GMN News Hausa

GMN News Hausa Gaskiya Media Network (GMN) is an independent, digital-first media organization based in Northern Nigeria.
(4)

We produce trusted, public-interest journalism primarily in Hausa, with selected content in English, to inform citizens, amplify community voices.

Akalla mutum 219 ne s**a jikkata yayin rikice-rikicen da s**a barke tsakanin magoya bayan kwallon kafa da ‘yan sanda a s...
31/05/2026

Akalla mutum 219 ne s**a jikkata yayin rikice-rikicen da s**a barke tsakanin magoya bayan kwallon kafa da ‘yan sanda a sassan Faransa bayan da PSG ta lashe gasar Champions League bayan doke Arsenal.

Ministan Harkokin Cikin Gida na Faransa, Laurent Nuñez, ya ce mutane takwas na cikin mawuyacin hali, yayin da jami’an ‘yan sanda 57 s**a samu raunuka a lokacin rikicin.

A cewarsa, an k**a mutum 780 bisa zargin hannu a tashin hankalin, kuma fiye da mutum 450 ne s**a tsare.

Haka kuma wani mutum ya mutu bayan wani hatsari da ya afku a kan wata babbar hanya a Paris da masu tarzoma s**a yi yunkurin toshe ya da daddare.

Mahukunta sun tura jami’an tsaro kusan 6,000 domin tabbatar da tsaro yayin faretin murnar nasarar da za a gudanar kusa da Hasumiyar Eiffel a ranar Lahadi.

GMN News Hausa

Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ƙarƙashin jagorancin Sanata Seriake Dickson ta bayyana tsohon gwamnan Jihar ...
31/05/2026

Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ƙarƙashin jagorancin Sanata Seriake Dickson ta bayyana tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, a matsayin dan takararta na shugaban kasa a zaben shekarar 2027.

An bayyana Obi a matsayin wanda zai yi wa jam’iyyar takara ne a babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja ranar Asabar.

Bayan karbar tutar jam’iyyar, Obi ya sanar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Musa Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa.

Fitowar Obi a matsayin dan takarar NDC ya sake bude gasar neman shugabancin kasa tsakanin manyan 'yan siyasa uku.

Wannan na zuwa ne bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya lashe tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC.

Atiku da Obi dai da farko sun shiga ADC tare da wasu manyan 'yan adawa a watan Yulin 2025 a wani yunƙuri na hada kan adawa domin ƙalubalantar APC a zaben 2027. Sai daga baya Obi ya fice daga ADC tare da Kwankwaso, inda s**a koma NDC.

Shigowar Obi da Kwankwaso cikin NDC tare da magoya bayansu na kungiyoyin Obidient Movement da Kwankwasiyya Movement ya ƙara wa jam’iyyar ƙarfi a fagen siyasa.

GMN News Hausa -

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta cika kusan kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da ta yi...
31/05/2026

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta cika kusan kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da ta yi wa al’ummar jihar cikin shekaru uku a kan mulki.

Ya yi wannan bayani ne yayin da ya karbi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru, wanda ya kai masa ziyarar Sallah a Fadar Gwamnatin Kano a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, ya ce gwamnatin Yusuf ta mayar da hankali kan aiwatar da ayyukan raya kasa da manufofi da s**a shafi rayuwar al’umma kai tsaye a fannoni daban-daban.

Ya bayyana cewa an samu ci gaba a fannonin ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, noma, samar da ruwa, tallafawa matasa da bunkasa tattalin arziki, tare da cewa duk wadannan na nufin inganta rayuwar jama’a da kuma ciyar da Kano gaba mai dorewa.

A nasa bangaren, Sarkin Rano ya yaba wa gwamnan bisa abin da ya kira manyan nasarori cikin shekaru uku, inda ya ambaci kammala hanyoyi mai tsawon kilomita biyar a Rano, Kibiya da Bunkure, da kuma ci gaban aikin ruwa na Kaluwaiwai.

GMN News Hausa

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin ta kasa (NGF) kuma gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa gwamnoni na ...
30/05/2026

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin ta kasa (NGF) kuma gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa gwamnoni na nazarin yiwuwar ɗaga mafi ƙarancin albashin ƙasa zuwa Naira 100,000, k**ar yadda jaridar Punch ta rawaito.

AbdulRazaq ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce hauhawar farashi, tsadar rayuwa da matsin tattalin arziƙi da ma'aikata ke fuskanta ne s**a sa ake duba batun.

