DDL Hausa

DDL Hausa Media News Company

Domin kawo muku ingantattun Labarai da Kuma tsage gaskiya duk dacinta. DDL Hausa Tashar Al'umma.
(1)

13/10/2025

Kada Ku Cire Tsammani Daga Nijeriya, Sakon Sanata Akpabio Ga Matasa

ABIN TAUSAYI: Dattijowa Ta Fashe da Kuka Bayan Rashin Ganin Sunan Ɗanta a Cikin Waɗanda Isra’ila Za Ta SakiWata dattijow...
13/10/2025

ABIN TAUSAYI: Dattijowa Ta Fashe da Kuka Bayan Rashin Ganin Sunan Ɗanta a Cikin Waɗanda Isra’ila Za Ta Saki

Wata dattijowa ‘yar asalin Gaza ta fashe da kuka bayan ta kasa ganin sunan ɗanta cikin jerin fursunonin da Isra’ila ta sanar da za ta saki ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wuta.

Dattijuwar ta ce ta shafe shekaru tana jiran dawowar ɗanta tun kafin barkewar yakin, amma yau farin ciki ya koma baƙin ciki bayan sunan ɗan nata bai bayyana cikin jerin ba.

TIRKASHI: Duk Wanda Bai Yi Aiki Ba, Ba Za a Biya Shi Kuɗin Wata Ba — GwamnatiGwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ba za ta...
13/10/2025

TIRKASHI: Duk Wanda Bai Yi Aiki Ba, Ba Za a Biya Shi Kuɗin Wata Ba — Gwamnati

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ba za ta biya kuɗin wata ga duk wani malamin jami’a da bai yi aiki ba ba, sakamakon yajin aikin da ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙasa (ASUU) ta sanar da shiga.

Wannan martani na zuwa ne bayan da ASUU ta bayyana aniyarta ta shiga yajin aikin gargadi na makonni biyu, tana zargin gwamnatin tarayya da gazawa wajen cika alƙawuran da ta dauka, ciki har da yarjejeniyar shekarar 2009 da har yanzu ba a aiwatar da ita gaba ɗaya ba.

Yadda Hamas ke mika Fursunonin 1sra'ila 7 a wani ɓangare na tabbatar da shirin yarjejeniyar zaman lafiya.
13/10/2025

Yadda Hamas ke mika Fursunonin 1sra'ila 7 a wani ɓangare na tabbatar da shirin yarjejeniyar zaman lafiya.

YANZU-YANZU: Isra’ila ta kammala gyara asibiti don karɓar fursunonin da Hamas za ta mikaIsra’ila ta kammala shirye-shiry...
13/10/2025

YANZU-YANZU: Isra’ila ta kammala gyara asibiti don karɓar fursunonin da Hamas za ta mika

Isra’ila ta kammala shirye-shiryenta na musamman a wasu asibitoci domin karɓar fursunonin Isra’ila da Hamas ta ce za ta mika, tare da samar da dakuna na musamman da kulawar likitoci kafin a mayar da su ga ’yan uwansu.

YANZU-YANZU: Isra’ila Ta Saki Falasɗinawa Dubu 2 a Musayar Fursunoni Da HamasRahotanni daga Gabas ta Tsakiya sun tabbata...
13/10/2025

YANZU-YANZU: Isra’ila Ta Saki Falasɗinawa Dubu 2 a Musayar Fursunoni Da Hamas

Rahotanni daga Gabas ta Tsakiya sun tabbatar da cewa, gwamnatin Isra’ila ta saki Falasɗinawa sama da 2,000 da ke tsare a gidajen yarenta, sakamakon yarjejeniyar musayar fursunoni da aka kulla tsakaninta da ƙungiyar Hamas.

Wannan lamari ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan kawo ƙarshen tashin hankali tsakanin ɓangarorin biyu, bayan watanni na rikici da ya jawo asarar rayuka da dama a yankin Gaza.

Majiyoyi sun bayyana cewa an fara mika waɗanda aka saki zuwa iyakar Gaza, inda ake karɓar su cikin murna da hawaye na farin ciki daga iyalansu da sauran jama’a.

Rahoton Zuhair Ali Ibraheem

TIRKASHI: Rogo Ya Karye A Cikin Gaban Wata Mata A Yayin Da Take Rage TarzomaAn garzaya Asibiti da Wata mata a yankin Mar...
12/10/2025

TIRKASHI: Rogo Ya Karye A Cikin Gaban Wata Mata A Yayin Da Take Rage Tarzoma

An garzaya Asibiti da Wata mata a yankin Mararaba dake jihar Nasarawa bayan wani lamari mai ban mamaki da ya faru da ita yayin da take amfani da rogo wajen rage zafi

Rahotanni sun bayyana cewa matar, wacce asalin ta daga Ogoja ce, ta fara amfani da rogon ne bayan ta lullube shi da kwaroron roba. Amma daga baya ta cire kwaroron robar, inda rogon ya karye, wani ɓangare kuma ya makale a cikin jikinta.

