Walkiya

Walkiya Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Walkiya, Media/News Company, Karu.

Walkiya Jarida ce mallakin kamfanin Walkiya Digital Media LTD dake watsa labarai kan harshen Hausa a Najeriya, Whatsapp ko kira duk za'a iya samun mu akan wannan lamba 0916 132 6043

Dan majalisar wakilai, Bello El-Rufai, ya bayyana cewa Kotun Tarayya da ke jihar Kaduna ta amince da belin mahaifinsa, t...
14/04/2026

Dan majalisar wakilai, Bello El-Rufai, ya bayyana cewa Kotun Tarayya da ke jihar Kaduna ta amince da belin mahaifinsa, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.

Rahotanni daga Daily Trust sun nuna cewa Bello El-Rufai, wanda ya kasance cikin kotun yayin zaman da aka hana ‘yan jarida shiga, ya ce a yanzu suna ci gaba da cika dukkan sharuddan da kotu ta gindaya domin kammala belin.

Haka kuma, wani jigo a jam’iyyar ADC kuma na hannun daman El-Rufai, Hayatudeen Lawal Makarfi, ya tabbatar da cewa an sanya wasu sharuɗɗa kan belin, tare da bayyana kwarin gwiwar cewa za a cika su nan ba da jimawa ba.

A baya, Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gurfanar da El-Rufai a gaban kotu, inda daga bisani aka dage sauraron bukatar belin zuwa ranar 21 ga Afrilu, 2026.

Shugaban ƙasa ya gudanar da wata ganawa ta musamman da shugabannin tsaro, bayan wani mummunan hari da jirgin saman soji ...
14/04/2026

Shugaban ƙasa ya gudanar da wata ganawa ta musamman da shugabannin tsaro, bayan wani mummunan hari da jirgin saman soji ya kai a kasuwar Jilli da ke kan iyakar jihohin Borno da Yobe.

Rahotanni sun bayyana cewa harin ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutane 200, yayin da wasu da dama s**a jikkata, lamarin da ya janyo damuwa da ce-ce-ku-ce a tsakanin al’umma.

Ganawar, wadda aka gudanar a ranar Litinin, ta biyo bayan dawowar Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga ziyarar aiki da ya kai jihohin Lagos, Ogun da Plateau, inda ake sa ran za a duba matakan tsaro da kuma hanyoyin kauce wa irin wannan mummunan lamari a nan gaba.

Kotun da ke sauraron ƙarar da ake yi wa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ta sake ɗage zaman saur...
14/04/2026

Kotun da ke sauraron ƙarar da ake yi wa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ta sake ɗage zaman sauraron buƙatar bada belinsa zuwa ranar 21 ga watan Afrilu, 2026.

A zaman kotun na yau, alkalin ya bayyana cewa an ɗage shari’ar ne domin bai wa ɓangarorin da ke ƙara da kuma waɗanda ake ƙara damar kammala shirye-shiryensu gabanin ci gaba da sauraron ƙarar.

Lauyoyin ɓangarorin biyu sun amince da ranar da kotun ta bayar, inda s**a nuna shirinsu na gabatar da hujjoji da s**a dace a zama na gaba.

Ana zargin El-Rufai da aikata wasu laifuffuka da s**a shafi cin hanci da rashawa, zarge-zargen da har yanzu yake musantawa.

Za a ci gaba da sauraron shari’ar a ranar 21 ga Afrilu, inda ake sa ran kotun za ta fara zurfafa bincike kan muhimman hujjoji da s**a shafi lamarin.

An Tsauraran Matakan Tsaro Yayin Da El-Rufai Ya Isa Kotun Tarayya Domin Sauraron Hukuncin BelinsaTsohon gwamnan jihar Ka...
14/04/2026

An Tsauraran Matakan Tsaro Yayin Da El-Rufai Ya Isa Kotun Tarayya Domin Sauraron Hukuncin Belinsa

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya isa babbar kotun tarayya domin sauraron hukuncin belinsa kan sabbin tuhume-tuhumen cin hanci da rashawa da hukumar ICPC ke yi masa.

Rahotanni sun nuna cewa an girke jami’an tsaro da dama a harabar kotun, inda aka tsaurara bincike da sanya ido domin tabbatar da tsaro da hana duk wata barazana yayin zaman kotun.

