Idon Dambatta

Idon Dambatta Fal yaqul khairan

Assalamualaikum Alaikum Warahamatullah !!Jama'ar Annabi Matashi Jabiru Sani Dambatta Yana Chikin wani mayuya chin Hali W...
27/08/2026

Assalamualaikum Alaikum Warahamatullah !!

Jama'ar Annabi Matashi Jabiru Sani Dambatta Yana Chikin wani mayuya chin Hali Wanda ya samu karaya a hannun sa a kwanakin baya, to bayan anyimasa gyara Gyaran Bai yuwu ba har sai da takai takawo tsokar jikin hannun Jabiru ta rube tana ruwa Yanzu a takaice dai Yan uwan sa sun kaishi Asibitin Kashi na Dala inda wannan Asibiti s**a basu tabbacin za'a yimasa aiki, Amma Aikin bazai samu ba sai sun ajje kudi kimanin naira Miliyan Daya da Dubu Dari biyar ₦1,500,000.

Iyayen Jabiru da Yan uwansa basu da wannan kudi saboda masu karamin karfi ne sannan Kuma Duk karfin su ya tafi akan magunguna Shine suke Neman Alummar Annabi da su taimaka musu su sharewa wannan bawan Allah hawaye ba dole sai an samu Wanda zai Bada kudin duka ba Ko da karo karo a haka za'a hada Wannan kudi. Allah ubangiji ya Bada Ikon taimakawa.

Muna Rokon Allah subhanahu wata'ala ya Bashi lafiya da duk Alumma Musulmi Dake Fadi Duniya Allah ya basu lafiya mukuma da muke da lafiya Allah ya Kara mana lafiya da abinda lafiya zata chi Amin ya hayyu ya kayyum.

Domin Neman karin bayani za'aiya tuntubar Wannan kafa Kai tsaye Ta Nomba kamar haka

08104568468
07069614064

IDON Dambatta

SANARWAR MANEMA LABARAI24 GA AGUSTA, 2026KAROTAKAROTA TA CAFKE DIREBAN MOTAR DA YA BUGE JAMI’IN HUKUMAR, YA BAR SHI DA K...
25/08/2026

SANARWAR MANEMA LABARAI

24 GA AGUSTA, 2026

KAROTA

KAROTA TA CAFKE DIREBAN MOTAR DA YA BUGE JAMI’IN HUKUMAR, YA BAR SHI DA KARYEWAKI DABAN-DABAN

Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) ta samu nasarar cafke wani direban mota da ake zargi da yin gudun hijira bayan ya buge wani jami’in hukumar a yayin da yake kokarin kaucewa binciken jami’an KAROTA a sashen Dambatta.

Lamarin ya faru ne ranar Asabar da misalin karfe 3:00 na rana, lokacin da jami’an KAROTA ke gudanar da aikin bincike a yankin Dambatta. A yayin da jami’an ke kokarin tsayar da motar, direban ya yi yunkurin tserewa, inda ya buge Mataimakin Shugaban Tawagar Sintiri (2IC) na tawagar, Malam Nasir Abdullahi.

Bayan bugun, Malam Nasir Abdullahi ya suma, tare da samun raunuka masu tsanani da s**a hada da karyewar kasusuwa daban-daban a jikinsa.

Duk da cewa direban ya samu damar tserewa daga wurin da lamarin ya faru, jami’an leken asiri na KAROTA sun ci gaba da bin sawunsa, har sai da s**a yi nasarar gano inda yake tare da cafke shi.

Daga bisani, an mika wanda ake zargin ga sashen kula da zirga-zirgar ababen hawa na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano da ke Kofar Nassarawa, domin ci gaba da gudanar da bincike da kuma daukar matakin da ya dace na shari’a.

A halin yanzu, Malam Nasir Abdullahi yana kwance a Sashen Kula da Marasa Lafiya Masu Tsananin Ciwo (ICU) na Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad, inda binciken likitoci ya tabbatar da cewa ya samu karyewar kasusuwa guda shida sakamakon raunukan da ya ji a hatsarin.

Hukumar KAROTA na ci gaba da addu’ar samun saukin gaggawa ga jami’in nata, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da yin aiki tukuru wajen tabbatar da bin dokokin hanya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sa hannu:
Abubakar Ibrahim Sharada, ANIPR
Jami’in Hulda da Jama’a (PRO), KAROTA, Jihar Kano

Wasu kafafen yaɗa labarai na Turkiyya sun ruwaito cewa tsohon shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Brazil, Roberto Carl...
18/08/2026

Wasu kafafen yaɗa labarai na Turkiyya sun ruwaito cewa tsohon shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Brazil, Roberto Carlos, ya musulunta.

