DDL Hausa

DDL Hausa Media News Company

Domin kawo muku ingantattun Labarai da Kuma tsage gaskiya duk dacinta. DDL Hausa Tashar Al'umma.
(1)

YANZU-YANZU: Ka Dakatar da manufar ka: A hir dinka, Najeriya kasa ce mai cikakken yancin gashin kanta, Sakon Kungiyar Ta...
07/11/2025

YANZU-YANZU: Ka Dakatar da manufar ka: A hir dinka, Najeriya kasa ce mai cikakken yancin gashin kanta, Sakon Kungiyar Tarayyar Afirka ta AU ga Trump.

YANZU-YANZU: Najeriya ta yi Asarar Naira Tiriliyan N2.8 a cikin mako guda bayan barazanar Shugaba Trump na kai hari Naje...
07/11/2025

YANZU-YANZU: Najeriya ta yi Asarar Naira Tiriliyan N2.8 a cikin mako guda bayan barazanar Shugaba Trump na kai hari Najeriya

Takardun bashin Gwamnatin Tarayyar Najeriya sun fadi a kasuwannin duniya a ranar Litinin, bayan da tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai harin soji a kan Najeriya, idan har gwamnatin kasar ba ta dauki matakan gaggawa wajen tabbatar da kariya ga Kiristoci ba.

Rahoton Reuters ya bayyana cewa wannan barazana ta janyo raguwar darajar takardun bashin Najeriya, lamarin da ya haifar da asarar da ta kai kusan Naira Tiriliyan N2.8 cikin mako guda.

Sai dai masana da gogaggun ’yan kasuwa sun bayyana cewa duk da illar farko da wannan furuci ya jawo, tasirin zai iya raguwa a cikin makonni masu zuwa, musamman idan gwamnati ta dauki matakan sassauta fargaba a kasuwannin duniya da wajen masu zuba jari.

DA DUMI-DUMI: Almajiran Shaikh Zakzaky sun yi jerin gwano na Allah-wadai kan barazanar TrumpƳan Shi’a almajiran Shaikh I...
07/11/2025

DA DUMI-DUMI: Almajiran Shaikh Zakzaky sun yi jerin gwano na Allah-wadai kan barazanar Trump

Ƴan Shi’a almajiran Shaikh Ibrahim Zakzaky sun gudanar da jerin gwano na Allah-wadai kan barazanar da tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na kai hari kan Najeriya. Masu zanga-zangar sun bayyana cewa wannan batu yunƙuri ne na mamaye Najeriya da kuma wawurar albarkatun ƙasar.

Rahoton ya nuna cewa ƴan’uwan Musulmi sun fito zagaye jim kaɗan bayan kammala Sallar Jumu’a a Kano, inda s**a yi kira ga gwamnatin Najeriya ta tashi tsaye wajen kare martabar ƙasa da albarkatunta.

Sun kuma buƙaci al’umma su kasance a faɗake, domin kare Ƙasa daga duk wani abu da zai iya haifar da rikici ko tayar da fitina.

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammadu Saad Abubakar III yau ...
07/11/2025

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammadu Saad Abubakar III yau Juma'a a fadar A*o Rock da ke Abuja

Me kuke fatar wannan ganawa ta haifar?

Mun saka ido a Najeriya kan barazanar Amurka, muna bibiyar komai, inji shugaban kasar Rasha.
07/11/2025

Mun saka ido a Najeriya kan barazanar Amurka, muna bibiyar komai, inji shugaban kasar Rasha.

07/11/2025

YANZU-YANZU: An Barke da zanga-zangar Adawa da shirin kawo harin Amurka a Najeriya.

Wasu ‘yan kishin Najeriya sun fara gudanar da zanga-zangar lumana kan rahotannin da ke cewa Amurka na shirin kai harin soji a Najeriya.

07/11/2025

Wasu 'yan bîndīga da ba a san ko su wane ne ba, sun kashê mutum biyu sannan sun yi awon gaba da mutum uku a ƙauyen Sarkin Noma da ke kusa da garin Kadarko a yankin Ƙaramar Hukumar Keana, Jihar Nasarawa.

Majiyarmu ta ce, harin ya auku ne a daren da ya gabata.

