11/05/2026
2027: Tinubu ne ya kafa jam'iyyar NDC don ya yi wa ƴan adawa illa - ADC
Jam’iyyar adawa ta ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma jam’iyyarsa ta APC da hannu wajen kafa sabuwar jam’iyyar NDC domin raunata haɗin kan ƴan adawa a Najeriya.
Zargin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tafka muhawara tsakanin jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.
A cewar ADC, kafa jam’iyyar NDC wata dabara ce da aka ƙirƙira domin raba kan masu jefa ƙuri’a ga jam’iyyun hamayya, tare da rage ƙarfin manyan jam’iyyun adawa da ke shirin ƙalubalantar gwamnati mai mulki.
Jam’iyyar ta ce maimakon bunƙasa dimokaraɗiyya ta gaskiya, an kafa sabuwar jam’iyyar ne domin kawo cikas ga haɗin kai tsakanin ƴan adawa.
Sai dai jam’iyyar APC ta musanta zargin, inda ta ce ba ta da hannu wajen kafa jam’iyyar NDC, tare da ƙoƙarin wanke kanta daga zarge-zargen da ADC ke yi.