31/05/2026
Akalla mutum 219 ne s**a jikkata yayin rikice-rikicen da s**a barke tsakanin magoya bayan kwallon kafa da ‘yan sanda a sassan Faransa bayan da PSG ta lashe gasar Champions League bayan doke Arsenal.
Ministan Harkokin Cikin Gida na Faransa, Laurent Nuñez, ya ce mutane takwas na cikin mawuyacin hali, yayin da jami’an ‘yan sanda 57 s**a samu raunuka a lokacin rikicin.
A cewarsa, an k**a mutum 780 bisa zargin hannu a tashin hankalin, kuma fiye da mutum 450 ne s**a tsare.
Haka kuma wani mutum ya mutu bayan wani hatsari da ya afku a kan wata babbar hanya a Paris da masu tarzoma s**a yi yunkurin toshe ya da daddare.
Mahukunta sun tura jami’an tsaro kusan 6,000 domin tabbatar da tsaro yayin faretin murnar nasarar da za a gudanar kusa da Hasumiyar Eiffel a ranar Lahadi.
GMN News Hausa