AN KUMA: Nnamdi Kanu ya rubutawa Trump wasika, ya zargi gwamnati da aikata kisan kare ɗangi a Kudu maso GabasA daidai lo...
07/11/2025

AN KUMA: Nnamdi Kanu ya rubutawa Trump wasika, ya zargi gwamnati da aikata kisan kare ɗangi a Kudu maso Gabas

A daidai lokacin da ake shirin sauraron shari’arsa a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja yau, shugaban ƙungiyar IPOB da ke tsare, Mazi Nnamdi Kanu, ya rubuta wasika zuwa ga Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump.

A cikin wasikar, Kanu ya yi zargin cewa ana gudanar da “kisan kare ɗangi na ɓoye” a kan al’ummar Kirisitoci da ke yankin Kudu maso Gabas na Najeriya.

Ya kuma bayyana goyon bayansa ga duk wani mataki da gwamnatin Amurka za ta ɗauka kan Najeriya domin, a cewarsa, “kare rayukan mutanen da ake zalunta da gangan”.

Wasikar ta zo ne yayin da ake cigaba da cece-kuce kan halin da al’ummar yankin ke ciki, da kuma korafin da Kanu ke yi na cin zarafi da tsangwama daga jami’an tsaro.

TIRKASHI: Bama-bamai da harsasai ba su san addini ko ƙabila ba – ShettimaMataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya c...
07/11/2025

TIRKASHI: Bama-bamai da harsasai ba su san addini ko ƙabila ba – Shettima

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce kalubalen tsaro da Najeriya ke fuskanta na buƙatar haɗin kai tsakanin ’yan ƙasa gaba ɗaya.

Ya bayyana cewa hare-haren ta’addanci da tashin bam ba su bambanta tsakanin Musulmi ko Kirista, ko kuma tsakanin mai arziki da talaka.

Shettima ya jaddada cewa lokaci ya yi da ’yan Najeriya za su tashi tsaye su haɗa kai domin kawo ƙarshen ta’addanci da rikice-rikice a ƙasar.

“Tsaro na buƙatar haɗin kai, domin harsasai da bama-bamai ba su san addini ko ƙabila ba.”

TIRKASHI: Da Addinin Musulunci Mallakin Uban Wasu Ne, Da Tuni Sun Fitar da Mutane Daga Ciki Tare da Hana Wasu Shiga Addi...
07/11/2025

TIRKASHI: Da Addinin Musulunci Mallakin Uban Wasu Ne, Da Tuni Sun Fitar da Mutane Daga Ciki Tare da Hana Wasu Shiga Addinin — In Ji Ibrahim D. Isma’il

Jarumin fina-finan Hausa na Kannywood, Ibrahim D. Isma’il, ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu mutane ke ɗaukar addinin Musulunci tamkar mallakinsu, suna ƙoƙarin fitar da wasu daga ciki tare da tsoratar da waɗanda ke sha’awar shiga addinin.

Jarumin ya ce, ya fahimci cewa Musulunci addini ne na kowa da kowa, amma akwai wasu da ke amfani da kaifin harshe da munanan halaye da zasu iya jawo mutane su guje masa, ko kuma su hana masu sha’awa shiga cikinsa.

Ya jaddada cewa addinin Musulunci addini ne na sauƙi, hikima, kyakkyawan hali da tsarin da zai jawo mutane soyayya ga addini, ba tsangwama ko ƙyashi ba.

Ibrahim ya kuma yi kira ga al’umma su rika nuna Musulunci ta halayensu masu kyau domin hakan shi ne babban hanyar jan hankalin mutane su fahimci gaskiyar addini ba tare da ƙiyayya ko nuna bambanci ba.

YANZU -YANZU :sanyin safiyar nan zanga-zanga ta sake barkewa a Amurka, dubban mutane suke ta kiran da a sauke Donald Tru...
07/11/2025

YANZU -YANZU :sanyin safiyar nan zanga-zanga ta sake barkewa a Amurka, dubban mutane suke ta kiran da a sauke Donald Trump.

Cin zarafin Wakilin NTA ya tada ƙura a YobeCin zarafin da Babban Jami’an tsaro (CSO) na Gwamnan Yobe,  CSP Yakubu Zakari...
06/11/2025

Cin zarafin Wakilin NTA ya tada ƙura a Yobe

Cin zarafin da Babban Jami’an tsaro (CSO) na Gwamnan Yobe, CSP Yakubu Zakari Deba ya yi ga wakilin Talabijin NTA da ke Damaturu, Babagana Kolo a harabar Majalisar Dokokin Yobe da ke Damaturu a ranar Alhamis ya tada ƙura.

Address

Kano

Telephone

+2348118797344

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DDL Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share