Rahotannin sun ce Carlos, mai shekaru 53, ya musulunta ne kimanin makonni huɗu da s**a gabata, bayan ya furta Kalmar Shahada a yayin wani taro da Sheikh Jihad Hamada, ɗaya daga cikin fitattun mutane a cikin al’ummar Musulmi a Brazil.

Rahoton ya fito ne daga wasu jaridun Turkiyya da dama, ciki har da Haberler, inda aka bayyana cewa tsohon ɗan wasan Real Madrid da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Brazil ya karɓi Musulunci.

Roberto Carlos ya shafe wani ɓangare na rayuwarsa ta ƙwallon ƙafa yana taka leda a manyan ƙungiyoyi, ciki har da Real Madrid da Fenerbahçe, tare da lashe manyan kofuna a matakin kulob da kuma ƙasar Brazil.

Sai dai har yanzu babu tabbaci kai tsaye daga Roberto Carlos da kansa kan rahotannin cewa ya karɓi Musulunci.

MATASAN NAJERIYA A YAU BA SUNA FITA NEMAN HALAL DON SU TARA DUKIYA BANE…...‎‎Da yawa daga cikinsu suna fita ne domin su ...
18/08/2026

MATASAN NAJERIYA A YAU BA SUNA FITA NEMAN HALAL DON SU TARA DUKIYA BANE…...

‎Da yawa daga cikinsu suna fita ne domin su tsira da rayuwa.

‎A da, matashi yana cewa:

‎“Zan yi aiki, in tara kuɗi, in gina gida, in sayi mota, in fara kasuwanci.”

‎Amma yau, burin wasu ya dawo zuwa:

‎“Ya Allah, yau dai in samu abinda zan ci.”

‎Ba wai matasa sun daina son cigaba bane.

‎Ba wai sun daina mafarki bane.

‎Ba wai basa son su mallaki gida ko su kafa kasuwanci bane.

‎Tsadar rayuwace ta tilasta musu mayar da hankali daga gina rayuwa zuwa tsira daga yau.

‎Ka ga matashi ya tashi da safe ya fita neman halal.

‎Bai san abinda zai samu ba.

‎Amma dole ya fita.

‎Domin akwai abincin da za'a ci.
‎Akwai kuɗin mota.
‎Akwai haya.
‎Akwai wutar lantarki.
‎Akwai kuɗin data.
‎Akwai taimakon iyaye.
‎Akwai ƴan uwa da suke kallonsa a matsayin wanda zai iya taimaka musu.

‎Wani lokacin ma idan ya samu ɗan abin da zai ajiye, sai wata buƙata ta taso.

‎Ya qara ɗauka.

‎Ba don bai san muhimmancin saving ba bane.

‎Sai dai rayuwa ta tilasta masa yayi amfani da abinda ya ajiye.

‎Wannan shine halin da wasu daga cikin matasan Najeriya suke ciki.

‎Suna aiki, amma basa jin kamar suna samun cigaba.

‎Suna samun kuɗi, amma kuɗin bai daɗewa a hannunsu.

‎Suna ƙoƙari, amma kullum akwai wata sabuwar buƙata.

‎Suna murmushi a social media, amma a zahiri suna kuka.

‎Kuma abinda yafi ciwo shine, idan ka kalli wasu daga nesa, zaka iya tunanin basu da wata matsala.

‎Amma baka san sau nawa s**a kwana suna tunanin: “Gobe a ina zan samu?”

‎Duk matashin da yake cikin wannan hali:

‎Kada kaji kunyar ƙoƙarinka.

‎Idan yau abinda kake samu yana ciyar da kaine kawai, ka cigaba.

‎Idan baka iya tara kuɗi sosai ba, kada ka ɗauka gazawar ka ce.

‎Ka cigaba da neman halal.
‎Ka ƙara ƙwarewa.
‎Ka nemi damar da zata ƙara maka samun kuɗi.
‎Ka rage abinda za ka iya ragewa.
‎Kayi haƙuri.
‎Ka riƙe gaskiya.

‎Allah Ya sauƙaƙawa duk matashin da yake fita kullum neman halal. 🤲

‎Comrade Ibrahim ✍

Har yanzu dan takarar APC bai kira ya taya ni murna ba - Gwamna Adeleke na Accord Party a jihar OsunGwamnan Osun, Ademol...
16/08/2026

Har yanzu dan takarar APC bai kira ya taya ni murna ba - Gwamna Adeleke na Accord Party a jihar Osun

Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kira shi ya taya shi murnar sake lashe zaɓen gwamnan jihar. Ya ce nasarar tasa nasara ce ga dimokuraɗiyya da al’ummar Osun.

Adeleke ya ce babu wanda ya yi nasara ko rashin nasara a zaɓen, yana mai fatan babban abokin hamayyarsa na APC, Bola Oyebamiji, zai kira shi ya taya shi murna. Sai dai Oyebamiji bai fito ya taya Adeleke murna ba.

