DDL Hausa

DDL Hausa DDL Hausa Jarida Ce Mallakin Kamfanin Dandalin Labarai Multimedia Dake Watsa Labarai Cikin Harshen Hausa A Duniya.
(7)

Domin Magana Da Editan Mu, WhatsApp 08118797344

Ana zargin Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume Kabo, da hannu wajen k**a da tsare wani matash...
11/08/2026

Ana zargin Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume Kabo, da hannu wajen k**a da tsare wani matashi mai suna Aliyu Muhammad Haruna, wanda aka fi sani da Babagana, bisa zargin ya bayyana ra’ayinsa kan wasu batutuwan siyasa.

An bayyana hakan ne cikin wata takardar ƙorafi mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Agusta, 2026, wadda aka miƙa wa Sufeto-Janar na Rundunar ’Yan Sandan Najeriya a Hedikwatar ’Yan Sanda da ke Louis Edet House, Abuja.

Takardar ta ƙunshi ƙorafi kan k**awa da tsarewa ba bisa ka’idar doka ba, da kuma zargin amfani da ikon ’yan sanda ba daidai ba wajen k**a matashin.
‎A cikin ƙorafin, lauyoyin Aliyu Muhammad Haruna sun bayyana cewa:

“Mu ne lauyoyin Mr. Aliyu Muhammad Haruna (Babagana), kuma bisa umarninsa, mun rubuto wannan wasiƙa domin sanar da ku halin da ya dabaibaye k**awa da tsare shi da jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo.”

A cewar takardar, lauyoyin sun yi zargin cewa k**awa da tsare Babagana ya faru ne bisa umarni ko sa hannun Shugaban Karamar Hukumar Kabo, Hon. Lawan Najume Kabo.

‎LauyoyinLauyoyin sun kuma nemi a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa domin gano halaccin k**awa da tsarewar, yanayin da ya kai ga jami’an ’yan sanda ɗaukar matakin, da kuma rawar da Shugaban Karamar Hukumar ya taka a cikin lamarin.

Takardar ta bayyana Babagana a matsayin ɗan Najeriya, ɗalibi kuma ɗan asalin Jihar Kano, tare da cewa, bisa bayanan lauyoyinsa, ba shi da wani tarihin aikata laifi da ya shafi wannan ƙorafi.


A ranar 3 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo sun je gidan Babagana da ke Gidan Alh. Haruna, Kabo, inda s**a k**a shi tare da kai shi ofishin ’yan sanda.

A cewar Babagana, jami’an sun ɗauki matakin ne bisa umarni ko sa hannun Hon. Lawan Najume Kabo, Shugaban Karamar Hukumar Kabo.

Takardar ta ƙara da cewa Babagana ya taɓa samun rashin jituwa da Shugaban Karamar Hukumar kan wasu batutuwan siyasa da kuma yadda ake gudanar da harkokin ƙaramar hukumar.

Kafin k**a shi, Babagana ya kasance yana bayyana ra’ayoyinsa da rashin amincewarsa da wasu manufofi ko matakan gudanarwa da s**a shafi Shugaban Karamar Hukumar.

‎A halin yanzu, lauyoyin matashin suna neman a gudanar da bincike domin tabbatar da ainihin dalilin k**awa da tsare shi, da kuma gano ko an yi amfani da ikon ’yan sanda ba bisa ka’ida ba.

11/08/2026

Ana gab da fara taron ƙasa da ƙasa na Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League) kan tsaro a Abuja.

Manyan baki na cigaba da halara zauren taron na Bola Ahmed Tinibu International Conference Center.

YANZU-YANZU: An Hango Tinubu Yana Tafiya Da Ƙafa Zuwa Ofis Ba Tare da Ayarin Motoci Ba, Lamarin da Ya Sake Tabbatar da M...
11/08/2026

YANZU-YANZU: An Hango Tinubu Yana Tafiya Da Ƙafa Zuwa Ofis Ba Tare da Ayarin Motoci Ba, Lamarin da Ya Sake Tabbatar da Maganganun Shugaban NRS Na Baya

IBY Hausa

GWAMNA INUWA YAHAYA YA GANA DA MINISTAN AYYUKA, KAN AIKIN HANYAR GOMBE-BIUGwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, y...
11/08/2026

GWAMNA INUWA YAHAYA YA GANA DA MINISTAN AYYUKA, KAN AIKIN HANYAR GOMBE-BIU

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙara matsa lamba ga Gwamnatin Tarayya domin a fara aikin hanyar Gombe-Biu, wadda ke cikin babbar hanyar Akwanga–Jos–Bauchi–Gombe–Biu–Maiduguri Super Highway.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, a Abuja ranar Litinin.

