11/08/2026
Ana zargin Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume Kabo, da hannu wajen k**a da tsare wani matashi mai suna Aliyu Muhammad Haruna, wanda aka fi sani da Babagana, bisa zargin ya bayyana ra’ayinsa kan wasu batutuwan siyasa.
An bayyana hakan ne cikin wata takardar ƙorafi mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Agusta, 2026, wadda aka miƙa wa Sufeto-Janar na Rundunar ’Yan Sandan Najeriya a Hedikwatar ’Yan Sanda da ke Louis Edet House, Abuja.
Takardar ta ƙunshi ƙorafi kan k**awa da tsarewa ba bisa ka’idar doka ba, da kuma zargin amfani da ikon ’yan sanda ba daidai ba wajen k**a matashin.
A cikin ƙorafin, lauyoyin Aliyu Muhammad Haruna sun bayyana cewa:
“Mu ne lauyoyin Mr. Aliyu Muhammad Haruna (Babagana), kuma bisa umarninsa, mun rubuto wannan wasiƙa domin sanar da ku halin da ya dabaibaye k**awa da tsare shi da jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo.”
A cewar takardar, lauyoyin sun yi zargin cewa k**awa da tsare Babagana ya faru ne bisa umarni ko sa hannun Shugaban Karamar Hukumar Kabo, Hon. Lawan Najume Kabo.
LauyoyinLauyoyin sun kuma nemi a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa domin gano halaccin k**awa da tsarewar, yanayin da ya kai ga jami’an ’yan sanda ɗaukar matakin, da kuma rawar da Shugaban Karamar Hukumar ya taka a cikin lamarin.
Takardar ta bayyana Babagana a matsayin ɗan Najeriya, ɗalibi kuma ɗan asalin Jihar Kano, tare da cewa, bisa bayanan lauyoyinsa, ba shi da wani tarihin aikata laifi da ya shafi wannan ƙorafi.
A ranar 3 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo sun je gidan Babagana da ke Gidan Alh. Haruna, Kabo, inda s**a k**a shi tare da kai shi ofishin ’yan sanda.
A cewar Babagana, jami’an sun ɗauki matakin ne bisa umarni ko sa hannun Hon. Lawan Najume Kabo, Shugaban Karamar Hukumar Kabo.
Takardar ta ƙara da cewa Babagana ya taɓa samun rashin jituwa da Shugaban Karamar Hukumar kan wasu batutuwan siyasa da kuma yadda ake gudanar da harkokin ƙaramar hukumar.
Kafin k**a shi, Babagana ya kasance yana bayyana ra’ayoyinsa da rashin amincewarsa da wasu manufofi ko matakan gudanarwa da s**a shafi Shugaban Karamar Hukumar.
A halin yanzu, lauyoyin matashin suna neman a gudanar da bincike domin tabbatar da ainihin dalilin k**awa da tsare shi, da kuma gano ko an yi amfani da ikon ’yan sanda ba bisa ka’ida ba.