Adeleke ya lashe zaɓen da ƙuri’u 511,067, yayin da Oyebamiji ya samu 444,815. Gwamnan ya ce sakamakon ya nuna amincewar al’ummar jihar da ayyukan gwamnatinsa.

KADA KA SAYAR DA MUTUNCINKA SABODA SIYASAIdan ka san kimarka da darajar kanka, kada ka durkusa wa kowa saboda siyasa, Ko...
15/08/2026

KADA KA SAYAR DA MUTUNCINKA SABODA SIYASA

Idan ka san kimarka da darajar kanka, kada ka durkusa wa kowa saboda siyasa, Ko Ubanka ne dan siyasa, idan ya ki sauraronka, ya raina ka, ko ya dauke ka a matsayin wanda ba shi da wani amfani, to ka watsar dashi, ka rungumi wanda zai martaba ka

Ba dole ba ne ka ci gaba da bin dan siyasa wanda bai daraja ka ba, saboda kawai kana neman wata kujera, kudi ko wata alfarma irin na siyasa a gareshi, shi ma dan siyasar riba yake nema da kai, domin ya gina kansa da iyalansa da 'yan uwansa

’Yan siyasa suna zuwa su wuce, kujeru suna zuwa su wuce. Mulki yana zuwa ya wuce, amma sunanka, mutuncinka da darajarka su ne abubuwan da za su kasance tare da kai har tsawon rayuwarka

Siyasa ba ta isa ta sayi mutuncin mutum ba, don haka:
👉 Ku san kimar ku
👉 Ku san ’yancin ku
👉 Ku daina bautar da kanku saboda siyasa
👉 Ku mutunta ’yan siyasa, amma kada ku mayar da kanku bayin 'yan siyasa

Sannan kada ku bari neman kusanci da 'yan siyasa yasa ku rasa darajar da Allah Ya baku

Allah Ya mana muwafaka duniya da lahira

Zaɓen Gwamnan Osun 2026: Manyan ’Yan Takarar Gwamna Sun Kada Ƙuri’unsuAna ci gaba da gudanar da zaɓen gwamnan Jihar Osun...
15/08/2026

Zaɓen Gwamnan Osun 2026: Manyan ’Yan Takarar Gwamna Sun Kada Ƙuri’unsu

Ana ci gaba da gudanar da zaɓen gwamnan Jihar Osun a yau Asabar, 15 ga Agusta 2026, inda masu zaɓe ke kada ƙuri’a a faɗin ƙananan hukumomi 30 na jihar. Manyan masu fafatawa sun haɗa da Gwamna Ademola Adeleke na Accord, Bola Oyebamiji na APC da Najeem Salaam na ADC.

Gwamna Ademola Adeleke ya kada ƙuri’arsa da misalin ƙarfe 8:32 na safe a Ward 2, Unit 9, Sagba Abogunde, Ede North, inda ya bayyana kwarin gwiwarsa na samun nasara.

Ɗan takarar APC, Bola Oyebamiji, shi ma ya kada ƙuri’arsa da misalin ƙarfe 10:35 na safe a Ward 9, Unit 11, Open Space Gantry Sawmill, Ikire, Irewole LGA, tare da bayyana cewa yana da yakinin samun nasara.

Haka kuma, ɗan takarar ADC, Najeem Salaam, ya kada ƙuri’arsa a Ward 4, Unit 13, Iroyin Ayo, Ejigbo, inda ya ce yana da kwarin gwiwar yin nasara idan zaɓen ya kasance cikin adalci.

A halin yanzu, ba a fitar da sakamakon hukuma ba, don haka ba za a iya cewa wani ɗan takara ya yi nasara ko yana kan gaba ba har sai INEC ta fara tattarawa da sanar da sakamakon.

Idon Dambatta

Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya sake yin aure a ranar Juma’a, 14 ga Agusta 2026, a ƙasar Nijar.Jarumin ya ...
15/08/2026

Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya sake yin aure a ranar Juma’a, 14 ga Agusta 2026, a ƙasar Nijar.

Jarumin ya bayyana cewa ya yi sabon auren ne da fatan dacewa da wannan lokaci na watan Rabi’ul Awwal, yana mai neman addu’a daga masoyansa da magoya bayansa domin samun zaman lafiya da dorewar auren.

A wani bidiyo bayan bikin, Zango ya bayyana godiyarsa ga Allah, tare da tura saƙo ga masu s**ar sabon auren nasa.

Jarumin ya ce bai taɓa shiga aure da niyyar ya rabu da matar ba, yana mai cewa rabuwar da ta faru a auren da ya gabata ƙaddara ce.

Zango ya kuma yi kira ga masoyansa da su ci gaba da yi masa addu’a, musamman domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a sabon gidansa.

13/08/2026

Fulbe Duniyaru

Address

Kofar Kudu
Kano
900001

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Idon Dambatta posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share