DDL Hausa

DDL Hausa Media News Company

Domin kawo muku ingantattun Labarai da Kuma tsage gaskiya duk dacinta.
(4)

DDL Hausa Tashar Al'umma. 08118797344

Youtube 👉 https://youtu.be/pSlKL-pFDfk?si=8ZCcIJ_k_MgOvm8l

DA DUMI-DUMI: An Zargi Shugaban Jami'ar FCAPT ta Kano da Gwanjon manyan Taraktoci, da Daukar ’Ya’yansa Aiki ba Bisa Ka’i...
18/08/2025

DA DUMI-DUMI: An Zargi Shugaban Jami'ar FCAPT ta Kano da Gwanjon manyan Taraktoci, da Daukar ’Ya’yansa Aiki ba Bisa Ka’ida ba

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban Kwalejin Noma ta Tarayya da ke Kano (Federal College of Agricultural Produce Technology – FCAPT), Dr. Yusha’u Muhammad Gwaram, na fuskantar zarge-zarge masu nauyi na yiwa kansa gwanjon taraktoci da motar makarantar, tare da daukar ’ya’yansa aiki a kwalejin ba bisa ka’ida ba.

Bincike ya nuna cewa duk da ya rage masa kasa da watanni biyu ya sauka daga kujerarsa, shugaban ya mayar da hankali wajen baiwa wasu malamai da ma’aikata kwairi, alhali kuma daya daga cikin ’ya’yansa da ya dauka aiki yana ci gaba da kauracewa wajen aikinsa.

Wata majiya mai tushe ta shaidawa kamfanin dillancin labarai cewa akwai wani asusun banki da ake karbar kudade daga hannun dalibai ta hanyar da ba ta dace ba.

Sai dai a nasa bangaren, Dr. Gwaram ya musanta duka zarge-zargen, inda ya ce ma’aikatan da ke neman bata masa suna ne ke yada irin wadannan rahotanni.

Shi ma Rejistar makarantar, Malam Waziri Umar, ya yi karin haske, inda ya ce duk wani gwanjon da aka gudanar, ko na taraktoci ko na motocin hawa, an yi shi bisa ka’ida.

Game da zargin ’ya’yan shugaban makarantar kuwa, ya ce Ahmad – daya daga cikinsu – yana zuwa aiki, har ma sun hadu da shi kwanan nan a makarantar. Ita kuma ’yar tasa mace tana ci gaba da karatun digiri tare da izinin hukumar makarantar na tsawon shekaru biyu, sannan idan bukatar hakan ta taso, za a iya kara mata lokaci.

A nasa bangaren, Shu’aibu Umar Idris, wanda ya bayyana kansa a matsayin mai magana da yawun shugaban makarantar, ya ce za su dauki matakin shari’a idan aka sake wallafa wani labari da zai bata musu suna.

An tsamo gawawakin mutane 44 da s**a rasu bayan bus kin STM Niger ya fada cikin ruwa a jamhuriyar Benin
18/08/2025

An tsamo gawawakin mutane 44 da s**a rasu bayan bus kin STM Niger ya fada cikin ruwa a jamhuriyar Benin

YANZU-YANZU: Kungiyar Kiristoci ta Arewacin Najeriya, ta yabawa Malam Nuhu Ribadu bisa k**a jagororin Yan ta'addan Kungi...
18/08/2025

YANZU-YANZU: Kungiyar Kiristoci ta Arewacin Najeriya, ta yabawa Malam Nuhu Ribadu bisa k**a jagororin Yan ta'addan Kungiyar ANSARU.

DA DUMI-DUMI: Wata Kungiya ta nemi Majalisar Dattawan Najeriya da ta tsige shugaban kasa Bola Tinubu akan karagar Mulki ...
18/08/2025

DA DUMI-DUMI: Wata Kungiya ta nemi Majalisar Dattawan Najeriya da ta tsige shugaban kasa Bola Tinubu akan karagar Mulki

Wata babbar ƙungiyar farar hula daga Jihar Rivers ta rubuta ƙorafi ga Majalisar Dattawan Najeriya, tana kira da a fara shirin tsige Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa abin da ta kira aikata babban laifi a tafiyar da mulki.

Ƙungiyar ta zargi Shugaban Ƙasar da karya Kundin Tsarin Mulkin Najeriya, inda ta ce matakan da ya ɗauka a Jihar Rivers sun nuna dakatar da tsarin dimokuraɗiyya a jihar, tare da naɗa Gwamnan rikon kwarya, lamarin da ta bayyana a matsayin cin zarafin dimokuraɗiyya da kuma karya doka.

A cikin wasikar da ta aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ƙungiyar ta bukaci Majalisar Dattawa da ta gudanar da cikakken bincike tare da ɗaukar mataki bisa kundin tsarin mulki.

Kungiyar ta ce “Abin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aikata a Jihar Rivers ya saba wa tanade-tanaden tsarin mulki. Wannan ba wai kawai rashin adalci ba ne, har ila yau ya na iya zama barazana ga dorewar dimokuraɗiyya a Najeriya. Don haka, muna kira da a ɗauki matakin gaggawa domin kare martabar kundin tsarin mulki da kuma ƙasar gaba ɗaya.”

