DDL Hausa

DDL Hausa DDL Hausa Jarida Ce Mallakin Kamfanin Dandalin Labarai Multimedia Dake Watsa Labarai Cikin Harshen Hausa A Duniya.
(6)

Domin Magana Da Editan Mu, WhatsApp 08118797344

2027: Tinubu ne ya kafa jam'iyyar NDC don ya yi wa ƴan adawa illa - ADCJam’iyyar adawa ta ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bol...
11/05/2026

2027: Tinubu ne ya kafa jam'iyyar NDC don ya yi wa ƴan adawa illa - ADC

Jam’iyyar adawa ta ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma jam’iyyarsa ta APC da hannu wajen kafa sabuwar jam’iyyar NDC domin raunata haɗin kan ƴan adawa a Najeriya.

Zargin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tafka muhawara tsakanin jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

A cewar ADC, kafa jam’iyyar NDC wata dabara ce da aka ƙirƙira domin raba kan masu jefa ƙuri’a ga jam’iyyun hamayya, tare da rage ƙarfin manyan jam’iyyun adawa da ke shirin ƙalubalantar gwamnati mai mulki.

Jam’iyyar ta ce maimakon bunƙasa dimokaraɗiyya ta gaskiya, an kafa sabuwar jam’iyyar ne domin kawo cikas ga haɗin kai tsakanin ƴan adawa.

Sai dai jam’iyyar APC ta musanta zargin, inda ta ce ba ta da hannu wajen kafa jam’iyyar NDC, tare da ƙoƙarin wanke kanta daga zarge-zargen da ADC ke yi.

Tsohon gwamnan Kano, Ibrahim Shekarau, ya zama ɗan takarar bai ɗaya na kujerar Sanatan Kano ta Tsakiya a jam’iyyar All P...
11/05/2026

Tsohon gwamnan Kano, Ibrahim Shekarau, ya zama ɗan takarar bai ɗaya na kujerar Sanatan Kano ta Tsakiya a jam’iyyar All Progressives Congress.

Hakan ya biyo bayan sasancin da gwamnan Kano, Abba Yusuf, ya yi domin kawo ƙarshen rikicin da ya dabaibaye takarar kujerar sanatan yankin.

10/05/2026

Dan Takarar Majalissar Tarayya Na Gwarzo/Kabo A Jam’iyyar APC Hon Fahad Dankabo Ya Bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf A Matsayin Shugaba Adali.

TIRKASHI: Daga Karshe Jarumin Kannywood Musa Mai Sana’a Ya Hadu da Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Mallam Nuh...
10/05/2026

TIRKASHI: Daga Karshe Jarumin Kannywood Musa Mai Sana’a Ya Hadu da Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu

Da Dumi-Dumi: Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja - PantamiTsohon ministan sadarwa na Najeriya Farfesa Isa Al...
10/05/2026

Da Dumi-Dumi: Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja - Pantami

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya Farfesa Isa Ali Pantami ya yi ƙarin haske kan dalilin da ya sa ya taɓa mayar da akwatin zaɓensa zuwa Abuja daga Gombe.

A hirarsa da gidan talabijin na TVC a yau Lahadi, Pantami wanda ɗaya ne daga cikin masu neman tikitin takarar gwamnan jihar Gombe a zaɓen 2027, ya kuma yi tsokaci kan zargin da ake masa na watsi da lamuran jam'iyyar ta APC na tsawon lokaci.

Pantami ya ce ya maida akwatin zaɓensa zuwa Abuja ne a shekarar 2019 saboda muƙamin da ya riƙe na shugaban hukumar NITDA a lokacin, kuma yana daga cikin masu jagorantar abubuwan da s**a shafi bayanan intanet da suke da alaƙa da zaɓen, wanda hakan ya sa ake buƙatar kasancewrasa a birnin tarayyar ƙasar.
Amma ya ce yanzu haka ya maida akwatin zaɓensa jihar Gombe.

A ƴan kwanakin nan dai Pantami ya ɗauki hankalin ƴan Najeriya, tun bayan da jam'iyyarsa ta APC ta amince da miƙa tikitin takarar gwamnan jihar Gombe ga Jamilu Isiyaku Gwamna bisa tsarin masalaha, abin da Farfesan ya yi watsi da shi, inda ya ce zai yaƙi "rashin adalcin da aka yi".

Da aka tambaye shi game da rashin ba da gudummuwa ga harkokin jam'iyyar APC a lokacin da yake riƙe da muƙamin minista, Pantami ya ce ba haka batun yake ba.