A yayin ganawar, gwamnan ya jaddada muhimmancin hanyar Gombe-Biu wajen bunƙasa harkokin noma, kasuwanci, masana’antu da yawon buɗe ido, tare da sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki a Gombe da sauran jihohin Arewa maso Gabas.

Hanyar Gombe-Biu na daga cikin manyan ayyukan more rayuwa da Gwamnatin Tarayya ta amince da su, kuma an riga an gudanar da bikin aza harsashin fara aikin.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ce, bayan kammala aza harsashin, abin da ya rage shi ne ganin an samu ci gaba mai ɗorewa wajen fara aikin gina hanyar baki ɗaya da kuma kammala ta cikin lokaci.

Gwamnan ya kuma nemi a yi la’akari da gina sabbin hanyoyin wucewa ta arewa da kudu na birnin Gombe, domin rage cunkoson ababen hawa a cikin birnin da kuma samar da sauƙaƙƙen haɗi da hanyar Gombe-Biu.

Da yake mayar da martani, Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya bayyana hanyar Gombe-Biu a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bai wa muhimmanci.

Umahi ya ce za a yi la’akari da buƙatar Gwamna Inuwa Yahaya na fara aikin daga wurin da aka gabatar, yayin da aikin ke shirin shiga matakin aiwatarwa.

Ministan ya kuma yaba wa kamfanin Hitech Construction Company, wanda ke kula da aikin, yana mai bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin ƙwararrun kamfanonin gine-ginen manyan ayyukan more rayuwa.

Sanata Umahi ya kuma yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa dagewarsa da jajircewarsa wajen neman ayyukan raya ƙasa ga al'ummar Gombe.

Ya ce tun bayan ziyararsa zuwa Gombe, ya fara ɗaukar kansa a matsayin jakadan jihar, saboda irin ci gaban da ya ce ya gani a ƙarƙashin gwamnatin Gwamna Inuwa Yahaya.

Ministan ya ce:

“Duk inda na je, ina magana ne game da Gombe. Idan kuna son ganin ci gaba na gaskiya da shugabanci mai hangen nesa, ku je Gombe.”

Baya ga hanyar Gombe-Biu, Ministan ya ce ya san irin matsin lambar da Gwamna Inuwa Yahaya ke yi domin a gyara tare da sake gina wasu muhimman hanyoyin da s**a haɗa Gombe da sauran sassan Arewa maso Gabas.

Daga cikinsu akwai Gombe–Bajoga–Potiskum, Gombe–Dukku–Darazo da Gombe–Bauchi.

Waɗannan hanyoyi na da matuƙar muhimmanci ga tattalin arzikin yankin, domin suna haɗa manoma da kasuwanni, al’ummomi da cibiyoyin kasuwanci, tare da bai wa Gombe damar samun sauƙin hulɗa da sauran cibiyoyin tattalin arziki na yankin.

Rahotanni sun nuna cewa kammala waɗannan manyan hanyoyi na iya ƙara bunƙasa kasuwanci da zirga-zirga, tare da buɗe sabbin damar tattalin arziki ga al’ummar Gombe da Arewa maso Gabas baki ɗaya.

Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya za ta gudanar da taron ƙasa da ƙasa kan tsaro a AbujaƘungiyar Ƙasashen Musulmi ta Du...
10/08/2026

Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya za ta gudanar da taron ƙasa da ƙasa kan tsaro a Abuja
Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (The Muslim World League), tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidiah Wa Iƙamatus Sunnah (JIBWIS), za ta gudanar da taron ƙasa da ƙasa kan tsaro a Abuja ranar Talata, da nufin inganta zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da tsaro.

Za a gudanar da taron ne a Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa ta Bola Ahmed Tinubu, inda za a haɗa shugabannin addinai da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna alaƙar da ke tsakanin zaman lafiya, tsaro da cigaban zamantakewa da tattalin arziki.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin ƙaddamar da wani sabon masallaci da aka gina a Abuja, wanda Babban Sakatare Janar na Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya kuma Shugaban Ƙungiyar Malaman Addinin Musulunci ta Duniya, Sheikh Mohammed Bin Abdulkarim Al-Issa, ya jagoranta.