Ana zargin tsohon gwamnan da aikata wasu laifuffuka da s**a shafi rashawa, lamarin da ya jawo hankalin jama’a da ‘yan siyasa da dama.

Ana sa ran kotun za ta yanke hukunci kan bukatar belin nasa, wanda zai tantance ko zai ci gaba da fuskantar shari’ar a tsare ko kuma a waje da gidan yari.

Kotun Ƙoli ta Jihar Kano ta yanke hukuncin watsi da tuhumar cin hanci da rashawa da ake yi wa tsohon kwamishina, Garo, b...
14/04/2026

Kotun Ƙoli ta Jihar Kano ta yanke hukuncin watsi da tuhumar cin hanci da rashawa da ake yi wa tsohon kwamishina, Garo, bayan ta bayyana cewa an kasa bin sahihan matakan bincike kafin gurfanar da shi a gaban kotu.

Alƙalin kotun ya jaddada cewa rashin cikakken bincike da bin ƙa’idojin shari’a ya sa ba za a iya ci gaba da sauraron ƙarar ba, lamarin da ya tilasta kotun yanke hukuncin soke shari’ar gaba ɗaya.

Pantami Ya Musanta Labarin Janyewa Daga Takarar Gwamnan GombeMai neman takarar gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar APC, Dr. ...
14/04/2026

Pantami Ya Musanta Labarin Janyewa Daga Takarar Gwamnan Gombe

Mai neman takarar gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar APC, Dr. Isa Ali Ibrahim Pantami, ya karyata rahotannin da ke cewa an bukace shi ya janye daga takararsa.

Pantami ya bayyana a shafinsa na X cewa labarin ba shi da tushe, yana mai jaddada cewa babu wani lokaci da gwamnan ya nemi hakan.

Ya ce akasin haka, an girmama shi ne ta hanyar gayyatarsa a matsayin mai jawabi a wani taro.

Hakazalika, ya zargi masu yada jita-jitar da kokarin tayar da rudani da bata suna, yana mai gargadin cewa irin wannan shiri ba zai yi nasara ba.

Wasu al’ummomin Fulani da ke yankunan Lahiyaje, Patigi da Gugu a jihar Kwara sun bayyana cewa suna fuskantar barazanar k...
14/04/2026

Wasu al’ummomin Fulani da ke yankunan Lahiyaje, Patigi da Gugu a jihar Kwara sun bayyana cewa suna fuskantar barazanar kora daga muhallinsu na gado.

Rahotanni sun ce an bai wa al’ummomin wa’adin kwanaki uku domin su fice daga yankunan nasu, wa’adin da ke cika a yau Talata, 14 ga watan Afrilu, 2026. An kuma gargade su cewa duk wanda bai bar wurin ba, zai fuskanci abin da zai biyo baya.

Shugaban matasan Fulani na yankin, Abdulahi Mohammed, ya bayyana wa BBC cewa wannan barazana ta jefa al’ummar cikin fargaba da tashin hankali, musamman ganin yadda aka fara kone wasu daga cikin muhallansu.

Ya ce, “An ba mu kwana biyu zuwa uku mu bar gidajenmu. Duk wanda bai tashi ba, an ce yana cikin matsala, kuma duk abin da ya same shi, shi ya jawo wa kansa.”

Al’ummomin sun nuna damuwa kan yadda suke rasa matsugunansu na iyaye da kakanni, tare da kira ga hukumomi da su dauki matakin gaggawa domin dakile lamarin.

YANZU-YANZU: Bola Ahmed Tinubu Ya Tattauna Da Shugabannin Tsaro Kan Harin Jirgin Soji A Kasuwar Jilli, YobeShugaban ƙasa...
13/04/2026

YANZU-YANZU: Bola Ahmed Tinubu Ya Tattauna Da Shugabannin Tsaro Kan Harin Jirgin Soji A Kasuwar Jilli, Yobe

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na gudanar da wata muhimmiyar ganawa da shugabannin hafsoshin tsaro domin nazari da ɗaukar mataki kan harin jirgin saman sojoji da ya auku a kasuwar Jilli da ke jihar Yobe.

Ganawar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa da tambayoyi daga jama’a kan yadda lamarin ya faru da kuma matakan da gwamnati za ta ɗauka domin kauce wa maimaituwar irin wannan lamari.

Tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Chika Malami, ya bayyana cewa jam’iyyar African Democratic ...
13/04/2026

Tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Chika Malami, ya bayyana cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) wata ƙaƙƙarfan haɗaka ce da aka kafa domin ceto Najeriya da kuma kifar da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) daga mulki a dukkan matakan gwamnati.

Malami ya jaddada cewa wannan haɗaka na ADC na da ƙarfin da zai iya kawo sauyi a siyasar ƙasar, tare da burin samar da ingantaccen shugabanci da zai amfanar da al’ummar Najeriya.

Jami’ar Bayero Kano Ta Ɗaga Sheikh Bashir Aliyu Zuwa Farfesa a Fannin Nazarin Addinin MusulunciHukumar Gudanarwar Jami’a...
13/04/2026

Jami’ar Bayero Kano Ta Ɗaga Sheikh Bashir Aliyu Zuwa Farfesa a Fannin Nazarin Addinin Musulunci

Hukumar Gudanarwar Jami’ar Bayero da ke Kano ta amince da ɗaga likkafar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Bashir Aliyu, zuwa matsayin Farfesa a Sashen Nazarin Addinin Musulunci.

Wannan mataki na zuwa ne a matsayin girmamawa da kuma karramawa ga irin gudunmawar da Sheikh Bashir Aliyu ya bayar tsawon shekaru wajen koyarwa, bincike, da kuma yaɗa ilimin addini a jami’a da ma al’umma baki ɗaya.

Masana da ɗalibai sun bayyana wannan ɗaukaka a matsayin abin alfahari ga jami’ar, tare da jaddada cewa irin gudunmawar da malamin ke bayarwa ta taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ilimin addinin Musulunci.

Ana sa ran wannan sabon matsayi zai ƙara masa ƙaimi wajen ci gaba da gudanar da ayyukansa na ilimi da tarbiyya.

Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi wani gagarumin bayani inda ya bayyan...
13/04/2026

Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi wani gagarumin bayani inda ya bayyana cewa Najeriya ba ta taɓa samun shugaban ƙasa mai adalci, hangen nesa da cikakken fahimtar makamar mulki kamar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba.

Pantami ya ce salon mulkin Tinubu ya bambanta da na shugabannin da s**a gabata, musamman ta fuskar yanke shawara cikin gaggawa da kuma yunƙurin da ake yi na ciyar da ƙasar gaba a fannoni daban-daban.

A cewarsa, irin shugabancin da Tinubu ke gudanarwa na nuna kwarewa, gogewa da kuma hangen nesa mai zurfi, wanda ya taimaka wajen ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar da inganta tsarin mulki.

Sai dai kuma, wannan batu na ci gaba da haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan Najeriya, inda wasu ke ganin ana samun ci gaba, yayin da wasu ke cewa har yanzu akwai kalubale masu yawa a ƙasa musamman a fannin tattalin arziki da rayuwar yau da kullum.

Rahotanni sun nuna cewa El-Rufai ya bayyana rashin gamsuwa da yadda alƙalin Kotun Tarayya da ke Kaduna ke tafiyar da sha...
13/04/2026

Rahotanni sun nuna cewa El-Rufai ya bayyana rashin gamsuwa da yadda alƙalin Kotun Tarayya da ke Kaduna ke tafiyar da shari’ar, inda ya zargi cewa akwai yiwuwar rashin adalci a cikin shari’ar da ake yi masa.

Wannan mataki nasa ya jawo muhawara mai zafi a fadin kasa, musamman a tsakanin masu sharhi kan harkokin shari’a da siyasa, inda wasu ke ganin wannan na iya zama dabarar kare kai, yayin da wasu kuma ke cewa yana da ‘yancin neman kotun da ta fi zaman lafiya da gaskiya.

A halin yanzu, ba a kai ga samun cikakken hukunci kan bukatar El-Rufai ba, yayin da ake sa ran kotu za ta yi nazari kan roƙon nasa a zaman da ke tafe.

Masu sa ido kan al’amura na ganin wannan lamari na iya kara daukar hankali a fagen siyasar Najeriya, musamman ganin irin matsayin El-Rufai a cikin jam’iyyar siyasa da ya fito daga cikinta.

Ana cigaba da bibiyar wannan batu domin samun sabon labari.

Address

Karu
900110

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Walkiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Walkiya:

Share