Ya ce gwamnatocin jihohi na tattaunawa da gwamnatin tarayya da kuma ƙungiyoyin ƙwadago domin cimma matsaya kan sabon tsarin albashi da zai inganta rayuwar ma'aikata tare da tabbatar da cewa jihohi za su iya ɗaukar nauyin biyan albashin.

A cewarsa, manufar ita ce ƙara ƙarfin sayen kayan masarufi na ma'aikata tare da bai wa gwamnatoci damar ci gaba da aiwatar da ayyukan raya ƙasa da hidimomin jama'a.

A halin yanzu, mafi ƙarancin albashi a Najeriya na tsaye ne a kan naira 70,000 a wata, yayin da wasu jihohi ke biyan fiye da hakan.

GMN News Hausa -

Rundunar sojin kasarnan ta ce dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su tare da kas...
30/05/2026

Rundunar sojin kasarnan ta ce dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su tare da kashe 'ƴan ta'adda'biyar a wasu hare-haren da s**a kai a jihohin Zamfara da Katsina.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar 29 ga Mayun 2026.

A cewar sanarwar, a Jihar Zamfara dakarun sun ceto mutanen ne a yankin Bagega zuwa Kawaye da ke ƙaramar hukumar Anka bayan wani samame ta sama da rundunar ta kai kan maɓoyar 'yan ta'adda da ke yammacin dajin Bagega.

Mutanen da aka ceto sun fito ne daga ƙananan hukumomin Maga, Gummi, Zuru, Wasugu, Bukuyyum da Anka da ke jihohin Zamfara da Sokoto, bayan sun shafe makonni da dama a hannun masu garkuwa da mutane.

Rundunar ta ce an ba su kulawar lafiya kafin a mayar da su ga iyalansu.

Haka kuma, a wani samame ta daban a yankunan Maradun da Gidan Dan Jaja na Zamfara, sojojin sun yi artabu da 'yan ta'adda inda s**a kashe biyu daga cikinsu tare da lalata sansanoninsu.

Rundunar ta kuma ƙwato wasu bindigogi da aka ƙera a gida da kuma babura hudu da ake zargin masu laifin na amfani da su wajen gudanar da hare-hare.

A Jihar Katsina kuwa, dakarun sun tare wasu 'yan ta'adda a yankunan Ruwan Godiya da titin Sayaya da ke ƙaramar hukumar Matazu yayin da suke kan hanyarsu ta kai hari.

Bayan musayar wuta mai zafi, sojojin sun kashe 'yan ta'adda uku tare da kwato babura da wasu harsasai.

GMN News Hausa -

Jam’iyyar PDP tsagin Kabiru Tanimu Turaki ta tsayar da tsohon shugaban Najeriya Goodluck Ebele Jonathan a matsayin ɗan t...
30/05/2026

Jam’iyyar PDP tsagin Kabiru Tanimu Turaki ta tsayar da tsohon shugaban Najeriya Goodluck Ebele Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027.

Jam’iyyar ce ta sanar da hakan bayan ta wallafa takardar shaidar tsayawa takarar Goodluck Jonathan a babban zaɓen ƙasar na 2027.

Farida Umar, Mataimakiyar sakataren yaɗa labaran jam'iyyar PDP ɓangaren Turaki ta ƙasa ta kuma shaida wa BBC batun tsayar da Jonathan a matsayin wanda zai kara da shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

Lamarin ya biyo bayan canjin wurin gudanar da taronta na ƙasa da jam’iyyar ta shirya a Abuja a yau Asabar, 30 ga watan Mayu, bayan da ‘yan sanda s**a hana mambobinta shiga A Class Hotel, wurin da aka fara tanada domin gudanar da taron.

Daga bisani jam’iyyar ta sauya wurin taron cikin gaggawa, inda aka kammala shi cikin ƙanƙanin lokaci.

A wajen taron, an gabatar da matakin tsayar da Jonathan, wanda aka ce ya samu goyon bayan manyan jiga-jigan ɓangaren Turaki na jam’iyyar.
...Asalin hoton,
Rahotanni sun ce an mika takardar shaidar tsayawa takara ga Fred Agbedi, wanda ya karɓa a madadin tsohon shugaban ƙasar, yayin da manyan mambobi irin su Prof. Jerry Gana, Tanimu Turaki da Adolphus Wabara s**a halarci taron. Jam’iyyar ta ce duk da taƙaddama da cikas, za ta ci gaba da shirinta na siyasa domin tunkarar zaɓen 2027.

