13/07/2026
Ba wanda yai zaton Annabi Musan da ya Shafe shekaru yana Leburanci(matsayin sadaki) zai wayi Gari bayan wasu shekaru matsayin "كليم الله"(Maiyin magana da Allah), haka Annabinmu Muhammad(s.a.w) lokacin da yake ƙwadago ga Manyan ƙuraishawa yai musu kiwo su biyashi, ba wanda cikinsu yai zaton bayan Shekaru zai zama shugabansu, sai ma gashi ta bayyana shine shugaban duk halittun Allah.
Shi Allah lamarinsa daban ne, sai yasa yace..
وتلك الأيام نداولها بين الناس
"(kamar haka) muke jujjuya kwanaki a tsakanin(su) mutane"
Wanda yau ka Rena, sai gobe ta bayyana kanka ka Rena.
Matukar matashi ya seta tunaninsa, ya niƙe sha'awarsa yaci gaba da fafutukarsa, Gobensa za tafi Yau, wannan Sunnar Allah ne.
Allah ka iya mana, aci gaba da karatu, ko kasuwanci sannan a cike Scholarship.
Kal-Hajab Foundation ✍️