Ya ce ya sha bayar da gudummuwar kuɗi ga jam'iyyar a lokuta daban-daban, inda ya yi iƙirarin cewa ko a kwanan nan ya ba da "gudummuwar naira miliyan 50" a yayin babban taron jam'iyar a Abuja, da kuma wata "miliyan 45" a lokacin sabunta rijistar jam'iyyar ta APC.
Shehin Malamin ya ƙara da cewa, ba a taɓa neman wata gudummuwa daga gareshi ya ƙi yi ba.

📸 BBC Hausa

A Ganin Ku Ko Gombawa Za Su Zaɓi Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe A Zaɓen 2027?
10/05/2026

A Ganin Ku Ko Gombawa Za Su Zaɓi Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe A Zaɓen 2027?

Mai neman Takarar Majalisar Tarayya a Gwarzo da Kabo Hon Fahad Muhammad Dankabo Ya samu halartar tantancewa a ofishin ja...
10/05/2026

Mai neman Takarar Majalisar Tarayya a Gwarzo da Kabo Hon Fahad Muhammad Dankabo Ya samu halartar tantancewa a ofishin jam'iyyar APC na kasa.

Me Zaku ce.?

TIRKASHI: Duk da Kin Tsayar da Shi Takarar Gwamna, Al’ummar Yobe na Ci Gaba da Nuna Kauna ga KMTDuk da cewa Gwamna bai t...
10/05/2026

TIRKASHI: Duk da Kin Tsayar da Shi Takarar Gwamna, Al’ummar Yobe na Ci Gaba da Nuna Kauna ga KMT

Duk da cewa Gwamna bai tsayar da shi takarar gwamnan jihar Yobe ba, al’umma musamman matasa na ci gaba da nuna sha’awa da goyon baya ga Kashim Musa Tumsah (KMT), sakamakon yadda suke kallon irin ra’ayoyinsa da hangen nesansa kan ci gaban jihar.

A lokuta da dama, sunan KMT na fitowa a tattaunawar siyasa da ci gaban Yobe, inda wasu ke bayyana shi a matsayin mutum mai sababbin tunani da fahimtar matsalolin zamani da s**a shafi rayuwar al’umma.

Masu bibiyar harkokin siyasa a jihar sun ce KMT ya samu karbuwa ne musamman saboda yadda yake mayar da hankali kan batutuwan tattalin arziki, bunkasa matasa da samar da hanyoyin cigaba mai dorewa.

Wasu daga cikin matasan jihar sun bayyana cewa suna ganin akwai bukatar shugabanci mai anfani da ilimi, kwarewa da dabarun zamani wajen magance kalubalen da Yobe ke fuskanta.

Ko da yake ba lokacin yakin neman zabe ba ne a yanzu, tattaunawa kan makomar shugabanci a jihar na ci gaba da daukar hankali, yayin da jama’a ke bayyana ra’ayoyinsu kan irin shugabannin da suke ganin za su iya kawo sauyi da ci gaba ga Yobe.

Gwamnatin Kebbi ta caccaki Malami game da yunƙurinsa na neman kujerar Gwamnan jihar
10/05/2026

Gwamnatin Kebbi ta caccaki Malami game da yunƙurinsa na neman kujerar Gwamnan jihar

YANZU-YANZU: Masu neman takarar Sanatan Kano ta tsakiya sun janye wa Shekarau'Yan takarkarun Kano ta tsakiya na jam’iyar...
10/05/2026

YANZU-YANZU: Masu neman takarar Sanatan Kano ta tsakiya sun janye wa Shekarau

'Yan takarkarun Kano ta tsakiya na jam’iyar APC sun janyewa tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim shekarau domin tsayawa takarar sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyar APC ta jihar Kano kamar yadda gidan talabijin na ARTV ya rawaito.

Gwamnatin Jihar Kano Ta Bayyana Wasu Kujerun Majalissun Tarayya Da Ba A Cimma Matsaya Ko Yin Sulhu Ba, Cikin Mazabun Da ...
10/05/2026

Gwamnatin Jihar Kano Ta Bayyana Wasu Kujerun Majalissun Tarayya Da Ba A Cimma Matsaya Ko Yin Sulhu Ba, Cikin Mazabun Da Ba a Yi Sulhu Ba Sun Hada Da Kujerar Majalisar tarayya Ta Gwarzo/Kabo, Da Kuma Ta Dambatta/Makoda Da Gezawa/Gabasawa Da Sumaila/Takai Da Bebeji/ Kiru.

Wadannan Sune Kujerun Majalissun Tarayya Da Jam’iyyar APC Bata Tsaida Yan Takara Ba, Sakamakon Rashin Yin Sulhu Tsakanin Yan Takarar,

Address

Kano

Telephone

+2348118797344

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DDL Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share