Lamarin ya janyo mata matsanancin ciwo, abin da ya sa maƙwabta s**a gaggauta kai ta asibiti domin samun taimakon gaggawa daga likitoci.

TSEGUMI: Jarumin Kennywood KB International Jarumi A Shirin Garwashi.Shin ko kun gane wacce suke tare ?
12/10/2025

TSEGUMI: Jarumin Kennywood KB International Jarumi A Shirin Garwashi.

Shin ko kun gane wacce suke tare ?

Zafafan Hotunan Jarumar Kannywood Momee Gombe Wanda S**a Dauki Hankula A Shafukan Sada ZumuntaWanne Fata Zaku Mata.?
12/10/2025

Zafafan Hotunan Jarumar Kannywood Momee Gombe Wanda S**a Dauki Hankula A Shafukan Sada Zumunta

Wanne Fata Zaku Mata.?

YANZU-YANZU:Ministan Kuɗi, Wale ya FAƊI Sumamme An Garzaya da shi Ƙasar Waje Jinya, Shugaba Tinubu na Ƙoƙarin Maye Gurbi...
12/10/2025

YANZU-YANZU:Ministan Kuɗi, Wale ya FAƊI Sumamme An Garzaya da shi Ƙasar Waje Jinya, Shugaba Tinubu na Ƙoƙarin Maye Gurbinsa

Ministan Kudi da Tsare-Tsaren Tattalin Arziki na Najeriya, Wale Edun, an tabbatar da cewa ya kamu da ciwon shanyewar rabin jiki(stroke) kuma an kai shi ƙasashen waje don samun kulawar likita cikin gaggawa.

Wani babban jami’in gwamnati ya tabbatar da lamarin ga jaridar Sahara Reporters a yau Lahadi, yana mai cewa halin da Minista Edun yake ciki yayi tsanani sosai, duk da cewa yana samun kulawa ta musamman a asibiti a ƙasar waje.

“Lamarin yana da tsanani sosai. Yana iya samun sauki amma ba zai iya komawa bakin aiki ba,” in ji majiyar.

Rahoton ya ƙara da cewa Shugaba Bola Tinubu ya fara nemi wanda zai maye gurbin Edun, musamman ganin yadda matsalolin tattalin arziki da na musayar kuɗi (dollar) ke ƙara taɓarɓarewa a ƙasar.

“Shugaba Tinubu na tattaunawa a ɓoye domin nemo sabon minista cikin gaggawa. nakasar jiki da Edun ya samu mai tsanani ce. Allah ya taimake mu,” in ji majiyar.

TIRKASHI: Ya kamata ‘yan Najeriya su shirya tsaf domin biyan kuɗi don su sake zaɓar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, — In Ji S...
12/10/2025

TIRKASHI: Ya kamata ‘yan Najeriya su shirya tsaf domin biyan kuɗi don su sake zaɓar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, — In Ji Sani Ahmad Zangina

Ɗan siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC, Sani Ahmad Zangina, ya bayyana cewa, idan Allah Ya kai mu shekarar 2027, ya kamata ‘yan Najeriya su shirya tsaf domin biyan kuɗi don su sake zaɓar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bisa la’akari da irin alherin da ya ce shugabancin Tinubu ya kawo wa ƙasar.

A cewarsa, “Alherin Shugaba Tinubu ya shiga kowane lungu da saƙo na Najeriya, daga arewa zuwa kudu, daga gabas har zuwa yamma. Bai kamata mu manta da irin wannan cigaba ba.”

Maganar tasa ta tayar da muhawara mai zafi a tsakanin ‘yan Najeriya, inda wasu ke ganin kalamansa abin mamaki ne a lokacin da ake fama da tsadar rayuwa, yayin da wasu kuma ke cewa yana nuna aminci da goyon baya ga gwamnatin Tinubu.

Shin kuna goyon bayan ra’ayinsa cewa ya kamata a biya kuɗi domin sake zaɓar Tinubu a 2027?

12/10/2025

BIDIYO: Yanzu Yanzu Shugaba Tinubu Ya Sauka Birnin Rome Domin Halartar Taro Kan Tsaro

🎥 NTA News

Address

Kano

Telephone

+2348118797344

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DDL Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share