun bai wa tsohon mataimakin gwamnan tabbacin samar da isasshen tallafin kuɗi domin gudanar da yaƙin neman zaɓensa idan har ya amince ya shiga takarar a ƙarƙashin jam’iyyar.
Rahotanni sun nuna cewa tsohon gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, da tsohon jakadan Najeriya, Faruk Yabo, na daga cikin fitattun ’yan siyasar da ke jagorantar yunƙurin jawo Gawuna zuwa jam’iyyar.
Duk da cewa a baya Gawuna ya sha bayyana biyayyarsa da jajircewarsa ga tafiyar Kwankwasiyya, majiyoyin cikin gida sun ce ci gaba da matsin lamba da kuma irin tayin siyasar da ADC ke yi sun sa aka fara sake nazari kan lamarin a tsakanin na kusa da shi.
Ana tuna cewa har yanzu shugabancin ADC na ƙasa bai sanar da wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na takarar gwamnan Kano ba, wanda Ibrahim Khalil da Ibrahim Little s**a fafata a cikinsa.
Majiyoyin jam’iyyar sun ce an jinkirta sanar da sakamakon ne domin bai wa jam’iyyar damar kammala yarjejeniya da Gawuna, wanda ake ganin takararsa za ta ƙara wa ADC ƙarfin fafatawa a jihar.
Gawuna, wanda ya taba zama mataimakin gwamnan Kano kuma ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan adawa masu tasiri a jihar.
Masu nazarin siyasa sun yi nuni da cewa har yanzu yana da dimbin magoya baya a sassa daban-daban na Kano, lamarin da ke sa ya zama abin sha’awa ga jam’iyyun da ke neman fitar da ƙwararren ɗan takara da zai iya ƙalubalantar gwamna mai ci, Abba Kabir Yusuf, a zaɓen da ke tafe.
Haka kuma, an yi ta hasashen cewa Gawuna na daga cikin waɗanda za su iya zama ’yan takarar gwamna a jam’iyyar NDC, kafin jagoran jam’iyyar, Rabiu Musa Kwankwaso, ya zaɓi amininsa na kusa kuma tsohon mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, a matsayin wanda jam’iyyar ke son ya zama mai ɗaukar tutarta.
Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga Gawuna ko shugabannin ADC dangane da rahotannin tattaunawar da ake yi tsakaninsu.