Idris, wanda tun da farko ya tarbi Sheikh Al-Issa a Ɓangaren Shugaban Ƙasa na Babban Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe, tare da raka shi zuwa wurin ƙaddamar da masallacin, ya bayyana ziyarar a matsayin wata shaida ta kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin Nijeriya, Saudiyya da sauran ƙasashen duniya.

Ya ce taron yana zuwa ne a wani muhimmin lokaci da Nijeriya take ci gaba da ƙarfafa tsarin tsaron ƙasa, tare da aiwatar da sauye-sauye da zuba jari da nufin hanzarta cigaban zamantakewa da tattalin arziki.

Ministan ya sake jaddada aniyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da zaman lafiya tsakanin al'ummomi, daidaituwar addinai da haɗin kan ƙasa, yana mai cewa zaman lafiya da tsaro su ne ginshiƙan wadata da zaman lafiyar Nijeriya da Afrika.

Idris ya ce: “Shugaban Ƙasa ya ƙudiri aniyar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ba a Nijeriya kaɗai ba, har ma a faɗin duniya. Wannan wata bayyananniyar shaida ce ta hanyar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yake bi.”

Ya ce Nijeriya, kasancewar ta ƙasa mafi yawan al'umma a Afrika, tana da babban nauyi da ya rataya a wuyan ta na inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin nahiyar, yana mai cewa Nijeriya mai zaman lafiya da tsaro za ta yi tasiri mai kyau a Yammacin Afrika da nahiyar baki ɗaya.

A cewar sa, taron zai samar da wata muhimmiyar kafa da shugabannin addinai da sauran masu ruwa da tsaki za su yi amfani da ita wajen musayar ra'ayoyi da samar da hanyoyin da za su taimaka wajen ƙarfafa zaman lafiya tsakanin al'ummomi, tsaro da fahimtar juna.

Idris ya yaba wa Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya, JIBWIS, Gwamnatin Saudiyya da sauran masu ruwa da tsaki bisa sauƙaƙa ziyarar Sheikh Al-Issa da kuma kafa masallacin.

Ya yi godiya ga Sheikh Al-Issa bisa ci gaba da jajircewar sa wajen inganta zaman lafiya, tattaunawa da fahimtar juna tsakanin al'ummomin mabiya addinai daban-daban.

Tun da farko, Sheikh Al-Issa ya yaba wa ƙoƙarin Shugaba Tinubu na inganta zaman lafiya tsakanin Musulmi da waɗanda ba Musulmi ba, yana mai cewa zaman lafiya da daidaito a Nijeriya za su bayar da gagarumar gudunmawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a Yammacin Afrika da sauran sassan duniya.

Babban Sakatare Janar ɗin ya ce ziyarar sa ta ta'allaƙa ne kan zaman lafiya da zaman lafiya tsakanin al'ummomi, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa taron zai samar da muhimmiyar kafa wajen ciyar da tattaunawa da fahimtar juna gaba a Nijeriya da duniya baki ɗaya.

Ana sa ran taron zai haɗa shugabannin addinai, masu tsara manufofi da sauran masu ruwa da tsaki a wuri guda.

Daga cikin waɗanda s**a tarbi Sheikh Al-Issa a filin jirgin saman akwai Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmad Aliyu Sokoto; Ministan Lafiya da Jin Daɗin Jama'a, Farfesa Muhammad Ali Pate; Ministan Ƙwadago da Ayyukan Yi, Muhammad Maigari Dingyaɗi; Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, mai wakiltar Mazaɓar Sanatan Sakkwato ta Arewa; Sanata Mohammed Ɗanjuma Goje, mai wakiltar Mazaɓar Sanatan Gombe ta Tsakiya; Sanata Ahmed Sani Yerima, da sauran manyan baƙi.

NANS Ta Karrama Umahi da matsayin Patron, Ta Shirya Rangadin Ayyukan Hanyoyin Tarayya a Faɗin NajeriyaƘungiyar Daliban N...
10/08/2026

NANS Ta Karrama Umahi da matsayin Patron, Ta Shirya Rangadin Ayyukan Hanyoyin Tarayya a Faɗin Najeriya

Ƙungiyar Daliban Najeriya, National Association of Nigerian Students (NANS), ta karrama Ministan Ayyuka na Tarayya, Sanata Injiniya David Nweze Umahi, CON, da matsayin Patron na ƙungiyar, bisa gudummawar da take ganin ya bayar wajen bunƙasa ayyukan hanyoyi da hidimar ƙasa.