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar ta gargadi Majalisar cewa idan ba a ɗauki mataki ba, hakan zai iya buɗe ƙofa ga keta dokokin ƙasa da karya dimokuraɗiyya a sauran jihohin ƙasar.

Sai dai har yanzu ba a samu martanin Shugaban Majalisar Dattawa ko kuma Fadar Shugaban Ƙasa ba kan wannan kira na neman tsige Shugaban Ƙasar.

YANZU-YANZU: Shugaba Bola Ahmed ya isa birnin Tokyo na kasar Japan Gabannin taron TICAD na 2025, Ambasada Hideo MATSUBAR...
18/08/2025

YANZU-YANZU: Shugaba Bola Ahmed ya isa birnin Tokyo na kasar Japan Gabannin taron TICAD na 2025, Ambasada Hideo MATSUBARA, jakadan Japan mai kula da TICAD ya tarbe shi.

KU JIRA SAI TA ALLAH TAZO Bayan Majiyar mu ta tuntubi jarumi Ali Nuhu, inda ya karyata labarin mutuwarsa da kansa.Ali Nu...
18/08/2025

KU JIRA SAI TA ALLAH TAZO Bayan Majiyar mu ta tuntubi jarumi Ali Nuhu, inda ya karyata labarin mutuwarsa da kansa.

Ali Nuhu ya shaidawa DDL Hausa cewa an saba yada irin wannan jita-jitar duk shekara.

Gwamnan Jahar Kebbi Dakta. Nasir Idris kauran Gwandu, Na Cigaba Da Alhinin Babban Rashin Da Jahar Kebbi Tayi A Jiya ne A...
18/08/2025

Gwamnan Jahar Kebbi Dakta. Nasir Idris kauran Gwandu, Na Cigaba Da Alhinin Babban Rashin Da Jahar Kebbi Tayi

A Jiya ne Allah yayi ma Mai Martaba Sarkin Zuru Major General Sani Sami, Sami Gomo II, Rasuwa.

Muna Rokon Allah Yasa Mutuwa tazamo hutu gareshi

Allah yajikansa da Rahama.

DARA TA CI GIDA:Masu Garkuwa Da Mutane Sun Yi Hadari Bayan Sun Karɓi Kuɗin Fansa A Jihar Nassarawa A safiyar yau, Farfes...
18/08/2025

DARA TA CI GIDA:Masu Garkuwa Da Mutane Sun Yi Hadari Bayan Sun Karɓi Kuɗin Fansa A Jihar Nassarawa

A safiyar yau, Farfesa Akyala Ishaku ya bayyana cewa yayin da suke hanyarsu ta zuwa aiki, wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi hatsari da motarsu kirar Peugeot 406 dauke da bindigogi da kuma kuɗin fansar da s**a karɓa.

Hatsarin ya faru ne a garin Angwan Mayo, kusa da Karamar Hukumar Kokona a jihar Nassarawa. A cewar Farfesa Ishaku, masu laifin sun tsere daga wurin, amma sun bar kuɗaden da s**a karɓa da bindigogi a cikin motarsu.

Ya kuma bayyana godiyarsa ga jami'an tsaro, sojoji da 'yan sanda, da s**a amsa kiran gaggawa cikin hanzari.

Lamarin na ci gaba da jawo ce-ce-ku-ce a yankin, yayin da ake cigaba da bincike.

Gwamnatin Najeriya ta dauke wa maniyyatan Kiristoci masu son zuwa Ibada Isra‘ila rabin kudin kujeraJaridar Punch
18/08/2025

Gwamnatin Najeriya ta dauke wa maniyyatan Kiristoci masu son zuwa Ibada Isra‘ila rabin kudin kujera

Jaridar Punch

Al'ummar Isra'ila sun gudanar da zanga-zanga mafi girma domin neman gwamnatin ƙasar ta kawo karshen yaƙin Gaza da kuma s...
18/08/2025

Al'ummar Isra'ila sun gudanar da zanga-zanga mafi girma domin neman gwamnatin ƙasar ta kawo karshen yaƙin Gaza da kuma shirinta na mamaye yankin.

📷 Aminiya

Hukumar Kula Da Shige Da Fice Ta Najeriya Ta Tura Wasu Daga Cikin 'Yan Kasar China Da Philipins Zuwa Kasashen Su Bayan K...
18/08/2025

Hukumar Kula Da Shige Da Fice Ta Najeriya Ta Tura Wasu Daga Cikin 'Yan Kasar China Da Philipins Zuwa Kasashen Su Bayan K**a Su Da Yin Damfara A Yanar Gizo

Rashin Lafiya Ta Ci Jikina  Ina Bukatar Taimakon Al'umma, Cewar Malam Nata'ala Na Shirin 'Dadin Kowa'
17/08/2025

Rashin Lafiya Ta Ci Jikina Ina Bukatar Taimakon Al'umma, Cewar Malam Nata'ala Na Shirin 'Dadin Kowa'

Address

Kano

Telephone

+2348118797344

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DDL Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share