Kano First Media

Kano First Media Kano First Media. Rahotanni, hotuna da bidiyo kan ayyukan ci gaban kasa Nigeria sassan duniya cikin gaskiya da adalci.

04/03/2026

Koda tsiya koda tsiya tsiya, Maganar zaben Abba da Tinubu, sai sunkawo kujerarsu 2027 cewar Abdullahi Abbas.

Meza kuce dan gane da wannan furucin nasa shin akwai tauhidi ko babu?


02/03/2026

Shugaban kungiyar izala sheik Abdullah Pakistan. Magoya bayansa su tareshi suna Nigeria Sai Tinubu sai Pakistan.

Me zakuce danagene da wannan furuci

  Sanata Barau I. Jibrin ya bayyana cewa ya kai ziyarar ta’aziyya a Dawakin Kudu, Jihar Kano, domin jajanta wa Hon. Must...
02/03/2026



Sanata Barau I. Jibrin ya bayyana cewa ya kai ziyarar ta’aziyya a Dawakin Kudu, Jihar Kano, domin jajanta wa Hon. Mustapha Bala Dawaki bisa rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Binta.

Ya ce marigayiyar ta kasance mace mai tsoron Allah, mai tawali’u da sadaukarwa ga iyali da al’umma. Ya roƙi Allah Ya gafarta mata, Ya yalwata kabarinta, Ya ba ta Aljannatul Firdaus. Ameen.

Iran ta tabbatar da mutuwar jagoran mulkin kasar Ayatollah Ali Khameni," a cewar kafar yada labaran kasar.
01/03/2026

Iran ta tabbatar da mutuwar jagoran mulkin kasar Ayatollah Ali Khameni," a cewar kafar yada labaran kasar.

01/03/2026

Breaking news: vedio yadda wani bangare na Tel Aviv yake yanzu
Daga Irani Military

01/03/2026

Breaking news: Rahotanni da vedio dake yawo daga Kafar yada labarai ta Irani Military ta nuna yadda wani bangare na Birnin Hulon dake kudancin Israel yake yanzu.

Sai dai har yanzu manyan gidan jaridu basu tabbatar da hakanba

Taimakon sojin Amurka ba ya tauye ikon Nijeriya – Hedikwatar TsaroHedikwatar tsaron Nijeriya ta bayyana cewa taimakon da...
27/02/2026

Taimakon sojin Amurka ba ya tauye ikon Nijeriya – Hedikwatar Tsaro

Hedikwatar tsaron Nijeriya ta bayyana cewa taimakon da gwamnatin Amurka ke bai wa kasar a fannin tsaro babu sisin-kobo da gwamnati ta biya, kuma ba ya tauye ikon mallakar ƙasar ko cin gashin kanta ta kowace hanya.

A ranar 17 ga Fabrairu, Hedikwatar Tsaron ta tabbatar da isowar kimanin jami’an sojin Amurka 100 tare da wasu kayan aiki da s**a shafi harkokin tsaro.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro, Manjo Janar Samaila Uba ya fitar, ya ce tura jami’an ya biyo bayan tattaunawa da aka yi tsakanin wakilan Nijeriya da takwarorinsu na Amurka.


  Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Adamawa Fintiri Ya Sauya Sheƙarsa Zuwa APCGwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar ...
27/02/2026



Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Adamawa Fintiri Ya Sauya Sheƙarsa Zuwa APC

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar APC a hukumance, tare da duka mambobin majalisar zartarwarsa da wasu manyan jiga-jigan PDP na jihar. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ganin sauya sheƙar wasu gwamnoni da jiga-jigan jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar mai mulki.

Har yanzu babu cikakken martani daga shugabannin PDP na ƙasa dangane da wannan mataki. Sauyin sheƙar ya biyo bayan ziyarar aiki da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya kai jihar Adamawa, da kuma ficewar kakakin majalisar dokokin jihar, Bathiya Wesley, tare da wasu mambobi 13 daga PDP.

📰 Source: BBC Hausa

Gwamnatin Jihar Kano ta soma kwato motocin gwamnati da wasu tsofaffin kwamishinoni s**a tafi da su bayan murabus dinsu.K...
26/02/2026

Gwamnatin Jihar Kano ta soma kwato motocin gwamnati da wasu tsofaffin kwamishinoni s**a tafi da su bayan murabus dinsu.

Kano First Media ta samo rahoto daga Arewa Updates cewa Shugaban Hukumar Karbar Korafe-Korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, Comrade Sa’idu Yahaya, ne ya jagoranci aikin kwato motocin a ranar Alhamis, 26 ga Fabrairu, 2026.

Ya ce ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Kano ya rubuta wasiku ga tsofaffin jami’an domin su mayar da motocin, amma s**a gaza bin umarnin, lamarin da ya sa aka dauki matakin kwato su.

Daga cikin wadanda aka kwato motocin hannunsu akwai tsohon Kwamishinan Tsaro, Air Vice Marshal Ibrahim Umar, tsohon Kwamishinan Matasa, Mustapha Rabiu Kwankwaso, tsohon Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dr Yusuf Ibrahim Kofar Mata, tsohon Kwamishinan Jin Kai, Dr. Adamu Aliyu Kibiya, da tsohon Kwamishinan Ayyuka na Musamman, Nasiru Sani Garo.

