14/04/2026
Dan majalisar wakilai, Bello El-Rufai, ya bayyana cewa Kotun Tarayya da ke jihar Kaduna ta amince da belin mahaifinsa, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
Rahotanni daga Daily Trust sun nuna cewa Bello El-Rufai, wanda ya kasance cikin kotun yayin zaman da aka hana ‘yan jarida shiga, ya ce a yanzu suna ci gaba da cika dukkan sharuddan da kotu ta gindaya domin kammala belin.
Haka kuma, wani jigo a jam’iyyar ADC kuma na hannun daman El-Rufai, Hayatudeen Lawal Makarfi, ya tabbatar da cewa an sanya wasu sharuɗɗa kan belin, tare da bayyana kwarin gwiwar cewa za a cika su nan ba da jimawa ba.
A baya, Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gurfanar da El-Rufai a gaban kotu, inda daga bisani aka dage sauraron bukatar belin zuwa ranar 21 ga Afrilu, 2026.