Tun dai lokacin da jam'iyyar ta bayyana cewa ta tattance Jonthan har zuwa lokacin da ta tabbatar da cewa shi ta tsayar a matsayin ɗan takararta ba, ba a ji ta bakin tsohon shugaban ƙasar ba akan ko ya yarda zai sake tsayawa takara a shekarar 2027 ko a'a

Jonathan dai yayi shugabancin ƙasar daga shekarar 2010 zuwa 2015.

Shine shugaban ƙasar da aka taɓa kayarwa a kan mulki kuma ya amince da kayarwar da aka yi masa.

Shin da Gaske ne, Sanata Rufa'i Sani Hanga, shi ne zai zama dan takarar mataimakin gwamna a jihar Kano, bayan da aka ayy...
30/05/2026

Shin da Gaske ne, Sanata Rufa'i Sani Hanga, shi ne zai zama dan takarar mataimakin gwamna a jihar Kano, bayan da aka ayyuna Dr. Nasiru Yusuf Gawuna wanda zai maye kujerar a Kano ta tsakiya.

Kuna ganin hadin Comrd. Aminu Abdussalam Gwarzo da Rufa'i Sani Hanga a matsayin yan Takarar Gwamna a Kano, zai sa jam'iyar NDC ta samu nasara?

Ku bayyana mana ra'ayoyinku - GMN News Hausa -

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya fahimci irin sadaukarwar da iyalai s**a yi a shekarun baya-bayan nan inda kuma ya bayyana f...
29/05/2026

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya fahimci irin sadaukarwar da iyalai s**a yi a shekarun baya-bayan nan inda kuma ya bayyana fatansa na samun ci gaba a Najeriya.

Ya kuma ce har yanzu tsaro na ka gaba a manufofin gwamnatinsa yayin da ƙasar ke ci gaba da tunkarar ƙalubale gadan-gadan kuma ana samun ci gaba yana mai bai wa ƴan Najeriya tabbacin cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin ƴan Najeriya suna harkokinsu ba tare da zullumi ba.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a jawabinsa na bikin shekara uku kan mulki inda ya ce gwamnatinsa ba ta kai ga magance matsalolin ƙasar ba amma sun dasa tubalin samun ci gaba.

Ya ce aikin da ke gabansu shi ne tabbatar da cewa al'ummar Najeriya sun amfana daga sauye-sauyen da gwamnatinsa ke yi.

Shugaban ya kuma ce gwamnatinsa za ta ci gaba da tabbatar da cewa farashin kayan masarufi da ya sauka tun 2023/2024 bai tashi ba.

Ya kuma ce yana aiki don rage kuɗin sufuri kasancewar masu ababen hawa na mayar da motocinsu zuwa masu amfani da iskar gas da motoci masu amfani da lantarki.

GMN News Hausa

Yau shugaba Tinubu ya cika shekaru 3 da fara jagorantar Najeriya, wane abu kuka fi ribata a mulkinsa? - GMN News Hausa
29/05/2026

Yau shugaba Tinubu ya cika shekaru 3 da fara jagorantar Najeriya, wane abu kuka fi ribata a mulkinsa? - GMN News Hausa

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya sanar da zaɓar Kwamared Aminu Abdussalam G...
29/05/2026

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya sanar da zaɓar Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo a matsayin wanda zai yi wa jam'iyyar NDC takarar gwamna a zaɓen 2027.

Kwankwaso ya faɗi haka ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na X inda ya ce Dakta Nasiru Yusuf Gawuna kuma zai nemi kujerar sanata don wakiltar al'ummar Kano ta Tsakiya.

Ya ce an ɗauki matakin bisa gaskiya da biyayya da kuma ƙwarewa - ɗabi'un da har yanzu ginshiƙai ne a ci gaba da haɗin kan jam'iyyarmu da kuma Kwankwasiyya.

Saarwar ta zo ne bayan shafe kwanaki ana tattaunawar sirri a tsakanin mambobin Kwankwasiyya da kuma tuntuɓar manyan ƴan siyasa.

Kwamared Gwarzo ya sauka daga muƙaminsa na mataimaki gwamnan jihar Kano a watan Maris sak**akon rikicin siyasa tun bayan da gwamna Abba Kabir Yusuf ya fice daga NNPP ya koma jam'iyyar APC mai mulki.

GMN News Hausa

Address

Media House Plaza Sani
Kano
700101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GMN News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share