Hukumar ta ce za ta ci gaba da daukar duk matakan da s**a dace domin kare dukiyar gwamnati a jihar Kano.

Me za ku ce kan wannan mataki da Gwmanatin ke dauka?

 Da ɗumi-ɗumi: Matasa Sun Fito Kan Tituna a Kaduna, Sun Bukaci Tsare El-RufaiDa ɗumi-ɗumi: Matasa Suna Zanga-zanga a Kad...
26/02/2026



Da ɗumi-ɗumi: Matasa Sun Fito Kan Tituna a Kaduna, Sun Bukaci Tsare El-Rufai

Da ɗumi-ɗumi: Matasa Suna Zanga-zanga a Kaduna, Suna Neman A Ci Gaba da Tsare Nasir El-Rufai

Wasu daruruwan matasa masu da s**a bayyana kansu a matsayin masu kishin Jihar Kaduna sun fito kan titunan birnin Kaduna domin gudanar da zanga-zanga, inda s**a bukaci hukumomi su ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai, domin gudanar da cikakken bincike a kan zargin da ake yi masa.

Matasan sun ce dole ne a binciki batun ɓatan Dadiyata domin tabbatar da gaskiya da kuma bai wa iyalansa da al’umma adalci.

Sun jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin dole ne ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ba.

Haka kuma, masu zanga-zangar sun bukaci gwamnati ta binciki zargin ɓacewar dala miliyan 350 da ake cewa ya faru a lokacin gwamnatin El-Rufai a jihar Kaduna, tare da tabbatar da cewa an gano gaskiyar lamarin.

A yayin zanga-zangar, matasan sun kuma yi kira ga hukumomi su k**a wasu mutane da s**a hada da Bashir Saidu da Jafaru da Hafiz Bayero, inda s**a zarge su da daukar nauyin wasu tsirarun mutane da sunan zanga-zanga domin kawar da hankalin jama’a daga zarge-zargen da ake yi wa tsohon gwamnan.
Masu zanga-zangar sun ce manufarsu ita ce ganin an yi adalci, tare da tabbatar da cewa doka ta yi aiki a kan kowa ba tare da nuna bambanci ba.

Sun kuma bukaci hukumomi su yi cikakken bincike kan dukkan zarge-zargen da ake yadawa domin tabbatar da gaskiya ga al’ummar jihar Kaduna.

Source Mikiya

 Gwamnatin Jihar Kano ta umurci dukkan tsofaffin Kwamishinoni da su gaggauta dawo da motocin Gwamnati da aka ba su domin...
26/02/2026



Gwamnatin Jihar Kano ta umurci dukkan tsofaffin Kwamishinoni da su gaggauta dawo da motocin Gwamnati da aka ba su domin gudanar da ayyukan ofisoshinsu a lokacin da suke kan mukami.

Gwamnati na jaddada cewa motocin hukuma dukiyar al’umma ne, kuma an ware su ne domin amfanin ofisoshi, ba mallakar mutum ɗaya ba.

Saboda haka, duk wanda har yanzu yana riƙe da motar hukuma bayan barin aiki, wajibi ne ya miƙa ta ga hukumomin da s**a dace ba tare da ɓata lokaci ba.

Haka kuma, duk wanda aka samu da sayar da irin waɗannan motocin, ana buƙatar ya nemo su cikin gaggawa ya mayar wa Gwamnati kayanta, domin kauce wa duk wani mataki na doka da za a ɗauka.

Gwamnati na kira ga dukkan waɗanda abin ya shafa da su nuna gaskiya da kishin ƙasa ta hanyar bin wannan umarni cikin hanzari.
An bayar da wannan sanarwa ne domin wayar da kai da kuma tabbatar da bin doka da oda.

Source Abba Gid-gida TV





 🔴 Barau Ya Karɓi ‘Yan Kasuwar Singer, Ya Jaddada Goyon Bayan Harkokin KasuwanciMambobin Ƙungiyar Cigaban Kasuwar Singer...
26/02/2026



🔴 Barau Ya Karɓi ‘Yan Kasuwar Singer, Ya Jaddada Goyon Bayan Harkokin Kasuwanci

Mambobin Ƙungiyar Cigaban Kasuwar Singer ta Jihar Kano sun kai min ziyarar godiya a gidana da ke Abuja, bisa irin tallafin da na bayar musu, ciki har da ziyarar da na kai da kuma gudummawar da na bayar lokacin da gobara ta lalata kayayyakinsu da dukiyoyi na biliyoyin naira makonni da s**a gabata.

Ƙungiyar ta zo ne ƙarƙashin jagorancin Shugabanta, Alhaji Junaidu Zakari, inda s**a nuna jin daɗinsu kan kudirin da na gabatar a zauren Majalisar Dattawa dangane da gobarar kasuwar.

Abubuwa biyu ne suke da matuƙar muhimmanci ga al’ummarmu: addininmu, Musulunci, da kuma kasuwancinsu. Za mu yi duk mai yiwuwa domin tallafawa da bunƙasa harkokin kasuwancinsu.

Kano a santa da kasuwanci, kuma babu wani mataki na tallafi da zai yi yawa ga wannan muhimmin ɓangare na tattalin arzikimmu.





Address

Kano State Ministry Of Information
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kano First Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share