Shugaban NANS na ƙasa, Dist. Comr. Akinteye Babatunde Afeez, ne ya bayyana karramawar yayin wata ganawa da Ministan a ranar Lahadi, 9 ga Agusta, 2026. Ya ce matakin ya samo asali ne daga jajircewar Umahi wajen aiwatarwa, sa ido da gyaran manyan hanyoyin Tarayya a sassa daban-daban na ƙasar.

A cewar Shugaban NANS, ingantattun hanyoyi suna da matuƙar muhimmanci ga ɗalibai, domin suna sauƙaƙa zirga-zirgar su zuwa makarantu, jarrabawa, wuraren koyon aiki, tarurrukan ilimi da sauran harkokin karatu.

Ya yaba da ayyukan Ma'aikatar Ayyuka ƙarƙashin jagorancin Umahi, musamman manyan ayyukan Abuja–Kaduna–Kano Expressway, Abuja–Kaduna–Minna, Enugu–Port Harcourt Expressway da Lagos–Calabar Coastal Highway, tare da jaddada muhimmancin hanyar Lagos–Sokoto wajen haɗa al'ummomi da sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki.

NANS ta kuma bayyana shirin gudanar da wani babban rangadin ayyukan hanyoyin Tarayya a faɗin ƙasar, inda shugabannin ɗalibai daga sassa daban-daban za su ziyarci wasu daga cikin ayyukan da aka kammala ko ake aiwatarwa ƙarƙashin jagorancin Umahi domin gani da ido da kuma isar da bayanan tasirin ayyukan ga miliyoyin ɗalibai da sauran jama'a.

Shugaban NANS ya ce ƙungiyar ba ta son karramawar ta tsaya a matsayin girmamawa kawai, sai dai tana son gina kyakkyawar alaƙa mai ɗorewa da Ma'aikatar Ayyuka, tare da taka rawa wajen wayar da kan jama'a kan ayyukan ci gaban ƙasa.

Da yake karɓar karramawar, Umahi ya bayyana matsayin NANS a matsayin muhimmiyar ƙungiyar matasa da za ta iya taka rawa wajen fahimtar da al'umma irin tasirin manyan ayyukan more rayuwa ga rayuwar yau da kullum.

Wannan karramawa da shirin rangadin na NANS na ƙara nuna yadda ayyukan hanyoyin Tarayya ke samun kulawa daga ɗalibai da sauran ɓangarorin al'umma, musamman saboda muhimmiyar rawar da hanyoyi ke takawa wajen haɗa al'umma, ilimi, kasuwanci da tattalin arziki.

10/08/2026

Ana Zargin Yan Hisbah Jahar Yobe Da Lakadawa Yar TikTok Shatow Duka, Tare Da Tilasta Mata Tayi Bidiyo Ta Basu Hakuri, a Damaturu dake Jahar Yobe

Me Zaku ce.?

DA DUMI DUMI: Babu Laifi Mutum Yayi Video Da Matarsa Ya Dora A Social Media Duniya Ta Gani, Matukar Babu Zagi Ko Aibu A ...
10/08/2026

DA DUMI DUMI: Babu Laifi Mutum Yayi Video Da Matarsa Ya Dora A Social Media Duniya Ta Gani, Matukar Babu Zagi Ko Aibu A Video Din, Inji Sheik Maqari A Lokacin Da G fresh Kene man Fatawa Wajensa.

Da ɗumi-ɗumi: Atiku Ya Isa Osun, Magoya Bayan ADC S**a Yi Masa Kyakkyawar MarabaTsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku A...
10/08/2026

Da ɗumi-ɗumi: Atiku Ya Isa Osun, Magoya Bayan ADC S**a Yi Masa Kyakkyawar Maraba

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya isa Osun domin halartar babban gangamin karshe na yaƙin neman zaɓen ɗan takarar ADC, Dr. Najeem Salaam.

Magoya bayan jam’iyyar sun tarbi Atiku cikin farin ciki da nuna masa gagarumar karɓuwa.

Zawiyyar Sheikh Tijjani Usman Zangon Barebare ta yi kira ga matasa su guji yin abubuwan da basu dace ba a wurin Mauludi.
10/08/2026

Zawiyyar Sheikh Tijjani Usman Zangon Barebare ta yi kira ga matasa su guji yin abubuwan da basu dace ba a wurin Mauludi.

Address

Kano

Telephone

+2348118797344

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DDL Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share